Sashe 27
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kafin yace wani abu ta ajiye wayar tana murmushin takaici; batayi mamakin hakan ba domin idan wannan munafukar matar ce mai fuska biyu abinda yafi haka ma zata iya yi tunda wanda take kunya baya nan. Haka ta mike ta fita ta hau motar haya ta kama hanyar makaranta.
Tana tashi daga makarantar kuwa ta wuce gidan Yaya Zainab, can ta wuni sai bayan la’asar suka taho tare da Amira.
……….
Tun kafin sallar azahar dan aiken
Malam Hatimu ya iso, babu kowa a gidan daga ita sai Jummai. Maigadi ne ya shiga ya sanar da su akwai yaro da yace an aiko shi wajen Hajiya.
Nan da nan ta sa aka shigo da shi bakin kofar falo, ko gaisawa basuyi ba ta karbi sakon wanda yake a nannade a bakar leda ta bashi naira dubu uku tace ya hau mota.
Yayi godiya ya tafi.
Tun lokacin take tunanin yanda za ayi ta aika Yusra ta jefa wannan abun a toilet. Tun lokacin da ta fasa mata murfin tukunya Yusran ta daina shiga gidan, gashi jiya batayi tunani ba ta aika suka taho da Rukayya. Da ta sani ma da ta bari in ya so yau din sai su yi amfani da wannan damar a jefa maganin kuma a taho da Rukayya. Rukayyan ta riga ta bawa Mommy tabbacin a dakin baki suke kwana don haka a nan ne take so a jefe layar tunda ta san shiga dakin Aishan zai yi wahala. Amma in dai tana kwana a dakin bakin to tabbas ko cikin dare sai ta shiga bandakin.
Suna zaune a falo suna kallon TV bayan magriba Rukayya ta dubi Mommy cikin sanyin murya tace
‘Mommy, kayana fa suna gidan Anti kuma harda books dina ina son naje na dauko don gobe da su zanje school.’
Bude baki tayi zata yi mata tsawa sai kuma ta tuna dama tana neman damar da zata yi aike gidan, ta dubeta tace
‘To, bari Yayarki ta rakaki ku dauko.’
Ta mike tana fadin
‘Ina zuwa.’
Sai da ta hau sama sannan ta kwalawa Yusra kira, tana zuwa ta jata daki.
Layar ta bata a hannunta tayi mata bayani yanda zata yi mata da ita, bayan ta gama bayanin tace
‘Ki kula fa kada wanda ya gani, idan ta wuce ko bakiyi flushing ba babu matsala amma idan kinga bata wuce ba to ki kora.’
Ta amsa
‘To.’
Har ta juyo zata fito ta juya tace
‘Mommy layar ta mecece?’
Ta harareta tace
‘Ina ruwanki? Kiyi abinda aka saka ki kawai.’
Ta juya ta fice ba tare da tace komai ba.
Falon kasa ta dawo ta zauna bayan ta nade layar a siket dinta, ta cigaba da harkarta kamar yanda Mommy din ta tsara mata. Jimawa kadan Mommy din ta sauko, tana zama ta dubesu tace
‘Kuje ku debo kayan Rukayyan, maza kada ku bata lokaci.’
Ta harari Rukayyan tace
‘Saura ki zauna wani shisshigin.’
Suka tashi suka fice.
………
Suna zaune ita da Amira a falo suka ji bugu, ta tashi ta bude kofar. Kamar yanda Yusra ta saba ko gaisheta bata yi ba ta sa kai cikin gidan, Rukayya ce ta gaisheta sannan a kunyace tace
‘Kayana Mommy tace mu debo.’
Ta dafa kafadarta tace
‘To muje ku diba, suna nan a inda kika barsu.’
Suna shiga falon Aishan ta zauna a kan kujera tace
‘Kuje ku debo.’
Suka nufi dakin baki inda nan ne kayan Rukayyan suke.
Suna shigewa Aisha ta dubi Amira tace
‘Bisu Amira, ki sa min ido musamman a kan Babbar.’
Nan take ta tashi ta wuce, Rukayya na tsaye a gaban wardrobe tana fito da kayanta wadanda dama ba yawa ne da su ba yayinda Amira take jingine a jikin mudubi wanda yake kusa da kofar bandaki. Amira tana shiga ta wuce ta zauna a gefen gado, ta kula da yanda Yusra take mata kallon raini don haka itama ta tsare gida.
Bayan ta gama fito da kayan daga wardrobe din ta dauki jakarta ta makaranta ta bude kamar tana neman wani abu. Ta dubi Yusra tace
‘Yaya Yusra dan zuba min kayan a ledar gata nan kusa dake, bari na tambayi Anti books din da nayi homework naga bata sa min a nan ba.’
Kafin Yusran ta amsa ta fice tana dauke da jakar.
Tana fita Yusran taja tsaki
‘Ki kwashi kaya kawai sai kin bata mana lokaci.’
Ta dubi Amira tana kokarin bude bandaki tace
‘Bari nayi fitsari.’
Tayi wuf da shige bandakin ta turo kofar, tana shiga ta jefa layar a toilet tayi maza ta kora. Ta tsaya a gaban sink ta wanke hannunta ta danyi jinkiri sannan ta fito.
A dai-dai lokacin Rukayyan ta shigo tana rufe jakarta wadda cake dinta ne taje ta juyo tana fatan Mommy ba zata gani ba in ya so gobe in taje makaranta sai su cinye ita da kawayenta.
Tana shigowa suka karasa hada kayan suka kwasa suka fice.
Suna fitowa falo Rukayyan ta yiwa Aisha sai da safe, har sun kusan fita daga falon Aisha tace
‘Rukayya idan kin je ki kunno min ruwa idan tankin ya cika zan bugo waya sai a kashe.’
Ta amsa suka fice.
Gida daya ne tsakanin gidan Zahra da na Aisha don haka bai sake hada ruwa ba a gidan Aisha. Sai dai kawai aka hada tankin gidan Aisha da injin jan ruwa a can gidan. Kafin ya tafi Hajji kullum da suba yake kunna ruwan tankunan su cika ya kashe daga can ko kuma da daddare idan ba a can ya kwana ba. Tun ana i gobe zai tafi ya manta bai kunna ba, ranar dazai tafi ma haka ya sake mantawa har ya tafi. Ya gayawa Sadik ya dinga kunnawa kullum, sai dai yana tafiya Sadik din ya murder wata waya ta yanda in ya kunna injin iya tankin gidansu kawai zai cika. Don haka ko da suka shiga gidan Rukayya ta kunna injin tankin gidansu ne kawai ya sake cika aka kashe.
-------
Sai wajen tara da rabi lokacin ma Amira ta fara gyangyadi a falon, suka wuce daki suka kwanta. Bayan sun shiga dakin saida ta duba ko ina ta daga katifa ta daga kafet don ta tabbatar Yusra bata binne mata wani abu ba sannan suka kwanta.
Can wajen Sha biyu da Rabi na dare fitsari ya matseta, tana tashi ta shiga bandakin da yake nan dakin tayi fitsarin ta dawo ta kwanta. Minti goma Sha biyar da kwanciyarta taji kamar ana karta wani abu a mararta, ta tashi zaune ta dafe mara ta takure a waje guda tana fitar da numfashi da kyar.
A firgice Amira ta farka, bata gani sosai saboda duhu haka ta lalubota ta tabata tana fadin
‘Anti baki da lafiya?’
Da kyar ta amsa.
Take Amira ta tashi ta lalubi fitila ta kunna, ta karaso kusa da Aishan da gudu ta dafata ta rasa me zata ce mata don haka ta fara kwalla. Ta kama hannunta tace
‘Kiyi shiru Amira cikina ne yake ciwo ba komai.’
Ta dan share hawayen amma dai ta kasa nutsuwa.
Sun kai wajen minti talatin a haka Aishan tana ta addu’a , a hankali ciwon ya fara lafa mata. Har bacci ya fara kwasarta mararta ta kara katawa.
Ta yunkura saboda aman da ya taso mata, sai kuma taji ta jike. Ta ture Amira ta mike tana fadin
‘Kwanta Amira Ina zuwa.’
Kafin tace wani abu ta shige bandaki.
A kasa ta tsuguna tana ji jini yana bin jikinta, ta taba yin bari kafin ta haifi Abdallah don haka yanzun ma ta san abinda yake faruwa da ita. Ta kai kamar minti goma Sha biyar tana murkususu a bandakin nan, Amira tana bakin kofa tana jiranta cike da tsananin tashin hankali. Daga nan bakin kofar Amira tace
‘Anti na kirawo Mami a wayarki?’
Da kyar ta bude baki tace
‘A’a Amira bari na fito sai mu gani.’
Jimawa kadan taji gudan tayin cikin ya fado.
Ta yunkura ta mike da kyar ta karasa gaban toilet din, ta sabule dogon wandon kayan baccinta ta nade jinin da ta fitar a ciki sannan ta hau toilet din ta zauna. Mararta tana kara murdawa tana matsawa jini yana sake fita, a haka har abun ya fara lafa mata.
A hankali ta fara dawowa dai-dai, ta kirawo Amira wadda dama tana bakin kofa tace taje bandakinta ta dauko mata pad. Ta janyo abun tsarki don ta wanke jikinta tana murdawa taji babu ruwa.
‘Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun.’
Tabbas ta san Zahra ta hana a kunna mata ruwan kenan, dama taga ya ja baya shi yasa tace Rukayya ta kunna. Tunda tazo gidan nan bata taba murda fanfo ta ji babu ruwa ba sai yau, tana cikin wannan halin da take bukatar ruwa.
Amira ce ta katse mata tunanin ta kwankwasa kofar ta tura mata pad din. Ta dauke pad din ta yiwa Amira bayani akwai ruwa a bokitin fenti a bandakinta da kuma wani a kicin tace ta dauko mata su, in ba zata iya saukowa ba ta sami roba a kicin ta dinga debowa. Haka Amira ta kawo mata ruwan nan ta samu ta wanke jikinta ta kora toilet din ta goge sannan ta saka pad din ta dauro zanin da Amiran ta mika mata ta fito ta kwanta a jigace.
Amira ta dafata tace
‘Sannu Anti.’
Ta bude ruwan robar da ta dauko ta mika mata ta, karba ta sha kadan ta mayar mata.
‘Anti na kirawo Mami?’
‘Ki barsu Amira, da anyi asuba sai mu kirawosu. Yanzu tayar musu da hankali kawai zamuyi ba zasu iya zuwa ba kinga biyun dare ce zata yi.’
Haka suka kwanta ita da Amira, a hankali bacci ya kwashesu.
UWAR SADDIKU
Written by Sakina Yazid
(Innar su Amal)
17
Saida gari ya gama wayewa sannan Aisha ta kirawo Yaya Zainab, direbanta yana dawowa daga kai yara makaranta ta kamo hanyar gidan Aisha. Kafin ta zo Amira ta dafa musu shayi sun sha sun canza kayansu duk da basu sami ruwan wanka ba. Yaya Zainab tana zuwa suka wuce asibiti.
A can likita ya dubata aka ce cikin ya zube gaba daya don haka sai aka yi mata allura aka rubuta mata magunguna suka dawo gidan.
Suna zuwa gida Yaya Zuwaira ta karaso suka hadu.
Tana tashi daga makarantar kuwa ta wuce gidan Yaya Zainab, can ta wuni sai bayan la’asar suka taho tare da Amira.
……….
Tun kafin sallar azahar dan aiken
Malam Hatimu ya iso, babu kowa a gidan daga ita sai Jummai. Maigadi ne ya shiga ya sanar da su akwai yaro da yace an aiko shi wajen Hajiya.
Nan da nan ta sa aka shigo da shi bakin kofar falo, ko gaisawa basuyi ba ta karbi sakon wanda yake a nannade a bakar leda ta bashi naira dubu uku tace ya hau mota.
Yayi godiya ya tafi.
Tun lokacin take tunanin yanda za ayi ta aika Yusra ta jefa wannan abun a toilet. Tun lokacin da ta fasa mata murfin tukunya Yusran ta daina shiga gidan, gashi jiya batayi tunani ba ta aika suka taho da Rukayya. Da ta sani ma da ta bari in ya so yau din sai su yi amfani da wannan damar a jefa maganin kuma a taho da Rukayya. Rukayyan ta riga ta bawa Mommy tabbacin a dakin baki suke kwana don haka a nan ne take so a jefe layar tunda ta san shiga dakin Aishan zai yi wahala. Amma in dai tana kwana a dakin bakin to tabbas ko cikin dare sai ta shiga bandakin.
Suna zaune a falo suna kallon TV bayan magriba Rukayya ta dubi Mommy cikin sanyin murya tace
‘Mommy, kayana fa suna gidan Anti kuma harda books dina ina son naje na dauko don gobe da su zanje school.’
Bude baki tayi zata yi mata tsawa sai kuma ta tuna dama tana neman damar da zata yi aike gidan, ta dubeta tace
‘To, bari Yayarki ta rakaki ku dauko.’
Ta mike tana fadin
‘Ina zuwa.’
Sai da ta hau sama sannan ta kwalawa Yusra kira, tana zuwa ta jata daki.
Layar ta bata a hannunta tayi mata bayani yanda zata yi mata da ita, bayan ta gama bayanin tace
‘Ki kula fa kada wanda ya gani, idan ta wuce ko bakiyi flushing ba babu matsala amma idan kinga bata wuce ba to ki kora.’
Ta amsa
‘To.’
Har ta juyo zata fito ta juya tace
‘Mommy layar ta mecece?’
Ta harareta tace
‘Ina ruwanki? Kiyi abinda aka saka ki kawai.’
Ta juya ta fice ba tare da tace komai ba.
Falon kasa ta dawo ta zauna bayan ta nade layar a siket dinta, ta cigaba da harkarta kamar yanda Mommy din ta tsara mata. Jimawa kadan Mommy din ta sauko, tana zama ta dubesu tace
‘Kuje ku debo kayan Rukayyan, maza kada ku bata lokaci.’
Ta harari Rukayyan tace
‘Saura ki zauna wani shisshigin.’
Suka tashi suka fice.
………
Suna zaune ita da Amira a falo suka ji bugu, ta tashi ta bude kofar. Kamar yanda Yusra ta saba ko gaisheta bata yi ba ta sa kai cikin gidan, Rukayya ce ta gaisheta sannan a kunyace tace
‘Kayana Mommy tace mu debo.’
Ta dafa kafadarta tace
‘To muje ku diba, suna nan a inda kika barsu.’
Suna shiga falon Aishan ta zauna a kan kujera tace
‘Kuje ku debo.’
Suka nufi dakin baki inda nan ne kayan Rukayyan suke.
Suna shigewa Aisha ta dubi Amira tace
‘Bisu Amira, ki sa min ido musamman a kan Babbar.’
Nan take ta tashi ta wuce, Rukayya na tsaye a gaban wardrobe tana fito da kayanta wadanda dama ba yawa ne da su ba yayinda Amira take jingine a jikin mudubi wanda yake kusa da kofar bandaki. Amira tana shiga ta wuce ta zauna a gefen gado, ta kula da yanda Yusra take mata kallon raini don haka itama ta tsare gida.
Bayan ta gama fito da kayan daga wardrobe din ta dauki jakarta ta makaranta ta bude kamar tana neman wani abu. Ta dubi Yusra tace
‘Yaya Yusra dan zuba min kayan a ledar gata nan kusa dake, bari na tambayi Anti books din da nayi homework naga bata sa min a nan ba.’
Kafin Yusran ta amsa ta fice tana dauke da jakar.
Tana fita Yusran taja tsaki
‘Ki kwashi kaya kawai sai kin bata mana lokaci.’
Ta dubi Amira tana kokarin bude bandaki tace
‘Bari nayi fitsari.’
Tayi wuf da shige bandakin ta turo kofar, tana shiga ta jefa layar a toilet tayi maza ta kora. Ta tsaya a gaban sink ta wanke hannunta ta danyi jinkiri sannan ta fito.
A dai-dai lokacin Rukayyan ta shigo tana rufe jakarta wadda cake dinta ne taje ta juyo tana fatan Mommy ba zata gani ba in ya so gobe in taje makaranta sai su cinye ita da kawayenta.
Tana shigowa suka karasa hada kayan suka kwasa suka fice.
Suna fitowa falo Rukayyan ta yiwa Aisha sai da safe, har sun kusan fita daga falon Aisha tace
‘Rukayya idan kin je ki kunno min ruwa idan tankin ya cika zan bugo waya sai a kashe.’
Ta amsa suka fice.
Gida daya ne tsakanin gidan Zahra da na Aisha don haka bai sake hada ruwa ba a gidan Aisha. Sai dai kawai aka hada tankin gidan Aisha da injin jan ruwa a can gidan. Kafin ya tafi Hajji kullum da suba yake kunna ruwan tankunan su cika ya kashe daga can ko kuma da daddare idan ba a can ya kwana ba. Tun ana i gobe zai tafi ya manta bai kunna ba, ranar dazai tafi ma haka ya sake mantawa har ya tafi. Ya gayawa Sadik ya dinga kunnawa kullum, sai dai yana tafiya Sadik din ya murder wata waya ta yanda in ya kunna injin iya tankin gidansu kawai zai cika. Don haka ko da suka shiga gidan Rukayya ta kunna injin tankin gidansu ne kawai ya sake cika aka kashe.
-------
Sai wajen tara da rabi lokacin ma Amira ta fara gyangyadi a falon, suka wuce daki suka kwanta. Bayan sun shiga dakin saida ta duba ko ina ta daga katifa ta daga kafet don ta tabbatar Yusra bata binne mata wani abu ba sannan suka kwanta.
Can wajen Sha biyu da Rabi na dare fitsari ya matseta, tana tashi ta shiga bandakin da yake nan dakin tayi fitsarin ta dawo ta kwanta. Minti goma Sha biyar da kwanciyarta taji kamar ana karta wani abu a mararta, ta tashi zaune ta dafe mara ta takure a waje guda tana fitar da numfashi da kyar.
A firgice Amira ta farka, bata gani sosai saboda duhu haka ta lalubota ta tabata tana fadin
‘Anti baki da lafiya?’
Da kyar ta amsa.
Take Amira ta tashi ta lalubi fitila ta kunna, ta karaso kusa da Aishan da gudu ta dafata ta rasa me zata ce mata don haka ta fara kwalla. Ta kama hannunta tace
‘Kiyi shiru Amira cikina ne yake ciwo ba komai.’
Ta dan share hawayen amma dai ta kasa nutsuwa.
Sun kai wajen minti talatin a haka Aishan tana ta addu’a , a hankali ciwon ya fara lafa mata. Har bacci ya fara kwasarta mararta ta kara katawa.
Ta yunkura saboda aman da ya taso mata, sai kuma taji ta jike. Ta ture Amira ta mike tana fadin
‘Kwanta Amira Ina zuwa.’
Kafin tace wani abu ta shige bandaki.
A kasa ta tsuguna tana ji jini yana bin jikinta, ta taba yin bari kafin ta haifi Abdallah don haka yanzun ma ta san abinda yake faruwa da ita. Ta kai kamar minti goma Sha biyar tana murkususu a bandakin nan, Amira tana bakin kofa tana jiranta cike da tsananin tashin hankali. Daga nan bakin kofar Amira tace
‘Anti na kirawo Mami a wayarki?’
Da kyar ta bude baki tace
‘A’a Amira bari na fito sai mu gani.’
Jimawa kadan taji gudan tayin cikin ya fado.
Ta yunkura ta mike da kyar ta karasa gaban toilet din, ta sabule dogon wandon kayan baccinta ta nade jinin da ta fitar a ciki sannan ta hau toilet din ta zauna. Mararta tana kara murdawa tana matsawa jini yana sake fita, a haka har abun ya fara lafa mata.
A hankali ta fara dawowa dai-dai, ta kirawo Amira wadda dama tana bakin kofa tace taje bandakinta ta dauko mata pad. Ta janyo abun tsarki don ta wanke jikinta tana murdawa taji babu ruwa.
‘Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun.’
Tabbas ta san Zahra ta hana a kunna mata ruwan kenan, dama taga ya ja baya shi yasa tace Rukayya ta kunna. Tunda tazo gidan nan bata taba murda fanfo ta ji babu ruwa ba sai yau, tana cikin wannan halin da take bukatar ruwa.
Amira ce ta katse mata tunanin ta kwankwasa kofar ta tura mata pad din. Ta dauke pad din ta yiwa Amira bayani akwai ruwa a bokitin fenti a bandakinta da kuma wani a kicin tace ta dauko mata su, in ba zata iya saukowa ba ta sami roba a kicin ta dinga debowa. Haka Amira ta kawo mata ruwan nan ta samu ta wanke jikinta ta kora toilet din ta goge sannan ta saka pad din ta dauro zanin da Amiran ta mika mata ta fito ta kwanta a jigace.
Amira ta dafata tace
‘Sannu Anti.’
Ta bude ruwan robar da ta dauko ta mika mata ta, karba ta sha kadan ta mayar mata.
‘Anti na kirawo Mami?’
‘Ki barsu Amira, da anyi asuba sai mu kirawosu. Yanzu tayar musu da hankali kawai zamuyi ba zasu iya zuwa ba kinga biyun dare ce zata yi.’
Haka suka kwanta ita da Amira, a hankali bacci ya kwashesu.
UWAR SADDIKU
Written by Sakina Yazid
(Innar su Amal)
17
Saida gari ya gama wayewa sannan Aisha ta kirawo Yaya Zainab, direbanta yana dawowa daga kai yara makaranta ta kamo hanyar gidan Aisha. Kafin ta zo Amira ta dafa musu shayi sun sha sun canza kayansu duk da basu sami ruwan wanka ba. Yaya Zainab tana zuwa suka wuce asibiti.
A can likita ya dubata aka ce cikin ya zube gaba daya don haka sai aka yi mata allura aka rubuta mata magunguna suka dawo gidan.
Suna zuwa gida Yaya Zuwaira ta karaso suka hadu.