Sashe 86
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana shiga gidan aka fara kiran Magriba, ta leka dakin Abban ta hangoshi yana nan yana bacci. Don haka ta karasa ta tasheshi saboda magriba. Tana yin Sallah ta fada kicin, nan da nan ta tuka tuwon semovita miyar kuka wadda ta sha busasshen kifi da nama. Ta hada ta ajiye a kan table sannan ta shiga wanka.
Bayan ta gama abinda takeyi ta dawo falo ta zauna tana jiransa. Karfe tara saura ta kalli agogon, har yanzu bai shigo ba? To ko ba zai ci abincin bane? Ta sake kallon wayarta sannan ta mayar da ita ta ajiye. Bata son ta kirawoshi domin bai saba ce mata zai dawo ya saba ba, ta san ba lallai ya kwana a wajenta ba domin tunda akayi rasuwar a can yake kwana kuma bata da matsala da hakan amma dai ta kasa gane dalilin da zai sakata ta dafa abinci kuma yaki zuwa. Har ta gaji da karatun wasikar jaki bai shigo ba don haka ta zuba abincinta ta fara ci.
Ko rabin abincin bata ci ba ta jiyo motsinsa a gate, ba tare da bata lokaci ba ya shigo falon da sallama. Bayan ya amsa sannu da zuwanta ya dubeta yana murmushi yace
'An gaji da jirana ko?’
Ta yi gajeran murmushi
'Yunwa nake ji shi yasa.’
Ta fara kokarin mikewa ya dakatar da ita yayinda ya ajiye wayar hannunsa da mukullai a kan kujera ya nufi dining table yana fadin
‘Yi zamanki ki gama zan zubo abincin, nima yunwa nake ji.’
Ta cigaba da cin abincinta yayinda shima ya zubo abincin a faranti ya dawo inda take ya zauna suna ci suna hira. Bayan sun gama cin abincin ta hada kwanukan ta kwashe sannan ta kawo masa shayi, ta zauna suka cigaba da hira.
Wajen sha daya saura ta mike tana hamma tace
'Ni kam bari naje na kwanta idan zaka fita kayi min magana wallahi bacci nake ji.’
Ba tare da ya kalleta ba yace
'A nan zan kwana ai, nima yanzu zan shigo.’
Da mamaki tace
'Yaran fa?’
'Ai Goggo Binta tana nan, sai jibi ne zata tafi. Ina tunanin ma na lallabata ta kara mana ko sati ne kafin nan kin gama shiryawa tunda kin ga idan tace dole jibi zata tafi to fa ko baki shirya ba dole ki koma can din in ya so a dinga kwashe kayan a hankali.’
Tace
'Uhm! To sai ka shigo.’
Ta shige dakin ta barshi a zaune.
Haka ta karasa shiryawa cikin sanyin jiki domin idan aka ce jibi zata koma gidan Zahra to tabbas akwai rigima don ba zata koma ba. Gashi ta rasa da kalaman da zata yi masa bayanin cewa ba zata koma ba don ta san ba zai fahimceta ba; a halin yanzu ma bata jin akwai wanda zai fahimceta. A iya shekarun da tayi a rayuwa ta ga matan aure da dama wadanda yaran miji ke hanasu zaman aure wadanda ba a taba yi musu adalci, bata jin nata labarin zai babanta. Wani lokacin sai taji kamar ta koma ta fara zama da su ta gani ko zaman zai yiwu, amma zuciyarta tana tuna mata idan ta fara sai ta fi shan wahalar bari don haka gara ma kawai kada ta fara.
Tana nan kwance tana karanta wasikar jaki ya shiga dakin ya sameta. Ba tare da wani bata lokaci ba ya shirya ya cimmata a kan gadon, lokacin har ta fara gyangyadi. Sai dai da yake ta san bukatar da ta kawoshi kuma ita din ma tayi kewarsa haka ta biye masa suna raba dare suna biyan bashi.
_
Tun kafin Abban ya sanar da Aisha zata koma gidan Zahra ya sanar da Jummai. Ya bata umarni a fitar da duk wasu kayan da suke dakin Saddiku ya kwashe ya kai gareji a gyara dakin don nan Aisha zata zauna kafin a gyara mata daki a sama. Nan da nan ba tare da bata lokaci da ta shiga aiki.
Tunda Rukayya taji wannan labarin ta kasa boye murnar ta, do da kanta ta dinga taya Jummai fitar da kayan dakin nan har aka gama. Yusra tana kallonsu tana kwafa musamman ya da taga Rukayyan tana ta rawar jiki.
Ranar litinin wadda tayi dai-dai da kwana shida da mutuwa ranar Abba ya umarci yara da suyi hakuri su koma makaranta. Musamman Aisha ta tashi da safe ta dafa musu abincin makaranta sannan tayiwa Abban waya ya turo Rukayya ta daukar musu. Haka ta zuzzuba musu kowa ya dauki nasa in banda Nana wadda tace ita indomie zata dafa.
Tun wuri Yusra ta dawo daga tata makarantar don haka ko da sauran yaran suka dawo wajen karfe biyu da rabi a gidan suka sameta. Bayan sun ci abinci Jummai ta taimakawa Nana, Ummi da Sumayya suka shirya suka wuce islamiyya. Basu dade da fita ba Rukayya ta shiga dakinsu na kasa inda ta sami Yusra a kashingide a kan gadonsu tana chatting a waya. Kai tsaye ta nufi wajen da ta ajiye jakar makarantar ta ta bude ta fara zaro littafanta. Yusra ta dubeta tace
'Ke bazaki islamiyyar bane?’
Ba tare da ta dubeta ba tace
'Eh, sai next week idan mun gama CA test a makarantar, yanzu ma karatu zan je nayi a gidan Anti sai dare zan dawo.’
Yusran ta tashi zaune a kan gadon a dai-dai lokacin da Rukayyan ta mayar da jakar ta rufe ta mike da litattafai a hannunta tana shirin ficewa daga dakin.
Yusran tace
'Kuma karatun ne ba zaki iya yi a nan ba duk fadin gidan nan dole sai kin je gidan da aka hanaki zuwa.’
Cikin halin ko in kula tace
'Eh, a can zan yi karatun sai dare zan dawo.’
'Lallai! Wato ke tun kafin ma Mommy ta kwana bakwai da barin duniya har kin fara karya dokokin da ta kafa miki ko, kamar daman jira kikeyi ta mutu ki koma inda ta hanaki zuwa.’
Cak ta tsaya a inda take ta juyo ta kalli Yusran yayinda idanuwanta suka cicciko da kwalla; kalaman yayar tata sun yi matukar yi mata ciwo a zuciya sai dai bata da wata amsa da zata iya bata. Ta ja hijabin jikinta ta goge kwallar da ta fado fuskarta ta juya ba tare da ta ce komai ba ta fice daga dakin. Tana fita ta tsaya a bayan kofar ta rasa me zata yi; tafiya zata yi kamar yanda tayi niyya ko kuwa ta hakura ta zauna a nan tayi karatun? Sai dai ta san idan ta zauna a gidan to da zarar Sumayya ta dawo daga islamiyya karatun ya kare. Domin a wajenta take zama kuma ko me take bukata haka Yusra zata ce taje Rukayya tayi mata.
Ta share hawayenta ta wuce tsakar gida inda ta jiyo motsin Goggo Binta da Jummai, ta sanar da su ta tafi gidan Anti Aisha sannan ta wuce cike da damuwa.
………
Yanda Aishan ta ganta cikin damuwa ya sa ta zata damuwar rasuwar ce don haka ta saka ta a gaba ta dinga bata baki tana yi mata nasiha har ta samu ta sami natsuwa. Ta sakata a gaba ta fara karatun wanda kusan tare suka yi shi.
Sai da akayi kiran Magriba tayi sallah taci abinci sannan ta koma gidan. Bata kula Yusra ba har dare yayi suka kwanta.
……….
Ranar Talata da safe kamar yanda Abba ya saba bayan ya shirya zai fita aiki ya tsaya a falo wajen Goggo Binta domin ya gaisheta. Bayan sun gaisa ta sanar da shi cewa gobe zata tafi, ba zata sami damar kara kwana ba. Sai dai tayi masa alkawarin idan an kwana biyu zata dawo. Nan ya nuna mata babu damuwa goben idan ta shirya Malam Ali zai kaita har can Sumaila shi da Saddiku, ya tabbatar mata da cewa kafin ma ta tafi Aishan zata dawo gidan.
Yayi mata sallama ya fice aiki.
Ya san Asiha ta riga tafi aiki don haka sai bayan da ya zauna a office sannan ya dauki waya ya kirawota, ya sanar da ita ya kamata da ta koma gida ta hada kayanta don daga yau zuwa gobe da safe yake so ta koma gidan Zahra saboda Goggo Binta zata tafi.
Bata iya ce masa komai ba sai dai tace masa idan ya dawo sayi maganar.
Sukayi sallama suka ajiye waya.
Haka ta karasa wunin ta a makaranta tana tunani rigimar da za ayi domin ita abu daya ta sani; ba zata zauna da Yusra da Nana ba domin Nana duk abinda Yusra ta sakata shi take yi.
__
Tun bayan rasuwar Zahra da Yaya Murja ta koma gida take tunanin makomar yaran. Ta yi tunanin Abba zai sa Aisha ta dawo gidan domin kula da su to amma hakan bai kwanta mata a rai ba. Bata san Aisha sosai ba sai ta hannun Zahra, a iya wannan sanin kuma bata taba jin wani alkhairi a kan Aishan ba. Hasali ma Zahran ta nuna musu cewa Aisha tana da sharri sannan kuma tana bin malamai sosai don ta mallake gidan. Don haka take jin bai kamata a bar ta da yaran ba sai dai idan hakan shi kadai ne zabinsu. Tana da labarai da yawa na irin haka yanda matar uba take mayar da yara kalar tausayi saboda rashin uwa kuma zata yi iya yinta ta tabbatar hakan bai faru da yaran Zahra ba; duk da ta san abu ne maii tsananin wahala.
Sun yi waya ta san gobe Goggo Binta zata tafi don haka yau ta tashi da niyyar zuwa gidan suyi sallama. Gidan Suwaiba ta fara zuwa don su tafi tare.
A dakin Suwaiban suka zauna ita Suwaiban tana canza kaya suna hira. Cikin damuwa Yaya Murja tacewa Suwaiban
‘Jiya da mukayi waya da Yusra tace Abbansu yace Aisha zata koma gidan amma dakin kasa ya sa a gyara mata.’
Suwaiba tace
'To Yaya ai idan ma dakin Ya Zahran yace ta shiga ba wani abu bane, na san ma hakan za ayi. Watakila dai yana jira ne ya sami lokaci a kwashe kayan a raba tun da ko ana so ko ba a so kayan da suke nata ne sun zama na magada.’
Bayan ta gama abinda takeyi ta dawo falo ta zauna tana jiransa. Karfe tara saura ta kalli agogon, har yanzu bai shigo ba? To ko ba zai ci abincin bane? Ta sake kallon wayarta sannan ta mayar da ita ta ajiye. Bata son ta kirawoshi domin bai saba ce mata zai dawo ya saba ba, ta san ba lallai ya kwana a wajenta ba domin tunda akayi rasuwar a can yake kwana kuma bata da matsala da hakan amma dai ta kasa gane dalilin da zai sakata ta dafa abinci kuma yaki zuwa. Har ta gaji da karatun wasikar jaki bai shigo ba don haka ta zuba abincinta ta fara ci.
Ko rabin abincin bata ci ba ta jiyo motsinsa a gate, ba tare da bata lokaci ba ya shigo falon da sallama. Bayan ya amsa sannu da zuwanta ya dubeta yana murmushi yace
'An gaji da jirana ko?’
Ta yi gajeran murmushi
'Yunwa nake ji shi yasa.’
Ta fara kokarin mikewa ya dakatar da ita yayinda ya ajiye wayar hannunsa da mukullai a kan kujera ya nufi dining table yana fadin
‘Yi zamanki ki gama zan zubo abincin, nima yunwa nake ji.’
Ta cigaba da cin abincinta yayinda shima ya zubo abincin a faranti ya dawo inda take ya zauna suna ci suna hira. Bayan sun gama cin abincin ta hada kwanukan ta kwashe sannan ta kawo masa shayi, ta zauna suka cigaba da hira.
Wajen sha daya saura ta mike tana hamma tace
'Ni kam bari naje na kwanta idan zaka fita kayi min magana wallahi bacci nake ji.’
Ba tare da ya kalleta ba yace
'A nan zan kwana ai, nima yanzu zan shigo.’
Da mamaki tace
'Yaran fa?’
'Ai Goggo Binta tana nan, sai jibi ne zata tafi. Ina tunanin ma na lallabata ta kara mana ko sati ne kafin nan kin gama shiryawa tunda kin ga idan tace dole jibi zata tafi to fa ko baki shirya ba dole ki koma can din in ya so a dinga kwashe kayan a hankali.’
Tace
'Uhm! To sai ka shigo.’
Ta shige dakin ta barshi a zaune.
Haka ta karasa shiryawa cikin sanyin jiki domin idan aka ce jibi zata koma gidan Zahra to tabbas akwai rigima don ba zata koma ba. Gashi ta rasa da kalaman da zata yi masa bayanin cewa ba zata koma ba don ta san ba zai fahimceta ba; a halin yanzu ma bata jin akwai wanda zai fahimceta. A iya shekarun da tayi a rayuwa ta ga matan aure da dama wadanda yaran miji ke hanasu zaman aure wadanda ba a taba yi musu adalci, bata jin nata labarin zai babanta. Wani lokacin sai taji kamar ta koma ta fara zama da su ta gani ko zaman zai yiwu, amma zuciyarta tana tuna mata idan ta fara sai ta fi shan wahalar bari don haka gara ma kawai kada ta fara.
Tana nan kwance tana karanta wasikar jaki ya shiga dakin ya sameta. Ba tare da wani bata lokaci ba ya shirya ya cimmata a kan gadon, lokacin har ta fara gyangyadi. Sai dai da yake ta san bukatar da ta kawoshi kuma ita din ma tayi kewarsa haka ta biye masa suna raba dare suna biyan bashi.
_
Tun kafin Abban ya sanar da Aisha zata koma gidan Zahra ya sanar da Jummai. Ya bata umarni a fitar da duk wasu kayan da suke dakin Saddiku ya kwashe ya kai gareji a gyara dakin don nan Aisha zata zauna kafin a gyara mata daki a sama. Nan da nan ba tare da bata lokaci da ta shiga aiki.
Tunda Rukayya taji wannan labarin ta kasa boye murnar ta, do da kanta ta dinga taya Jummai fitar da kayan dakin nan har aka gama. Yusra tana kallonsu tana kwafa musamman ya da taga Rukayyan tana ta rawar jiki.
Ranar litinin wadda tayi dai-dai da kwana shida da mutuwa ranar Abba ya umarci yara da suyi hakuri su koma makaranta. Musamman Aisha ta tashi da safe ta dafa musu abincin makaranta sannan tayiwa Abban waya ya turo Rukayya ta daukar musu. Haka ta zuzzuba musu kowa ya dauki nasa in banda Nana wadda tace ita indomie zata dafa.
Tun wuri Yusra ta dawo daga tata makarantar don haka ko da sauran yaran suka dawo wajen karfe biyu da rabi a gidan suka sameta. Bayan sun ci abinci Jummai ta taimakawa Nana, Ummi da Sumayya suka shirya suka wuce islamiyya. Basu dade da fita ba Rukayya ta shiga dakinsu na kasa inda ta sami Yusra a kashingide a kan gadonsu tana chatting a waya. Kai tsaye ta nufi wajen da ta ajiye jakar makarantar ta ta bude ta fara zaro littafanta. Yusra ta dubeta tace
'Ke bazaki islamiyyar bane?’
Ba tare da ta dubeta ba tace
'Eh, sai next week idan mun gama CA test a makarantar, yanzu ma karatu zan je nayi a gidan Anti sai dare zan dawo.’
Yusran ta tashi zaune a kan gadon a dai-dai lokacin da Rukayyan ta mayar da jakar ta rufe ta mike da litattafai a hannunta tana shirin ficewa daga dakin.
Yusran tace
'Kuma karatun ne ba zaki iya yi a nan ba duk fadin gidan nan dole sai kin je gidan da aka hanaki zuwa.’
Cikin halin ko in kula tace
'Eh, a can zan yi karatun sai dare zan dawo.’
'Lallai! Wato ke tun kafin ma Mommy ta kwana bakwai da barin duniya har kin fara karya dokokin da ta kafa miki ko, kamar daman jira kikeyi ta mutu ki koma inda ta hanaki zuwa.’
Cak ta tsaya a inda take ta juyo ta kalli Yusran yayinda idanuwanta suka cicciko da kwalla; kalaman yayar tata sun yi matukar yi mata ciwo a zuciya sai dai bata da wata amsa da zata iya bata. Ta ja hijabin jikinta ta goge kwallar da ta fado fuskarta ta juya ba tare da ta ce komai ba ta fice daga dakin. Tana fita ta tsaya a bayan kofar ta rasa me zata yi; tafiya zata yi kamar yanda tayi niyya ko kuwa ta hakura ta zauna a nan tayi karatun? Sai dai ta san idan ta zauna a gidan to da zarar Sumayya ta dawo daga islamiyya karatun ya kare. Domin a wajenta take zama kuma ko me take bukata haka Yusra zata ce taje Rukayya tayi mata.
Ta share hawayenta ta wuce tsakar gida inda ta jiyo motsin Goggo Binta da Jummai, ta sanar da su ta tafi gidan Anti Aisha sannan ta wuce cike da damuwa.
………
Yanda Aishan ta ganta cikin damuwa ya sa ta zata damuwar rasuwar ce don haka ta saka ta a gaba ta dinga bata baki tana yi mata nasiha har ta samu ta sami natsuwa. Ta sakata a gaba ta fara karatun wanda kusan tare suka yi shi.
Sai da akayi kiran Magriba tayi sallah taci abinci sannan ta koma gidan. Bata kula Yusra ba har dare yayi suka kwanta.
……….
Ranar Talata da safe kamar yanda Abba ya saba bayan ya shirya zai fita aiki ya tsaya a falo wajen Goggo Binta domin ya gaisheta. Bayan sun gaisa ta sanar da shi cewa gobe zata tafi, ba zata sami damar kara kwana ba. Sai dai tayi masa alkawarin idan an kwana biyu zata dawo. Nan ya nuna mata babu damuwa goben idan ta shirya Malam Ali zai kaita har can Sumaila shi da Saddiku, ya tabbatar mata da cewa kafin ma ta tafi Aishan zata dawo gidan.
Yayi mata sallama ya fice aiki.
Ya san Asiha ta riga tafi aiki don haka sai bayan da ya zauna a office sannan ya dauki waya ya kirawota, ya sanar da ita ya kamata da ta koma gida ta hada kayanta don daga yau zuwa gobe da safe yake so ta koma gidan Zahra saboda Goggo Binta zata tafi.
Bata iya ce masa komai ba sai dai tace masa idan ya dawo sayi maganar.
Sukayi sallama suka ajiye waya.
Haka ta karasa wunin ta a makaranta tana tunani rigimar da za ayi domin ita abu daya ta sani; ba zata zauna da Yusra da Nana ba domin Nana duk abinda Yusra ta sakata shi take yi.
__
Tun bayan rasuwar Zahra da Yaya Murja ta koma gida take tunanin makomar yaran. Ta yi tunanin Abba zai sa Aisha ta dawo gidan domin kula da su to amma hakan bai kwanta mata a rai ba. Bata san Aisha sosai ba sai ta hannun Zahra, a iya wannan sanin kuma bata taba jin wani alkhairi a kan Aishan ba. Hasali ma Zahran ta nuna musu cewa Aisha tana da sharri sannan kuma tana bin malamai sosai don ta mallake gidan. Don haka take jin bai kamata a bar ta da yaran ba sai dai idan hakan shi kadai ne zabinsu. Tana da labarai da yawa na irin haka yanda matar uba take mayar da yara kalar tausayi saboda rashin uwa kuma zata yi iya yinta ta tabbatar hakan bai faru da yaran Zahra ba; duk da ta san abu ne maii tsananin wahala.
Sun yi waya ta san gobe Goggo Binta zata tafi don haka yau ta tashi da niyyar zuwa gidan suyi sallama. Gidan Suwaiba ta fara zuwa don su tafi tare.
A dakin Suwaiban suka zauna ita Suwaiban tana canza kaya suna hira. Cikin damuwa Yaya Murja tacewa Suwaiban
‘Jiya da mukayi waya da Yusra tace Abbansu yace Aisha zata koma gidan amma dakin kasa ya sa a gyara mata.’
Suwaiba tace
'To Yaya ai idan ma dakin Ya Zahran yace ta shiga ba wani abu bane, na san ma hakan za ayi. Watakila dai yana jira ne ya sami lokaci a kwashe kayan a raba tun da ko ana so ko ba a so kayan da suke nata ne sun zama na magada.’