Sashe 68
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar Alhamis ce don haka yara babu islamiyya da yamma, tun safe ta gayawa Saddiku kada ya fitar mata da mota don zata fita da yamma amma ga mamakinta sai da ya fita; koda yake yanzu ta kula ko sauraron maganarta baya yi, yanda yayi niyya haka yake aikatawa. Malam Ali yana kawo yara daga makaranta tace ya tsaya zai kaita unguwa don haka nan ya zauna ya jirata.
Saida ta gama abinda takeyi tayi sallar la’asar sannan ta fito suka kama hanyar gidan Amina.
Duk da gidan Amina bai kai girman na Zahra ba amma shima ya tsaru, domin maigidanta ma ya fi Abba Saddiku dukiya. Cikin walwala ta sauketa ta ajiye mata lemo da cake sannan suka gaisa.
Bayan sun gaisa Aminan ta dubi Zahra wadda damuwa ta bayyana a fuskarta tace
‘Ya na ganki duk kinyi yaushi ne kawata, meye labari?’
Ta tabe baki ta kawar da kai
‘Mtseww, wallahi kin san na ce miki Aisha ta tafi gidansu ko?’
‘Eh kwarai kuwa.'
‘To wallahi yarinyar nan ta tattaro kayanta ta dawo.’
Ta rike haba tana mamaki
‘Ikon Allah, to amma dai Abban bai ce komai ba ko?’
‘Bai ma san da ita ba komai normal, kawai dai bana son zamanta a gidan ne. Nifa na fi so ace babu igiyar aurenta a wuyansa shine kawai zan huta.’
Ta dafa cinyarta
‘Ki daina damuwa, ki bawa banza ajiyarta kawai tunda dai maigidan yana hannunki. Kuma na gaya miki aikin bokan nan ba zata iya karyashi ba ko waye malaminta a garin nan.’
‘Hmm! Kin san kuma da maganar Yayansa da nace miki yana mun shisshigi, duk da dai na sa Yaron Malam yayi min aiki amma dai naga alama aikinsa bai yi ba. Ni wallahi Doguwan ma nake son zuwa don dai kawai cikin da yake jikina ne ya sa bana son zuwa.’
Ta dan zaro ido
‘Ciki uwar Saddiku? Lallai matar nan himmarki tana da yawa.’
‘To na sani ko shine namijin da nake ta nema, ai kin ga dole na tattala.’
Ta mika mata hannu suka tafa
‘Da kyau kawata. Nima wallahi ina son zuwa Doguwa saboda mijin Asiya, ya fara kawo mata wargi gara na nema mata taimako. To amma gaskiya sai an dan kara kwana biyu, in kina so idan na shirya sai muje ko kuma na tafi da sakonki mu gani ko zai karba. Sai dai shi kinsan fa baya aiki da sako sai dai kai da kake da bukata kaje da kanka, kuma gaskiya ba zan baki shawarar zuwa wajen nan da ciki ba.’
Ta dan yi tsaki
‘Wallahi nima abinda nake ji kenan, to amma bari mu gani a kwana biyu tunda ma yanzu babu wata major matsala.’
‘Gaskiya dai. Idan kuma wani abun ya taso ai sai kiyi maleji da Yaron Malam tunda shi ko ta waya zaku gama komai.’
Suka karasa hirarrakinsu sai gefin magriba sukayi sallama Zahra ta shiga mota Malam Ali wanda yake jiranta ya mayar da ita gida.
Haka ta hakura ta cigaba da rainon cikinta tana fatan ya zama namiji; tunda ko babu komai yanda bokan nan yayi mata alkawarin babu wanda yake maganar Aisha. Domin har dangin Abba ma babu wanda yake maganarta kamar ma babu ita, kuma tana da yakinin kwanan nan kudin hayar gidan zai kare ta san dole Aisha ta tashi tunda babu mai biya mata.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
35
Duk yanda Aisha ta kai ga son boye damuwarta game da rashin ganin mijinta abun yana mata wahala; lokuta da dama ta kan kwana tana kuka. Wasu lokutan kuma idan ta yi sujuda da nufin ta roki Allah sai kuka yaci karfinta, haka zatayi mai isarta sannan ta dago daga sujudar. Tana zuwa aiki da islamiyya ga kuma cinikin mayafanta amma duk wannan bai isa ya debe mata kewar mijinta ba.
Yau din ma haka ta tashi cikin yanayi na damuwa, gashi ranar hutu ce don haka babu aiki kuma gashi da wuri Amira ta fita saboda ana bikin babbar kawarta; don haka ita kadai ce a gidan.
Duk yanda ta so ta kawar da damuwar daga ranta abun ya faskara, haka tayi ta faman aikace-aikace, har aikin ma da batayi niyyar yi ba. Sai wajen karfe biyu ta gama goge gidan, ta dauko tsumman ta fito ta wanke a faffon tsakar gida ta shanya. Har ta kama hanyar shiga gidan sai kuma ta zauna a kan dankalin da fulawoyi suke ciki; ta karewa tsakar gidan kallo kamar mai neman wani abu.
Haka kawai kuma sai ta ji kamar ita kadai ce a duniyar; ya za ayi ace tana zaune a gidan mijinta amman saboda Zahra babu mai kulata? Makota gaba daya basa harka da ita gashi mijin ma yanzu ya daina kulata. Ta manta rabon da a buga mata gate don daga ita sai Amira suke rayuwarsa, sai dai da yake duk sati sai Anti Uwani ta kawo su Abdallah. Ta share zazzafar kwallar da ta zubo a kan fuskarta.
Tabbas ba zata taba yafewa Zahra ba da ma duk wani wanda yake da hannu wajen sakata a wannan halin.
A da ta yiwa kanta alkawarin zata zauna tayi jiran har mijinta ya dawo hayyacinsa amma kawo yanzu bata sani ba ko zata iya cika wannan alkawarin. Domin zaman ya fara isarta, ta fara rasa walwala gaba daya tunda komai ya daina bata farin ciki. Tabbas bata san zuwa yaushe zata iya jira ba amma dai ta fara tunanin yiwuwar ta koma gidan Hajiya kawai ko jiran ne tayi a can.
Ta share hawayenta lokacin da ta tuna la’asar ta kusa kuma bata ma yi azahar ba, ta mike cikin sanyin jiki ta shige cikin gidan domin yin sallar azahar.
___
Da yake tazarar dake tsakanin karamar Sallah da babbar Sallah babu yawa har har an fara lissafin babbar Sallah.
Kamar yanda ya saba haka yayi wa kowa kayan Sallah; baiyi maganar Aisha ba wanda wannan ya kara kwantarwa da Zahra hankali ta kara sakankancewa lallai aikin boka na Doguwa ya kama.
Sa ya siyo da rago daya wanda aka yanka Uwara Saddiku tayi yanda take so da shi cikin walwala. Cikinta ya fara girma domin ya shiga wata na hudu don haka ba da ita akayi aikin suya naman ba, masu aiki ne su uku sukayi. Sai dai kawai tana zaune daga gefe a kan tabarma tana nuna yanda take so ayi.
Haka suka gama aikin suka tattare mata naman aka saka a cikin gida.
Ita kuwa Aisha tun ana i gobe Sallah suka tafi gidan Hajiya, a can aka yanka mata ragonta aka gyara aka soya. Saida suka gama yawon Sallah lokacin bayan Sallah da kwana biyar sannan suka koma.
Haka rayuwa ta cigaba.
__
Ranar Talata ce tana zaune a staffroom, bata da aiki a daidai lokacin don haka take ta faman duba wayarta tana kallon status; daga kan wannan ta koma kan wannan. Suna ta wucewa har tazo kan status din Anti Karima, matar Yaya Bello.
Hotuna ne na yaronta na uku wato Yusuf wanda suke kira Adil, daga kallon hotunan zaka gane bikin sauka ake yiwa Adil din wanda tabbas ta tuna kamar wancan satin ta ga hoton katin gayyatar bikin saukar a status din Yaya Saratu. Daga rubutun da Anti Karima tayi a status din ne kuma ta gane saukar hadda yayi; tayi murmushi tana kallon hoton zayyanar dake hannunsa.
Idan taga yaro ya haddace alkur’ani tabbas yana bata sha’awa kuma tana alfahari da su domin Abdallah da farha ma tana fatan su haddace izu sittin.
Ana cikin bikin Sallah ta gani a status din Anti Karima an kawo kayan auren Asma’u yayar Adil din, ta manta dalilin da ya hanata koda waya ne ta yiwa Anti Karima tayi mata barka. Lallai yanzu ya kamata taje gidan nan don ba zata ma iya tuna rabonta da su ba, ko babu komai dai ya kamata taje mata murnar auren Asma’u da ake shirin yi kuma da saukar Adil din.
Nan take ta yanke shawarar ranar asabar idan ta tashi daga islamiyya zata je gidan tunda dama karfe sha daya suke tashi kuma ranar Amira tana da lecture har karfe daya; don haka daga islamiyya sai ta wuce gidan Yaya Bello daga can ta tsaya ta gaida Hajiya sai ta wuce ta dauko Amira.
Ta dan gatsina fuska a lokacin da tayi tunanin zuwa gidan Hajiya; bata son zuwa gidan Hajiya saboda yanda Hajiyan takeyi mata wanda ya sa Anisa ma da take gidan bata ganin girmanta don ko gaisheta bata yi. Ta tuno zuwanta na karshe gidan wanda bayan ta gaisa da Hajiyan haka Hajiyan ta tashi ta shige daki ta barta, itama Anisa da mai aikin Hajiya suka shige kicin suka barta ita kadai a falon Hajiya. Saida ta gaji da zama sannan ta taso ta fito kuma babu yanda bata yi ba Anisan ta kirawo mata Hajiyan tayi mata sallama taki; sai ce mata kawai tayi tayi bacci kuma idan tana bacci ba a tashinta. Haka ta hakura ta tafi tana mamakin dalilin da yasa suke mata wannan kiyayyar. Kusan zata iya cewa kaf ‘yan gidan su Abba Yaya Bello ne kawai da iyalansa suke zama da ita yanda ya kamata.
Ta kawar da tunanin ta cigaba da latsa wayar tana hakurkurtar da zuciyarta a kan haka zata hakura taje gidan Hajiyan, in ya so ta dauki dan rakiya daga gidan Yaya Bello watakila abun yayi mata sauki.
……….
Tun ranar Juma’a ta tanadin alkur’ani izu sittin da turaren mai kamshi da agogon hannu wanda ta saka a leda a kan zata kaiwa Adil. Da tayi tunanin zata dafawa Hajiya funkason alkama da farfaesun kifi to amma gaskiya bata son ta sha wahala taje su lalatar da abincin basu ci ba don haka ta yanke shawara gara ta sayawa Hajiyan tuffa da kayan shayi irin wanda ya dace da masu ciwon suga ta kai mata.
Ranar asabar suna tashi daga islamiyya ta wuce gidan Yaya Bello.
Tana tsayar da motarta a bakin gate din gidan yaran gidan suna dawowa daga tahafiz; tun daga nan yaran suka fara gaisheta, bayan ta amsa suka nufi cikin gidan a tare. Suna tafe tana yiwa Adil murnar haddar da yayi.
Saida ta gama abinda takeyi tayi sallar la’asar sannan ta fito suka kama hanyar gidan Amina.
Duk da gidan Amina bai kai girman na Zahra ba amma shima ya tsaru, domin maigidanta ma ya fi Abba Saddiku dukiya. Cikin walwala ta sauketa ta ajiye mata lemo da cake sannan suka gaisa.
Bayan sun gaisa Aminan ta dubi Zahra wadda damuwa ta bayyana a fuskarta tace
‘Ya na ganki duk kinyi yaushi ne kawata, meye labari?’
Ta tabe baki ta kawar da kai
‘Mtseww, wallahi kin san na ce miki Aisha ta tafi gidansu ko?’
‘Eh kwarai kuwa.'
‘To wallahi yarinyar nan ta tattaro kayanta ta dawo.’
Ta rike haba tana mamaki
‘Ikon Allah, to amma dai Abban bai ce komai ba ko?’
‘Bai ma san da ita ba komai normal, kawai dai bana son zamanta a gidan ne. Nifa na fi so ace babu igiyar aurenta a wuyansa shine kawai zan huta.’
Ta dafa cinyarta
‘Ki daina damuwa, ki bawa banza ajiyarta kawai tunda dai maigidan yana hannunki. Kuma na gaya miki aikin bokan nan ba zata iya karyashi ba ko waye malaminta a garin nan.’
‘Hmm! Kin san kuma da maganar Yayansa da nace miki yana mun shisshigi, duk da dai na sa Yaron Malam yayi min aiki amma dai naga alama aikinsa bai yi ba. Ni wallahi Doguwan ma nake son zuwa don dai kawai cikin da yake jikina ne ya sa bana son zuwa.’
Ta dan zaro ido
‘Ciki uwar Saddiku? Lallai matar nan himmarki tana da yawa.’
‘To na sani ko shine namijin da nake ta nema, ai kin ga dole na tattala.’
Ta mika mata hannu suka tafa
‘Da kyau kawata. Nima wallahi ina son zuwa Doguwa saboda mijin Asiya, ya fara kawo mata wargi gara na nema mata taimako. To amma gaskiya sai an dan kara kwana biyu, in kina so idan na shirya sai muje ko kuma na tafi da sakonki mu gani ko zai karba. Sai dai shi kinsan fa baya aiki da sako sai dai kai da kake da bukata kaje da kanka, kuma gaskiya ba zan baki shawarar zuwa wajen nan da ciki ba.’
Ta dan yi tsaki
‘Wallahi nima abinda nake ji kenan, to amma bari mu gani a kwana biyu tunda ma yanzu babu wata major matsala.’
‘Gaskiya dai. Idan kuma wani abun ya taso ai sai kiyi maleji da Yaron Malam tunda shi ko ta waya zaku gama komai.’
Suka karasa hirarrakinsu sai gefin magriba sukayi sallama Zahra ta shiga mota Malam Ali wanda yake jiranta ya mayar da ita gida.
Haka ta hakura ta cigaba da rainon cikinta tana fatan ya zama namiji; tunda ko babu komai yanda bokan nan yayi mata alkawarin babu wanda yake maganar Aisha. Domin har dangin Abba ma babu wanda yake maganarta kamar ma babu ita, kuma tana da yakinin kwanan nan kudin hayar gidan zai kare ta san dole Aisha ta tashi tunda babu mai biya mata.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
35
Duk yanda Aisha ta kai ga son boye damuwarta game da rashin ganin mijinta abun yana mata wahala; lokuta da dama ta kan kwana tana kuka. Wasu lokutan kuma idan ta yi sujuda da nufin ta roki Allah sai kuka yaci karfinta, haka zatayi mai isarta sannan ta dago daga sujudar. Tana zuwa aiki da islamiyya ga kuma cinikin mayafanta amma duk wannan bai isa ya debe mata kewar mijinta ba.
Yau din ma haka ta tashi cikin yanayi na damuwa, gashi ranar hutu ce don haka babu aiki kuma gashi da wuri Amira ta fita saboda ana bikin babbar kawarta; don haka ita kadai ce a gidan.
Duk yanda ta so ta kawar da damuwar daga ranta abun ya faskara, haka tayi ta faman aikace-aikace, har aikin ma da batayi niyyar yi ba. Sai wajen karfe biyu ta gama goge gidan, ta dauko tsumman ta fito ta wanke a faffon tsakar gida ta shanya. Har ta kama hanyar shiga gidan sai kuma ta zauna a kan dankalin da fulawoyi suke ciki; ta karewa tsakar gidan kallo kamar mai neman wani abu.
Haka kawai kuma sai ta ji kamar ita kadai ce a duniyar; ya za ayi ace tana zaune a gidan mijinta amman saboda Zahra babu mai kulata? Makota gaba daya basa harka da ita gashi mijin ma yanzu ya daina kulata. Ta manta rabon da a buga mata gate don daga ita sai Amira suke rayuwarsa, sai dai da yake duk sati sai Anti Uwani ta kawo su Abdallah. Ta share zazzafar kwallar da ta zubo a kan fuskarta.
Tabbas ba zata taba yafewa Zahra ba da ma duk wani wanda yake da hannu wajen sakata a wannan halin.
A da ta yiwa kanta alkawarin zata zauna tayi jiran har mijinta ya dawo hayyacinsa amma kawo yanzu bata sani ba ko zata iya cika wannan alkawarin. Domin zaman ya fara isarta, ta fara rasa walwala gaba daya tunda komai ya daina bata farin ciki. Tabbas bata san zuwa yaushe zata iya jira ba amma dai ta fara tunanin yiwuwar ta koma gidan Hajiya kawai ko jiran ne tayi a can.
Ta share hawayenta lokacin da ta tuna la’asar ta kusa kuma bata ma yi azahar ba, ta mike cikin sanyin jiki ta shige cikin gidan domin yin sallar azahar.
___
Da yake tazarar dake tsakanin karamar Sallah da babbar Sallah babu yawa har har an fara lissafin babbar Sallah.
Kamar yanda ya saba haka yayi wa kowa kayan Sallah; baiyi maganar Aisha ba wanda wannan ya kara kwantarwa da Zahra hankali ta kara sakankancewa lallai aikin boka na Doguwa ya kama.
Sa ya siyo da rago daya wanda aka yanka Uwara Saddiku tayi yanda take so da shi cikin walwala. Cikinta ya fara girma domin ya shiga wata na hudu don haka ba da ita akayi aikin suya naman ba, masu aiki ne su uku sukayi. Sai dai kawai tana zaune daga gefe a kan tabarma tana nuna yanda take so ayi.
Haka suka gama aikin suka tattare mata naman aka saka a cikin gida.
Ita kuwa Aisha tun ana i gobe Sallah suka tafi gidan Hajiya, a can aka yanka mata ragonta aka gyara aka soya. Saida suka gama yawon Sallah lokacin bayan Sallah da kwana biyar sannan suka koma.
Haka rayuwa ta cigaba.
__
Ranar Talata ce tana zaune a staffroom, bata da aiki a daidai lokacin don haka take ta faman duba wayarta tana kallon status; daga kan wannan ta koma kan wannan. Suna ta wucewa har tazo kan status din Anti Karima, matar Yaya Bello.
Hotuna ne na yaronta na uku wato Yusuf wanda suke kira Adil, daga kallon hotunan zaka gane bikin sauka ake yiwa Adil din wanda tabbas ta tuna kamar wancan satin ta ga hoton katin gayyatar bikin saukar a status din Yaya Saratu. Daga rubutun da Anti Karima tayi a status din ne kuma ta gane saukar hadda yayi; tayi murmushi tana kallon hoton zayyanar dake hannunsa.
Idan taga yaro ya haddace alkur’ani tabbas yana bata sha’awa kuma tana alfahari da su domin Abdallah da farha ma tana fatan su haddace izu sittin.
Ana cikin bikin Sallah ta gani a status din Anti Karima an kawo kayan auren Asma’u yayar Adil din, ta manta dalilin da ya hanata koda waya ne ta yiwa Anti Karima tayi mata barka. Lallai yanzu ya kamata taje gidan nan don ba zata ma iya tuna rabonta da su ba, ko babu komai dai ya kamata taje mata murnar auren Asma’u da ake shirin yi kuma da saukar Adil din.
Nan take ta yanke shawarar ranar asabar idan ta tashi daga islamiyya zata je gidan tunda dama karfe sha daya suke tashi kuma ranar Amira tana da lecture har karfe daya; don haka daga islamiyya sai ta wuce gidan Yaya Bello daga can ta tsaya ta gaida Hajiya sai ta wuce ta dauko Amira.
Ta dan gatsina fuska a lokacin da tayi tunanin zuwa gidan Hajiya; bata son zuwa gidan Hajiya saboda yanda Hajiyan takeyi mata wanda ya sa Anisa ma da take gidan bata ganin girmanta don ko gaisheta bata yi. Ta tuno zuwanta na karshe gidan wanda bayan ta gaisa da Hajiyan haka Hajiyan ta tashi ta shige daki ta barta, itama Anisa da mai aikin Hajiya suka shige kicin suka barta ita kadai a falon Hajiya. Saida ta gaji da zama sannan ta taso ta fito kuma babu yanda bata yi ba Anisan ta kirawo mata Hajiyan tayi mata sallama taki; sai ce mata kawai tayi tayi bacci kuma idan tana bacci ba a tashinta. Haka ta hakura ta tafi tana mamakin dalilin da yasa suke mata wannan kiyayyar. Kusan zata iya cewa kaf ‘yan gidan su Abba Yaya Bello ne kawai da iyalansa suke zama da ita yanda ya kamata.
Ta kawar da tunanin ta cigaba da latsa wayar tana hakurkurtar da zuciyarta a kan haka zata hakura taje gidan Hajiyan, in ya so ta dauki dan rakiya daga gidan Yaya Bello watakila abun yayi mata sauki.
……….
Tun ranar Juma’a ta tanadin alkur’ani izu sittin da turaren mai kamshi da agogon hannu wanda ta saka a leda a kan zata kaiwa Adil. Da tayi tunanin zata dafawa Hajiya funkason alkama da farfaesun kifi to amma gaskiya bata son ta sha wahala taje su lalatar da abincin basu ci ba don haka ta yanke shawara gara ta sayawa Hajiyan tuffa da kayan shayi irin wanda ya dace da masu ciwon suga ta kai mata.
Ranar asabar suna tashi daga islamiyya ta wuce gidan Yaya Bello.
Tana tsayar da motarta a bakin gate din gidan yaran gidan suna dawowa daga tahafiz; tun daga nan yaran suka fara gaisheta, bayan ta amsa suka nufi cikin gidan a tare. Suna tafe tana yiwa Adil murnar haddar da yayi.