Sashe 97
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Babu wanda yayi magana, don haka Abban yace
'Shikenan, ga kiran magriba nan mu tashi muyi shirin sallah.'
Ya tsallake su ya nufi daki yayinda su kuma suka nufi benen da nufin saukowa.
Tun a kafar benen Yusra ta fara mita ita kadai
'Wallahi bata isa na bata hakuri ba, ni da gidan ubana na ga wanda zai koreni sai dai kowa ya koma gidan ubansa wallahi.’
Har ya murda kofar dakin zai shiga sai kuma ya fasa ya dawo ya samesu a kafar bene don haka duk abinda Yusra ta fada ya ji. Bai kula da ita ba yace
'Sadik idan ka shirya ka jira ni mu tafi masallacin tare.’
Suka wuce shi kuma ya koma dakin yana mamakin Yusra.
Bai taba sanin lalacewar Yusra ta kai haka ba, tun kafin ma aje ko ina ta sanar ba zata bi umarninsa ba. Lallai gara ya barta taje gidan Yaya Bello don ya san ba zai yi mata a hankali ba. Watakila idan ya cigaba da addu'a Allah ya sa ta canza hali.
Nan da nan ya shirya suka tafi masallaci tare da Saddikun, suna dawowa ya shirya ya wuce gidan Yaya Bello.
……….
Tun a hanya ya sanar da Yaya Bellon yanda suka yi da Yusra, nan suka yanke maganar cewa kawai Yusra da Nana su dawo gidan Yayan.
Suna isa suka tarar Baffa da Yaya Abubakar suna jiransu.
A falon Baffa suka zauna gaba daya; Aisha, Anti Uwani da Zahida suna gefe yayinda Baffa da Ya Abubakar suke gefe sai Abban da Yaya Bello da suma suke gefe.
Tunda ya zauna yake kallon Aishan; tayi kyau tayi fes kamar bata da wata damuwa. Yanda yaki ya dauke idonsa daga kallonta ya sa ta sunkuyar da kai. Yaya Bello ne ya kula da halin da ake ciki ya tabo Abban.
Gaba dayansu suka gaisa da su Baffa da Anti Uwani.
Baffa yayi gyaran murya yace
'Yusufa me ya hadakane da amaryar taka har ta taho gida, duk da tace ba kaine kace ta taho ba?’
Nan ya mayarwa da Baffan yanda sukayi kamar yanda Aishan ta fada.
Sukayi shiru na dan lokaci, Baffa yace
'To tazo da wasu dalilai wadanda suka sa take jin ba zata iya zama da yarinyar ba, amma gata nan sai tayi bayani a gabanka kaji.’
A nan Baffa ya bawa Aishan umarni tayi bayanin abubuwan da Yusran takeyi mata da ma wasu abubuwan na cutarwa da Zahran ta dinga yi mata. Ta dora da
'Duk abinda za ayi kuma ita ake turowa ta shigo min da shi gida. Sannan kuma kullum muka hadu da ita sai ta gaya min bakar magana don kawai ina kawar da kai ne.’
Baffa yace
'Wannan maganar zargi a barta tunda kinga malamai ma sun ce wasu abubuwan aljanu ke son cutar da kai sai su nuna maka cewa wani ne daka sani.’
Tace
'Baffa wasu abubuwan idan tayi min da kanta take gaya min ko ta aiko Yusran ta gaya min.’
Kafin suce wani abu ta zaro waya ta kunna recording din da suka tsinta dazu na muryar Zahra. Kowa yayi kasake yana sauraro. Abba ya sunkuyar da kai zuciyarsa tana kara kuntata, muguntar Zahra da jahilcinta har ya kai haka?
Suna gama ji Yaya Bello yayi gyaran murya yace
'To Baffa dama muma hakuri muka zo mu bayar, kana zaune da mutum ne bisa kyautatatwar zato baka gane lokacin da yake sauyawa. Wadannan matsololi duk mun ji kuma ita Yusra da kanwarta Nana da ake magana in sha Allahu gidana zasu koma in ya so sai suyi zamansu da sauran yaran. Yanzu dai ana gyara a cikin gidan nan da sati biyu za a gama in ya so ita Aishan sai ta koma.’
Cikin farin ciki Baffa yace
'To Alhamdulillah, hakan yayi. Allah ya shirya mana zuri'a da mu gaba daya.’
Ya dubi Aisha yace
'Shatu ki dinga hakuri kin ji, yaro ko naka ne wanda ka haifa wani sai dai kayi hakuri da shi a lallaba. Bana jin ki da yara sai dai mu raka ku da addu'a, tunda gashi ita da take baki matsala bata nan don Allah sauran kuyi zamanku lafiya. Kuma ku sani mutum yana barin mugun hali ya shiryu musamman wanda ake tsaye ana masa addu'a don haka idan ta canza hali ita din ma duk ki hadasu ki rungume.’
Tace
'To Baffa.'
Yaya Bello yace
‘Akwai kuma yaran wajen Aishan su biyu idan babu damuwa sai ta taho da su duk su hadu a nan suyi zamansu gaba daya.’
Yaya Abubakar yace
'Wadannan ma ba za ayi haka ba. 'yan uwan mahaifinsu suna so su karbesu tunda Farha da take karama yanzu shekarunta sha biyu, suna ganin ya kamata a basu yaransu. Kuma yaran sunyi na'ama don haka nan da wani dan lokaci zasu koma wajen kanin mahaifinsu.’
'To babu laifi hakan ma yayi.’
Suka yiwa su Baffan sallama suka fice.
Suna fita Yaya Uwani tace
'Tunda ya auri yarinyar yana kallon yaran bai taba cewa su zo su koma wajenta ba sai yanzu da yake so ya bata rikon nashi yaran, ko kunya babu wai su koma can. Hmmm!’
Baffa yayi gyaran murya yana murmushi yace
'Hajiya Uwani ayi mana afuwa dai, kin san wani lokacin son kan mu yana rufe mana ido da yawa.’
Itama tayi dariyar tace
'Allah ya bude muku ido to ko kwa ga gaskiya.’
Daga baya suka yi sallama kowa ya koma gida.
………..
Tun da suka fito Aisha ta kasa walwala sosai. Bata ji dadin yanda taga Abban ba; yayi wata rama gashi kamar ma bashi da lafiya. Ta ji haushin kanta da ta ki daukar wayarsa har ya gaji ya daina kiranta. A take tausayinsa ya kamata duk da bata san me yake damunsa ba. Bata da wata matsala da shi kuma zata koma kamar yanda ya fada, musamman da yake ya amince zai dauke Yusra.
Haka suka koma gida tana cike da damuwar halin da ta ga Abban. Tana son ta kirawoshi a waya to amma bata san me zata ce masa ba, don haka ta hakura ta kwanta bacci.
Wajen karfe sha daya da rabi wayarta tayi kara, lokacin bacci ya fara daukanta. Tayi firgigit ta farka ta dauki wayar tana dubawa, Abban Sadik ne yake kiranta don haka ta tashi a hankali ta fice daga dakin saboda kada ta tashi Anti Uwani da Farha daga bacci.
Ta amsa wayar ta kara a kunnenta dai-dai lokacin da ta karasa falon ta zauna a kan kujera.
Yanayin yanda ya kirawo sunanta sai da tsigar jikinta ta tashi. Ta gaisheshi sannan ta tambayeshi yaran, bayan ya gama amsa gaisuwar yace
'Aisha, me yasa kika ki daukan wayata?’
Bata da amsar da zata bashi don haka tayi shiru. Sai da ya gaji da shirun sannan ya cigaba
‘Kiyi hakuri ki daina fushi dani kin ji.’
'Ni ba fushi nake yi ba fa.’
'To me yasa kika daina kula ni?’
'Ni ban daina kula ka ba.’
Yayi murmushin da saida ta jiyo sautinsa yace
‘Gobe za a fara aiki, wane kalar fenti kike so?’
Itama murmushi tayi tace
'Ko wanne kala ma yayi.’
Sukayi shiru na dan lokaci jimawa kadan ya sake kiran sunanta, ta amsa murya kasa-kasa. Yace
'Ina son ganinki, ya za ayi?’
'Gobe kazo gida mana.’
'Ba a gida ba gaskiya, please idan kin tashi daga makaranta ki zo office mana.’
Sukayi shiru na dan lokaci bata amsa ba, ya gaji da shirun ya sake maimaita mata
'Ki zo office kin ji Aisha.’
Tace
'To, amma da ka zo gidan zamu fi samun time mu tattauna a nutse.’
'To kizo din sai mu wuce gidan daga nan.’
'Ok.'
Suka sake yin shiru na dan lokaci, jimawa kadan tace
'Wai baka da lafiya ne?’
Yace
'A'a. Me kika gani?’
'Na dai ga kamar baka da lafiya ne.’
Yayi murmushi mai sauti yace
'Tsabar damuwa ce kawai, mutum yana da mata biyu a wayi gari daya ta mutu dayar kuma ta gudu ai kin ga dole na shiga damuwa ko?’
'Ni fa ba guduwa nayu ba.’
Yayi dariya. Suka dan taba hira sannan sukayi sallama ta koma ta kwanta.
—----
Washegari ranar litinin tun kafin yara su tafi makaranta ya sanar da su idan sun dawo daga makaranta su hada kayansu zasu tafi gidan Yaya Bello sai an gama aiki a nan sannan zasu dawo. Itama Jummai ya sanar da ita an bata Hutu, idan yaran sun tafi gidan Yaya zata iya tafiya ta barwa Saddiku mukullin gidan idan an gama aiki zai kirawota. Ya kawo kudi naira dubu ashirin ya bata yace ta yi wata hidimar, ya fice ya barta tana godiya.
Tun kafin ya karasa office din ya kirawo Aisha don ya tabbatar bata fasa alkawarin da ta yi masa ba akan zasu hadu a office, inda ta tabbatar masa zata zo da karfe sha biyu da rabi.
………
A zaune yake a office din yana faman duba lokaci saboda yanda ya kagu yaga Aishan. Sha biyu daidai ya ajiye aikin da yakeyi ya dan kifa kansa a kan tebur, ba tare da bata lokaci ba bacci ya kwasheshi saboda yanda ya tara bacci da gajiya kwana biyu.
A haka ta shiga ta sameshi a office din, sai motsin shigarta ne ya tasheshi daga baccin. Ya muttsike idonsa tare da mikewa tsaye yana murmushi, ya zagayo gaban tebur din ya tsaya a gabanta yana dan tokarewa da tebur din. Ya kama hannuwanta duka biyun yana murmushi, ta mayar masa da murmushin sannan tace
'Tun daga gate na jiyo minsharinka.’
Yayi dariya yace
'Shikenan kuma da mutum ya kifa kai a tebur sai a ce bacci yakeyi.’
Tayi dariya tace
'Au ashe hutawa yake yi.’
Ya karasa mikewa ya sumbaci lebenta, tayi murmushi tace
'A office fa kake.’
'Ni da wa?’
'Ko kai da waye, kayi aiki kawai aka ce.’
‘Wannan ma duk cikin aiki ne.’
Ya saki hannunta ya mika hannu ya dauko mukullin motarsa da waya yana fadin
'Fita fa zanyi, muje ki rakani.’
Tayi dariya tace
'Ko dai na wuce in ya so da yamma sai ka sameni a gida.’
'Ban yarda ba. Kizo muje idan muka dawo sai ki wuce gidan.’
'Shikenan, ga kiran magriba nan mu tashi muyi shirin sallah.'
Ya tsallake su ya nufi daki yayinda su kuma suka nufi benen da nufin saukowa.
Tun a kafar benen Yusra ta fara mita ita kadai
'Wallahi bata isa na bata hakuri ba, ni da gidan ubana na ga wanda zai koreni sai dai kowa ya koma gidan ubansa wallahi.’
Har ya murda kofar dakin zai shiga sai kuma ya fasa ya dawo ya samesu a kafar bene don haka duk abinda Yusra ta fada ya ji. Bai kula da ita ba yace
'Sadik idan ka shirya ka jira ni mu tafi masallacin tare.’
Suka wuce shi kuma ya koma dakin yana mamakin Yusra.
Bai taba sanin lalacewar Yusra ta kai haka ba, tun kafin ma aje ko ina ta sanar ba zata bi umarninsa ba. Lallai gara ya barta taje gidan Yaya Bello don ya san ba zai yi mata a hankali ba. Watakila idan ya cigaba da addu'a Allah ya sa ta canza hali.
Nan da nan ya shirya suka tafi masallaci tare da Saddikun, suna dawowa ya shirya ya wuce gidan Yaya Bello.
……….
Tun a hanya ya sanar da Yaya Bellon yanda suka yi da Yusra, nan suka yanke maganar cewa kawai Yusra da Nana su dawo gidan Yayan.
Suna isa suka tarar Baffa da Yaya Abubakar suna jiransu.
A falon Baffa suka zauna gaba daya; Aisha, Anti Uwani da Zahida suna gefe yayinda Baffa da Ya Abubakar suke gefe sai Abban da Yaya Bello da suma suke gefe.
Tunda ya zauna yake kallon Aishan; tayi kyau tayi fes kamar bata da wata damuwa. Yanda yaki ya dauke idonsa daga kallonta ya sa ta sunkuyar da kai. Yaya Bello ne ya kula da halin da ake ciki ya tabo Abban.
Gaba dayansu suka gaisa da su Baffa da Anti Uwani.
Baffa yayi gyaran murya yace
'Yusufa me ya hadakane da amaryar taka har ta taho gida, duk da tace ba kaine kace ta taho ba?’
Nan ya mayarwa da Baffan yanda sukayi kamar yanda Aishan ta fada.
Sukayi shiru na dan lokaci, Baffa yace
'To tazo da wasu dalilai wadanda suka sa take jin ba zata iya zama da yarinyar ba, amma gata nan sai tayi bayani a gabanka kaji.’
A nan Baffa ya bawa Aishan umarni tayi bayanin abubuwan da Yusran takeyi mata da ma wasu abubuwan na cutarwa da Zahran ta dinga yi mata. Ta dora da
'Duk abinda za ayi kuma ita ake turowa ta shigo min da shi gida. Sannan kuma kullum muka hadu da ita sai ta gaya min bakar magana don kawai ina kawar da kai ne.’
Baffa yace
'Wannan maganar zargi a barta tunda kinga malamai ma sun ce wasu abubuwan aljanu ke son cutar da kai sai su nuna maka cewa wani ne daka sani.’
Tace
'Baffa wasu abubuwan idan tayi min da kanta take gaya min ko ta aiko Yusran ta gaya min.’
Kafin suce wani abu ta zaro waya ta kunna recording din da suka tsinta dazu na muryar Zahra. Kowa yayi kasake yana sauraro. Abba ya sunkuyar da kai zuciyarsa tana kara kuntata, muguntar Zahra da jahilcinta har ya kai haka?
Suna gama ji Yaya Bello yayi gyaran murya yace
'To Baffa dama muma hakuri muka zo mu bayar, kana zaune da mutum ne bisa kyautatatwar zato baka gane lokacin da yake sauyawa. Wadannan matsololi duk mun ji kuma ita Yusra da kanwarta Nana da ake magana in sha Allahu gidana zasu koma in ya so sai suyi zamansu da sauran yaran. Yanzu dai ana gyara a cikin gidan nan da sati biyu za a gama in ya so ita Aishan sai ta koma.’
Cikin farin ciki Baffa yace
'To Alhamdulillah, hakan yayi. Allah ya shirya mana zuri'a da mu gaba daya.’
Ya dubi Aisha yace
'Shatu ki dinga hakuri kin ji, yaro ko naka ne wanda ka haifa wani sai dai kayi hakuri da shi a lallaba. Bana jin ki da yara sai dai mu raka ku da addu'a, tunda gashi ita da take baki matsala bata nan don Allah sauran kuyi zamanku lafiya. Kuma ku sani mutum yana barin mugun hali ya shiryu musamman wanda ake tsaye ana masa addu'a don haka idan ta canza hali ita din ma duk ki hadasu ki rungume.’
Tace
'To Baffa.'
Yaya Bello yace
‘Akwai kuma yaran wajen Aishan su biyu idan babu damuwa sai ta taho da su duk su hadu a nan suyi zamansu gaba daya.’
Yaya Abubakar yace
'Wadannan ma ba za ayi haka ba. 'yan uwan mahaifinsu suna so su karbesu tunda Farha da take karama yanzu shekarunta sha biyu, suna ganin ya kamata a basu yaransu. Kuma yaran sunyi na'ama don haka nan da wani dan lokaci zasu koma wajen kanin mahaifinsu.’
'To babu laifi hakan ma yayi.’
Suka yiwa su Baffan sallama suka fice.
Suna fita Yaya Uwani tace
'Tunda ya auri yarinyar yana kallon yaran bai taba cewa su zo su koma wajenta ba sai yanzu da yake so ya bata rikon nashi yaran, ko kunya babu wai su koma can. Hmmm!’
Baffa yayi gyaran murya yana murmushi yace
'Hajiya Uwani ayi mana afuwa dai, kin san wani lokacin son kan mu yana rufe mana ido da yawa.’
Itama tayi dariyar tace
'Allah ya bude muku ido to ko kwa ga gaskiya.’
Daga baya suka yi sallama kowa ya koma gida.
………..
Tun da suka fito Aisha ta kasa walwala sosai. Bata ji dadin yanda taga Abban ba; yayi wata rama gashi kamar ma bashi da lafiya. Ta ji haushin kanta da ta ki daukar wayarsa har ya gaji ya daina kiranta. A take tausayinsa ya kamata duk da bata san me yake damunsa ba. Bata da wata matsala da shi kuma zata koma kamar yanda ya fada, musamman da yake ya amince zai dauke Yusra.
Haka suka koma gida tana cike da damuwar halin da ta ga Abban. Tana son ta kirawoshi a waya to amma bata san me zata ce masa ba, don haka ta hakura ta kwanta bacci.
Wajen karfe sha daya da rabi wayarta tayi kara, lokacin bacci ya fara daukanta. Tayi firgigit ta farka ta dauki wayar tana dubawa, Abban Sadik ne yake kiranta don haka ta tashi a hankali ta fice daga dakin saboda kada ta tashi Anti Uwani da Farha daga bacci.
Ta amsa wayar ta kara a kunnenta dai-dai lokacin da ta karasa falon ta zauna a kan kujera.
Yanayin yanda ya kirawo sunanta sai da tsigar jikinta ta tashi. Ta gaisheshi sannan ta tambayeshi yaran, bayan ya gama amsa gaisuwar yace
'Aisha, me yasa kika ki daukan wayata?’
Bata da amsar da zata bashi don haka tayi shiru. Sai da ya gaji da shirun sannan ya cigaba
‘Kiyi hakuri ki daina fushi dani kin ji.’
'Ni ba fushi nake yi ba fa.’
'To me yasa kika daina kula ni?’
'Ni ban daina kula ka ba.’
Yayi murmushin da saida ta jiyo sautinsa yace
‘Gobe za a fara aiki, wane kalar fenti kike so?’
Itama murmushi tayi tace
'Ko wanne kala ma yayi.’
Sukayi shiru na dan lokaci jimawa kadan ya sake kiran sunanta, ta amsa murya kasa-kasa. Yace
'Ina son ganinki, ya za ayi?’
'Gobe kazo gida mana.’
'Ba a gida ba gaskiya, please idan kin tashi daga makaranta ki zo office mana.’
Sukayi shiru na dan lokaci bata amsa ba, ya gaji da shirun ya sake maimaita mata
'Ki zo office kin ji Aisha.’
Tace
'To, amma da ka zo gidan zamu fi samun time mu tattauna a nutse.’
'To kizo din sai mu wuce gidan daga nan.’
'Ok.'
Suka sake yin shiru na dan lokaci, jimawa kadan tace
'Wai baka da lafiya ne?’
Yace
'A'a. Me kika gani?’
'Na dai ga kamar baka da lafiya ne.’
Yayi murmushi mai sauti yace
'Tsabar damuwa ce kawai, mutum yana da mata biyu a wayi gari daya ta mutu dayar kuma ta gudu ai kin ga dole na shiga damuwa ko?’
'Ni fa ba guduwa nayu ba.’
Yayi dariya. Suka dan taba hira sannan sukayi sallama ta koma ta kwanta.
—----
Washegari ranar litinin tun kafin yara su tafi makaranta ya sanar da su idan sun dawo daga makaranta su hada kayansu zasu tafi gidan Yaya Bello sai an gama aiki a nan sannan zasu dawo. Itama Jummai ya sanar da ita an bata Hutu, idan yaran sun tafi gidan Yaya zata iya tafiya ta barwa Saddiku mukullin gidan idan an gama aiki zai kirawota. Ya kawo kudi naira dubu ashirin ya bata yace ta yi wata hidimar, ya fice ya barta tana godiya.
Tun kafin ya karasa office din ya kirawo Aisha don ya tabbatar bata fasa alkawarin da ta yi masa ba akan zasu hadu a office, inda ta tabbatar masa zata zo da karfe sha biyu da rabi.
………
A zaune yake a office din yana faman duba lokaci saboda yanda ya kagu yaga Aishan. Sha biyu daidai ya ajiye aikin da yakeyi ya dan kifa kansa a kan tebur, ba tare da bata lokaci ba bacci ya kwasheshi saboda yanda ya tara bacci da gajiya kwana biyu.
A haka ta shiga ta sameshi a office din, sai motsin shigarta ne ya tasheshi daga baccin. Ya muttsike idonsa tare da mikewa tsaye yana murmushi, ya zagayo gaban tebur din ya tsaya a gabanta yana dan tokarewa da tebur din. Ya kama hannuwanta duka biyun yana murmushi, ta mayar masa da murmushin sannan tace
'Tun daga gate na jiyo minsharinka.’
Yayi dariya yace
'Shikenan kuma da mutum ya kifa kai a tebur sai a ce bacci yakeyi.’
Tayi dariya tace
'Au ashe hutawa yake yi.’
Ya karasa mikewa ya sumbaci lebenta, tayi murmushi tace
'A office fa kake.’
'Ni da wa?’
'Ko kai da waye, kayi aiki kawai aka ce.’
‘Wannan ma duk cikin aiki ne.’
Ya saki hannunta ya mika hannu ya dauko mukullin motarsa da waya yana fadin
'Fita fa zanyi, muje ki rakani.’
Tayi dariya tace
'Ko dai na wuce in ya so da yamma sai ka sameni a gida.’
'Ban yarda ba. Kizo muje idan muka dawo sai ki wuce gidan.’