Sashe 44
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kiri-kiri Abba ya kori Balele daga aiki, sai dai ba a bashi dama ya kare kansa ba domin tabbas shi din ma yana shaye-shayen amma bai taba zuwa da abun maye gidan ba kuma bai taba zuwa gidan a buge ba. Gashi yana da in-ina don haka ma kafin yace wani abu aka yanke masa hukunci. Ya mikawa Abban mukullin mota ya fice, a ranar kuma ya dawo da Malam Sule aiki.
…………..
Bayan an sha ruwa Mommy din ta yiwo waya Yusra ta sanar da ita an dawo da Malam Sule, a lokacin ta kara shiga damuwa. Kamar dai duk wata tufka da ta taho ta bari an fara biyota da warwara. Ta zata wani direnban za a dauka amma an dawo da Malam Sule. Wannan ya kara kasa mata hankali acan Saudiya din.
__
Duk wani shirye-shiryen bikin Sallah an kammala don a yanzu saura kwana uku Sallah.
Makocin gidan Zahra wanda gidansa yake kallon gidan shine commissioner of Environment na Jihar Kano wato Alhaji Mamman Ahmad Yakasai.
Tun kafin a fara azumi gwamnatin Jiha take gangamin dashen bishiyoyi, ko ina an shuka. A yau commissioner ya ciko motar Hilux guda biyu da bishiyoyi don mutan unguwar su samu su shuka a unguwa da kuma gidajensu.
Bishiyun sun hada da na goba, gwanda, umbrella sai kuma bishiyar malmo da kuma ta madaci.
Gidan commissioner akwai masallacin a jiki wanda yawancin mutanen kan layin a nan suke khamsi salawati. Kuma da yake commissioner mutum ne mai son mutane da alkhairi in dai yana nan wajen baya rabuwa da mutane.
Nan kofar masallaci commissioner ya sa aka sauke bishiyun ga kuma matasa su kamar shida wadanda zasu shuka bishiyun.
Abba yana cikin mutane da suka fito daga masallacin daga karshe tare da liman, suna fita suka tsaya da commissioner da mutanen unguwa ana gaggaisawa.
Ya kama hannun liman yana nuna masa bishiyun yana cewa
‘Malam liman gasu fa, kaga goba da fruit kowa ya dauka a shukawa yara a cikin gidan don kaga gobar nan mai dadi ce kuma ‘yayanta manya ne sosai. Wadannan kuma da basa ‘yaya duk a shuka mana su a unguwa.’
Ya kama hannun Abba yace
‘Education! Teacher uban karatu. Ga goba nan a shukawa amarya don ina hango gidanta ko ganye babu.’
Yayi dariya suka cafke hannu
‘To sai na gayawa Uwargida in ya so tayi anti party.’
‘Kaina bisa wuyana kar kasa a mayar dani kauye, Uwargida ma a shuka mata goba harda fruit duk a hada.’
Nan liman ya sa hannu aka rarraba bishiyun, guda biyar aka warewa Abba goba biyu fruit biyu da kuma malmo wanda za a shuka a kofar gidan Aisha don gate din gidan Zahra bishiyar har guda hudu ne a wajen.
Yaran da aka taho dasu don shuka bishiyun suka fara dauka kowanne mai gida yana nuna musu gidan da zasu je su shuka masa.
Wani yarone matashi ya kwashi na gidan Abba, da hannu Abban ya nuno masa gidan Aisha yace duka a nan za a shuka domin gidan Zahra akwai bishiyar mangoro da kuma bishiyar ayaba, ga gwanda wajen bishiya hudu a jikin katanga.
Har ya juya zai wuce gaba ya rakasu sai kuma ya fasa, ya dauki waya ya kirawota. Bayan sun gaisa yace mata ga yaro nan zai shuka bishiya a cikin gidan ta bude gate.
Suna ajiye waya ya nunawa yaron gidan yace yaje za a bude masa.
Ya kwasa ya wuce ya bar Abban suna ta hirarrakinsu da mutane.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
25
Daidai lokacin da yaron da zai shuka bishiyar ya tsallako tare da abokin aikinsa dai-dai lokacin ta bude gate din. Suka gaisheta, bayan ta amsa ta ja baya suka wuce ciki. Har ta kama hanya zata koma ciki yaron wanda ake kira Masta yace
‘Hajiya a dai-dai ina zamu shuka, Alhaji cewa yayi a sa hudu a cikin gida biyu a waje; naga cikin gidan da dan fili ta wane gefen zamu saka?’
Ta dan karewa tsakar gidan kallo tace
‘Kusa biyu a nan gaba, biyun kuma sai ku saka a bayan gida.’
Har ta juya kuma sai ta sake tsayawa ta juyo ta nuna gefen gidan in an tafi za a zagaya dai-dai tagar dakin Abban tace
‘Ka shuka daya a nan, yanda idan ta girma zata dinga kare rana don da rana ta fito take shiga dakin nan ta taga.’
‘In sha Allah Hajiya.’
Tana wucewa suka fara aiki.
An kusa shan ruwa kuma so suke su gama kafin a sha ruwan don haka nan da nan suka fara aiki.
Suka shuka bishiyar umbrella guda daya da kuma goba guda daya a gaban gidan. Suka zagaya bayan gidan suka shuka bishiyar goba guda daya don wajen bashi da sarari sosai umbrella ba zata sami wajen budewa sosai ba.
Wajen tagar dakin Abba nan ne karshe, sai da Masta ya auna sosai tunda an ce masa ana so ta dinga kare rana, ya dan bada tazara kadan ya kara kusantar katangar tunda tagar dama bata da nisa sosai daga katangar. Yana hakawa daya yaron yana kwashe kasar.
Yana cikin hakawa ya daki roba, daya yaron yace
‘Kada fa ka fasa musu pipe Masta.’
‘Haba Baabaa, sai dai ko wata robar banza don da da dapipe a wajen nan Hajiya ba zata ce a shuka bishiyar a wajen ba.’
Ya saka hannu ya ficiko gutsuren robar, gaba daya ta taho amma sai dai ta riga ta dagargaje. Take suka kunduma ashar saboda wani wari da doyi da ya dumame wajen. Abinda yake cikin butar yayi tsalle waje daya saboda yanda aka finciko butar. Baabaa yace
‘Wannan wane irin bala’in wari ne mutumina?’
Ya goge hancinsa ya karasa kan abinda ya fita daga cikin butar, ya sa fatanyar hannunsa ta dungurin abun da yake nade a bakin kyalle yace
‘Kutumar uba, kai Baabaa ai ga warin nan.’
‘Bari na dauko ledar da muka cire sauran bishiyun mu nade a ciki kawai mu jefa a shara.’
‘Ai wallahi sai na bude bakin kyallen naga ko menene wannan, nifa ji nake kamar warin jaba ne kuma aka hada shi da wani abun da yafi jabar wari.’
Ya wuce ya nufi dauko ledar yana mita
‘Kai wallahi masta ka fiye jangwale-jangwale, daga hako abu sai kace sai ka bude. Yanzu ba zaka bari muyi mu gama aikin nan kafin a sha ruwan ba sai ka bata mana lokaci.’
Yana bude bakin kyallen yana toshe hanci kuma yana bawa Baabaa amsa
‘Ai ni na fi so mu sha ruwa a nan, Alhaji sawa zai yi a bamu dankali da kwai harda shayi, in muka tafi kuwa ka san sai da kyar ma zamu sami kunu da kosan.'
Suka saki baki gaba daya suna kallon ikon Allah, bayan ya gama cire bakin kyallen abinda yake ciki ya bayyana.
Kan jaba ne wanda gaba dayansa an rubuceshi da hatimi da wasu kalmomi sannan an tsiyaye idanuwan jabar. Bakin jabar kuma an kawo wani bakin kwado an huda sama da kasan bakin an datse kwadon, ga kuma wata laya da aka ajiye daga kan goshin jabar aka kawo allura aka soke layar a jiki.
Masta ya kalli baba, ya kara goge hancinsa yace
‘Wallahi wannan abun tsafine, ai wannan ma idan bamu fitar dashi ba gidan nan ba zai zaunu ba don ciki ma sai dai su fito su fice.’
Take Masta ya mayar da kan cikin bakin kyallen ya dauka ya nufo gate, Baabaa ya rufo masa baya.
Suna fitowa ya nufi kwalbatin da yake kofar gidan zai jefe, sai Baabaa ya dafa kafadarsa yace
‘Ka ga, mu kirawo mai gidan mu nuna masa tukunna.’
‘To kai idan fa shi yayi wa wani asirin ya binne a wajen.’
‘Shikenan asirinsa ya tonu don kaga ina jin wancan mutumin limami ne kuma da alama da iliminsa.’
Ya fada yana nuna Abba wanda yanzu su uku suka rage a kofar gidan commissioner; shi da liman da kuma commissioner.
Masta yace
‘Kuma ka san yanzu mutane har makota suke yiwa asiri ba, rike min nan na tsallaka na kirawosu su su gani.’
Ya mikawa Masta bakin kyallen ya karba yana tofar da yawu, shi kuma ya tsallaka.
Yana zuwa dab da su ya dan rage tsawo yace
‘Yallabai akwai matsala a gidan can fa da muka je shuka bishiyar.’
Commissioner yace
‘Subhanallah, Allah ya sa dai ba wani abun kuka faso ba garin shukar.’
‘Ba mu fasa komai ba yallabai amma dai gara Alhaji ya zo ya duba.’
Ya dubi Abba yace
‘Mu karasa mu gani, Allah ya sa ba pipe suka faso ba ko suck away.’
Suka tsallako Abban yana addu’ar Allah ya sa a kofar gidan ne don baya so ya shiga gidan a gaban commissioner da liman don ba zai iya tsayawa a gidan ya dade ba.
Tun kafin su karasa tsallakowa gaba dayansu suka ji wari, haka suka daure suka karasa.
Commissioner yace
‘Meye yake wari haka ne a wajen?’
Masta yace
‘Yallabai ai abun da muka hako ne garin shuka bishiyar, shine nace gara dai shi Alhaji ya duba kafin mu yar.’
Liman yace
‘Wannan ma ai baza a yar ba sai dai ko a binne din don idan an yar ma haka zai yi ta damun mutane da wari; kana azumi wannan warin ai sai ya bugar da kai.’
Suna karasawa bakin gate din Abba ya dafe kai, ya dan tsaya kafin su kai kusa da Baabaa wanda yake rike da abun. Commissioner da yake kusa da shi yace
‘Alhaji Yusufa yaya dai, naga fa kamar tsayuwar tana neman gagararka?’
Murya kasa kasa yace
‘Warin nan sa min ciwon kai yake.’
Yanda yaga yanayinsa ya sa ya dafe shi, ya dubi liman yace
‘Malam liman duba su binne wannan abun kawai, bari mu sami wajen zama kada Alhaji Yusuf ya fadi fa ka san akwai kishin ruwa.’
Ya karasa shi da Abba, suka sami waje suka zauna a kan kwalbatin da yake gidan kusa da gidan Aishan. Shi dai Abban ya zauna ne kawai don baya son ace matsalar daga gidansa ce kuma ya tafi ya barsu, amma har nan inda ya zauna yana jin warin kuma kansa juyawa kawai yakeyi.
…………..
Bayan an sha ruwa Mommy din ta yiwo waya Yusra ta sanar da ita an dawo da Malam Sule, a lokacin ta kara shiga damuwa. Kamar dai duk wata tufka da ta taho ta bari an fara biyota da warwara. Ta zata wani direnban za a dauka amma an dawo da Malam Sule. Wannan ya kara kasa mata hankali acan Saudiya din.
__
Duk wani shirye-shiryen bikin Sallah an kammala don a yanzu saura kwana uku Sallah.
Makocin gidan Zahra wanda gidansa yake kallon gidan shine commissioner of Environment na Jihar Kano wato Alhaji Mamman Ahmad Yakasai.
Tun kafin a fara azumi gwamnatin Jiha take gangamin dashen bishiyoyi, ko ina an shuka. A yau commissioner ya ciko motar Hilux guda biyu da bishiyoyi don mutan unguwar su samu su shuka a unguwa da kuma gidajensu.
Bishiyun sun hada da na goba, gwanda, umbrella sai kuma bishiyar malmo da kuma ta madaci.
Gidan commissioner akwai masallacin a jiki wanda yawancin mutanen kan layin a nan suke khamsi salawati. Kuma da yake commissioner mutum ne mai son mutane da alkhairi in dai yana nan wajen baya rabuwa da mutane.
Nan kofar masallaci commissioner ya sa aka sauke bishiyun ga kuma matasa su kamar shida wadanda zasu shuka bishiyun.
Abba yana cikin mutane da suka fito daga masallacin daga karshe tare da liman, suna fita suka tsaya da commissioner da mutanen unguwa ana gaggaisawa.
Ya kama hannun liman yana nuna masa bishiyun yana cewa
‘Malam liman gasu fa, kaga goba da fruit kowa ya dauka a shukawa yara a cikin gidan don kaga gobar nan mai dadi ce kuma ‘yayanta manya ne sosai. Wadannan kuma da basa ‘yaya duk a shuka mana su a unguwa.’
Ya kama hannun Abba yace
‘Education! Teacher uban karatu. Ga goba nan a shukawa amarya don ina hango gidanta ko ganye babu.’
Yayi dariya suka cafke hannu
‘To sai na gayawa Uwargida in ya so tayi anti party.’
‘Kaina bisa wuyana kar kasa a mayar dani kauye, Uwargida ma a shuka mata goba harda fruit duk a hada.’
Nan liman ya sa hannu aka rarraba bishiyun, guda biyar aka warewa Abba goba biyu fruit biyu da kuma malmo wanda za a shuka a kofar gidan Aisha don gate din gidan Zahra bishiyar har guda hudu ne a wajen.
Yaran da aka taho dasu don shuka bishiyun suka fara dauka kowanne mai gida yana nuna musu gidan da zasu je su shuka masa.
Wani yarone matashi ya kwashi na gidan Abba, da hannu Abban ya nuno masa gidan Aisha yace duka a nan za a shuka domin gidan Zahra akwai bishiyar mangoro da kuma bishiyar ayaba, ga gwanda wajen bishiya hudu a jikin katanga.
Har ya juya zai wuce gaba ya rakasu sai kuma ya fasa, ya dauki waya ya kirawota. Bayan sun gaisa yace mata ga yaro nan zai shuka bishiya a cikin gidan ta bude gate.
Suna ajiye waya ya nunawa yaron gidan yace yaje za a bude masa.
Ya kwasa ya wuce ya bar Abban suna ta hirarrakinsu da mutane.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
25
Daidai lokacin da yaron da zai shuka bishiyar ya tsallako tare da abokin aikinsa dai-dai lokacin ta bude gate din. Suka gaisheta, bayan ta amsa ta ja baya suka wuce ciki. Har ta kama hanya zata koma ciki yaron wanda ake kira Masta yace
‘Hajiya a dai-dai ina zamu shuka, Alhaji cewa yayi a sa hudu a cikin gida biyu a waje; naga cikin gidan da dan fili ta wane gefen zamu saka?’
Ta dan karewa tsakar gidan kallo tace
‘Kusa biyu a nan gaba, biyun kuma sai ku saka a bayan gida.’
Har ta juya kuma sai ta sake tsayawa ta juyo ta nuna gefen gidan in an tafi za a zagaya dai-dai tagar dakin Abban tace
‘Ka shuka daya a nan, yanda idan ta girma zata dinga kare rana don da rana ta fito take shiga dakin nan ta taga.’
‘In sha Allah Hajiya.’
Tana wucewa suka fara aiki.
An kusa shan ruwa kuma so suke su gama kafin a sha ruwan don haka nan da nan suka fara aiki.
Suka shuka bishiyar umbrella guda daya da kuma goba guda daya a gaban gidan. Suka zagaya bayan gidan suka shuka bishiyar goba guda daya don wajen bashi da sarari sosai umbrella ba zata sami wajen budewa sosai ba.
Wajen tagar dakin Abba nan ne karshe, sai da Masta ya auna sosai tunda an ce masa ana so ta dinga kare rana, ya dan bada tazara kadan ya kara kusantar katangar tunda tagar dama bata da nisa sosai daga katangar. Yana hakawa daya yaron yana kwashe kasar.
Yana cikin hakawa ya daki roba, daya yaron yace
‘Kada fa ka fasa musu pipe Masta.’
‘Haba Baabaa, sai dai ko wata robar banza don da da dapipe a wajen nan Hajiya ba zata ce a shuka bishiyar a wajen ba.’
Ya saka hannu ya ficiko gutsuren robar, gaba daya ta taho amma sai dai ta riga ta dagargaje. Take suka kunduma ashar saboda wani wari da doyi da ya dumame wajen. Abinda yake cikin butar yayi tsalle waje daya saboda yanda aka finciko butar. Baabaa yace
‘Wannan wane irin bala’in wari ne mutumina?’
Ya goge hancinsa ya karasa kan abinda ya fita daga cikin butar, ya sa fatanyar hannunsa ta dungurin abun da yake nade a bakin kyalle yace
‘Kutumar uba, kai Baabaa ai ga warin nan.’
‘Bari na dauko ledar da muka cire sauran bishiyun mu nade a ciki kawai mu jefa a shara.’
‘Ai wallahi sai na bude bakin kyallen naga ko menene wannan, nifa ji nake kamar warin jaba ne kuma aka hada shi da wani abun da yafi jabar wari.’
Ya wuce ya nufi dauko ledar yana mita
‘Kai wallahi masta ka fiye jangwale-jangwale, daga hako abu sai kace sai ka bude. Yanzu ba zaka bari muyi mu gama aikin nan kafin a sha ruwan ba sai ka bata mana lokaci.’
Yana bude bakin kyallen yana toshe hanci kuma yana bawa Baabaa amsa
‘Ai ni na fi so mu sha ruwa a nan, Alhaji sawa zai yi a bamu dankali da kwai harda shayi, in muka tafi kuwa ka san sai da kyar ma zamu sami kunu da kosan.'
Suka saki baki gaba daya suna kallon ikon Allah, bayan ya gama cire bakin kyallen abinda yake ciki ya bayyana.
Kan jaba ne wanda gaba dayansa an rubuceshi da hatimi da wasu kalmomi sannan an tsiyaye idanuwan jabar. Bakin jabar kuma an kawo wani bakin kwado an huda sama da kasan bakin an datse kwadon, ga kuma wata laya da aka ajiye daga kan goshin jabar aka kawo allura aka soke layar a jiki.
Masta ya kalli baba, ya kara goge hancinsa yace
‘Wallahi wannan abun tsafine, ai wannan ma idan bamu fitar dashi ba gidan nan ba zai zaunu ba don ciki ma sai dai su fito su fice.’
Take Masta ya mayar da kan cikin bakin kyallen ya dauka ya nufo gate, Baabaa ya rufo masa baya.
Suna fitowa ya nufi kwalbatin da yake kofar gidan zai jefe, sai Baabaa ya dafa kafadarsa yace
‘Ka ga, mu kirawo mai gidan mu nuna masa tukunna.’
‘To kai idan fa shi yayi wa wani asirin ya binne a wajen.’
‘Shikenan asirinsa ya tonu don kaga ina jin wancan mutumin limami ne kuma da alama da iliminsa.’
Ya fada yana nuna Abba wanda yanzu su uku suka rage a kofar gidan commissioner; shi da liman da kuma commissioner.
Masta yace
‘Kuma ka san yanzu mutane har makota suke yiwa asiri ba, rike min nan na tsallaka na kirawosu su su gani.’
Ya mikawa Masta bakin kyallen ya karba yana tofar da yawu, shi kuma ya tsallaka.
Yana zuwa dab da su ya dan rage tsawo yace
‘Yallabai akwai matsala a gidan can fa da muka je shuka bishiyar.’
Commissioner yace
‘Subhanallah, Allah ya sa dai ba wani abun kuka faso ba garin shukar.’
‘Ba mu fasa komai ba yallabai amma dai gara Alhaji ya zo ya duba.’
Ya dubi Abba yace
‘Mu karasa mu gani, Allah ya sa ba pipe suka faso ba ko suck away.’
Suka tsallako Abban yana addu’ar Allah ya sa a kofar gidan ne don baya so ya shiga gidan a gaban commissioner da liman don ba zai iya tsayawa a gidan ya dade ba.
Tun kafin su karasa tsallakowa gaba dayansu suka ji wari, haka suka daure suka karasa.
Commissioner yace
‘Meye yake wari haka ne a wajen?’
Masta yace
‘Yallabai ai abun da muka hako ne garin shuka bishiyar, shine nace gara dai shi Alhaji ya duba kafin mu yar.’
Liman yace
‘Wannan ma ai baza a yar ba sai dai ko a binne din don idan an yar ma haka zai yi ta damun mutane da wari; kana azumi wannan warin ai sai ya bugar da kai.’
Suna karasawa bakin gate din Abba ya dafe kai, ya dan tsaya kafin su kai kusa da Baabaa wanda yake rike da abun. Commissioner da yake kusa da shi yace
‘Alhaji Yusufa yaya dai, naga fa kamar tsayuwar tana neman gagararka?’
Murya kasa kasa yace
‘Warin nan sa min ciwon kai yake.’
Yanda yaga yanayinsa ya sa ya dafe shi, ya dubi liman yace
‘Malam liman duba su binne wannan abun kawai, bari mu sami wajen zama kada Alhaji Yusuf ya fadi fa ka san akwai kishin ruwa.’
Ya karasa shi da Abba, suka sami waje suka zauna a kan kwalbatin da yake gidan kusa da gidan Aishan. Shi dai Abban ya zauna ne kawai don baya son ace matsalar daga gidansa ce kuma ya tafi ya barsu, amma har nan inda ya zauna yana jin warin kuma kansa juyawa kawai yakeyi.