Sashe 69
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin girmamawa Anti Karima ta karbeta, Muhammad da Asma’u wadanda basu je tahfiz ba suka gaisheta sannan Asma’u ta kawo ruwa da lemo. Suka zauna ita da Anti Karima a falo sunata hirar yaushe gamo, daga baya kuma aka janyo akwatunan kayan auren Asma’u aka bude mata ta gani tana ta sa albarka.
Anti Karima ta dubeta tana daga mata kayan tace
‘Kinga yanzu saura wata uku da kwana goma bikin.’
Da murmushinta tace
‘Allah ya nuna mana, kice abun ma ya matso.’
Jimawa kadan Aishan ta dubi Anti Karima tace
‘Anti to me ake shiri? Akwai wani anko da za ayi don gara na karbi nawa kafin na tafi.’
Ta kama haba ta bude baki
‘Tab, ai Abbansu baya son anko babu ma wanda ya isa yayi wannan zance. Kina ji event center ma yace ba za aje ba wai a nan gidan zamuyi gaba dayan bikin. Har yanzu faman lallabarsa nake yana burtsewa; tunda kinga gidan ai ina muka ga filin yin biki idan banda rigimarsa.’
‘Gaskiya dai Baban su Muhammad da ya bari munje event center din. Amma fa kin san duk abun suna ne ko a nan din aka yi kalau za a gama shike nan, ai albarkar abun ake nema.’
‘Hakane.’
Suka cigaba da hirarrakinsu.
Sai wajen sha biyu da kwata sannan Aisha ta mike zata tafi. Ta nemi wanda zai rakata gidan Hajiya aka ce Asma’u ta shirya suje, don haka ta dan zauna tana jiran Asma’u ta kintsa.
--------
Kamar yanda ya saba duk ranar da babu aiki da safe yake tafiya gidan Hajiya, idan rana tayi sai ya wuce gidan Yaya Bello inda a can zai ci abincin rana. Ba zai koma gidansa ba har sai anyi sallar Magriba. Duk yanda Zahra taso ya daina zuwa gidan Yaya Bello ko kuma a kalla idan ya je ya daina dadewa abun yaci tura. Tunda yace mata a can yake cin abincin rana ta fara zargin wani abun suke barbada masa a abincin shi yasa ya kasa rabuwa da su.
Sau biyu tana turawa Yaron Malam kudi yayi mata aikin da zai raba Abban da Yaya Bello amma ko sauyi bata gani ba. Daga karshe Yaron Malam din ya sanar da ita aikin ba zai yiwu ba domin mutumin da ta bayar da bayaninsa idan sun tashi zasuyi aiki ko ganinsa basa iya yi.
Sosai abun ya bata mata rai amma babu yanda zatayi tunda tana tsoron zuwa Doguwa da cikin jikinta; musamman da yake sau biyu tana yin scanning a gurare daban-daban kuma duka biyun sun tabbatar mata namiji take dauke da shi; bata son wani abu ya sameshi.
Haka ta hakura ta daga musu kafa, amma tayi alkawarin idan ta haihu da zarar tayi arba’in zata je Doguwa duk sai tayi maganinsu ko waye malamin Yaya Bello bai isa ya mallake mata miji ba.
Yau din ma bayan ya gama cin abincin safe tana kallonsa ya shiryo ya fito, tun safe take masa korafin bata jin dadi da nufin ya fasa fitar amma bai ma kulata ba. Kawai sai ya sanar da ita idan da matsala tayi masa waya sai ya dawo. Da kyar ta bude baki tayi masa a dawo lafiya shi kuwa ya amsa ya fice ya kama hanya lokacin wajen karfe goma.
Kai tsaye gidan Hajiya ya wuce don ya san a yanzu Yaya Bello yana can, domin tunda diabetes dinta ya tashi da azumi da kanshi yake zuwa yana bata abincin safe da na dare. Sosai suke lallabata saboda bayan diabetes din kuma to tana yi musu rikici irin na tsufa domin ko abincin ma idan ta ga dama sai tace sai taci abinda likita ya hanata ci. Haka dai suke ta fama.
Lokacin da Abban ya shiga gidan Hajiya ta gama cin abincinta, suna zaune dai a falo suna hira ita da Yaya Bello. Nan ya zauna suka cigaba da hirarrakinsu gaba daya.
Can zuwa shabiyu lokacin har Hajiya ta fara gyangyadi a falon, sukayi mata sallama domin ta samu tayi baccinta. Suna fita suka nufi gidan Yaya Bello a motar Abba tunda shi Yaya Bello bai zo da mota ba.
__
Lokacin da Yaya Bello da Abban Saddiku suke shiga gidan Yaya Bellon yayi daidai da lokacin da Aisha suke fitowa tare da Asma’u yayinda Anti Zalihan take biye dasu tana yiwa Aisha sallama da godiya.
Kana shiga gate din gidan dan karamin farfajiya ne inda daga nan zaka shiga wata kofar mai irin siririn soron nan sannan ka fada tsakar gidan. Kasancewar kofar falon baki wanda take a farfajiyar farko a rufe take sai Yaya Bello ya wuce gaba suka nufi cikin gidan ta wannan soron.
Suna daf da kaiwa karshen soron Aisha ta sako kai Asma’u na biye da ita. Ganin Yaya Bello ta tsaya ta fara kokarin kaucewa ta bashi hanya ya shige, tana shirin rage tsawo ta gaisheshi ta hango Abban Sadik a bayansa.
Take ta manta da gaisuwar da take niyyar yi ta bi shi da kallo baki a bude. Ta kusan shekara biyu rabon da ta ganshi kamar haka, ya dan yi kiba amma kuma ya kara tsufa. Yanda take binsa da kallo shima haka yake binta da kallon.
Yaya Bello ne ya katse musu kallon yace
‘A’a! Aisha. Sannu da zuwa.’
Ta kauda kanta ta rage tsawo ta gaishe da Yaya Bello. Bayan ya amsa ya juya bayansa ya dubi Abba yace
‘To kai kaga amarya ta biyoka fa.’
Kamar bai ji abinda yace ba ya bude baki a hankali har yanzu idonsa a kan Aishan cike da tsananin mamaki yace
‘Aisha! Daman nan kika dawo?’
Ta kawar da kai ta dan share kwallar da ta fito daga idonta, a dai-dai lokacin Asma’u ta koma cikin tsakar gidan ta zauna a kan kujera domin jiransu.
Cike da mamaki Yaya Bello ya fara binsu da kallo daya bayan daya yana kokarin ya fahimci abinda yake faruwa. Ya gyara tsayuwa yace
‘A’a! Me yake faruwa ne? Me yake faruwa ne? Ya zaka ce nan ta dawo bayan da na fita ma bata zo ba.’
Kafin ya bashi amsa ya kama hannunsa ya dubi Aishan yana nuna mata cikin gidan yana fadin
‘Mu koma naji abinda yake faruwa, kunata kallon juna kamar wasu baki.’
Ta bude baki zata yi magana yayinda Yaya Bello ya janyo Abban suka nufi cikin, bata da wani zabi don haka ta wuce gaba suka bita a baya domin idan ta tsaya wajen ma ba zai isa su wuce ba.
A falon suka ci karo da Anti Zalihan ta mike tsaye tana fadin
‘A’a, kin tsintosu Aisha.’
Babu wanda ya amsa mata don haka ta matsa Abban Sadik da Yaya Bello suka zauna a kujerar zaman mutum uku yayinda ita da Aishan suka zauna a kujerun zaman mutum daya. Yaya Bello ya dubi Aishan yace
‘Aisha me yake faruwa ne, kamar mamakin ganin juna kukeyi ke har kina share kwalla. Me yake faruwa ne?’
Bata sami bakin bayar da amsa ba saboda hawayen da take ta faman tokarewa ne ya kwace ya wanke mata fuska gaba daya, ta sa hannu ta fara share hawayen.
Cikin tsananin damuwa da mamaki Yaya Bello ya gyara zama yana dubansu daga wannan ya dubi wannan. Yace
‘Yusufa wai me yake faruwa ne? Kayi min bayani.’
Ya sa hannu ya goge fuskarsa yana muttsike ido kamar wanda ya tashi daga bacci, a hankali ya bude baki yace
‘Yaya babu komai fa, na dai dade ban ga Aishan bane kawai.’
Ya dubi Aishan wadda ta sunkuyar da kai tana share hawaye yace
‘Ikon Allah! To yaji tayi ko rabuwa kuka yi amma baku sanar ba.’
Gaba daya su suka yi shiru kowa yana ta faman zare ido, itama Anti Zulaiha sai kallonsu take tana mamaki don bata ma fahimci kan zancen ba. Yaya Bello ya katse shirun ya dubi Aishan yace
‘Aisha me yake faruwa ne? Ya sake ki ne ko me ya faru?’
Ta share hawaye tace
‘A’a bai sake ni ba, ya dai kusa shekara biyu bai zo gidan da nake ba shi yasa muka dade bamu hadu ba.’
Yaya Bello ya sake shiga rudani, ya kalli Aishan ya kalli Yusuf din. Aisha ta sake share hawaye, ta bashi labarin yanda abubuwan suka faru. Binta kawai yake da kallo yana mamaki. Ya dubi Abban Sadik din yace
‘Yusufa kai kuma kana auren mace kawai sai baka ganta ba kuma ba zaka nemeta ba?’
Ya share gumi yace
‘Wallahi Yaya ni kaina har yanzu ina mamaki, don ni sai yanzu ma fa da na ganta na tuna da ita. Na kasa gane me yake faruwa ma gaba daya wallahi.’
‘Ikon Allah! To ni kaina ma ban fahimceku ba. Amma Yusufa ya za ayi ace kai da matarka kuma ga gidan da take kusa da daya gidan amma kace wai ka kusa shekara baku hadu ba. Wannan din wacce irin rayuwa ce?’
‘Wallahi Yaya nima sai yanzun nake mamaki, kamar ma gaba daya mantawa nayi da wani bangaren na rayuwata. Gaba daya ma na kasa ganewa.’
Sukayi shiru kowa da abinda yake ransa. Jimawa kadan Anti Karima tayi gyaran murya tace
‘Gaskiya Abban Muhammad ni ina ga ka kirawo Malam Sama’ila tunda yau asabar watakila yana gida, domin wannan abun yayi kama da aljannu ko shaidanu. Gara ka gane kan komai a dauki mataki kafin su bar nan su sake komawa ruwa.’
Yace
‘Hakane gaskiya, bari nayi masa waya na san yanzu zai shigo in sha Allah.’
Ya dauko waya ya kirawoshi, yace masa yana bakin titi zai fita amma yanzu zai dawo.
Sukayi shiru suna jiransa.
Jimawa kadan Yaya Bello ya kasa hakuri ya kirawo Muhammad yace masa ya fita waje da zarar Malam Sama’ila ya zo su shigo tare. Yana fitowa suka hadu suka shigo ya nuna masa falon.
Bayan sun gaisa Abban Muhammad yayi masa bayanin abinda yake faruwa, ya rufe da
‘To Malam Sama’ila abun ne naga kamar na mutanen boye, to shine nace gara ka zo muji ko da akwai abinda za a taimaka da shi.’
Yayi shiru yana jijjiga kai, jimawa kadan yace
Anti Karima ta dubeta tana daga mata kayan tace
‘Kinga yanzu saura wata uku da kwana goma bikin.’
Da murmushinta tace
‘Allah ya nuna mana, kice abun ma ya matso.’
Jimawa kadan Aishan ta dubi Anti Karima tace
‘Anti to me ake shiri? Akwai wani anko da za ayi don gara na karbi nawa kafin na tafi.’
Ta kama haba ta bude baki
‘Tab, ai Abbansu baya son anko babu ma wanda ya isa yayi wannan zance. Kina ji event center ma yace ba za aje ba wai a nan gidan zamuyi gaba dayan bikin. Har yanzu faman lallabarsa nake yana burtsewa; tunda kinga gidan ai ina muka ga filin yin biki idan banda rigimarsa.’
‘Gaskiya dai Baban su Muhammad da ya bari munje event center din. Amma fa kin san duk abun suna ne ko a nan din aka yi kalau za a gama shike nan, ai albarkar abun ake nema.’
‘Hakane.’
Suka cigaba da hirarrakinsu.
Sai wajen sha biyu da kwata sannan Aisha ta mike zata tafi. Ta nemi wanda zai rakata gidan Hajiya aka ce Asma’u ta shirya suje, don haka ta dan zauna tana jiran Asma’u ta kintsa.
--------
Kamar yanda ya saba duk ranar da babu aiki da safe yake tafiya gidan Hajiya, idan rana tayi sai ya wuce gidan Yaya Bello inda a can zai ci abincin rana. Ba zai koma gidansa ba har sai anyi sallar Magriba. Duk yanda Zahra taso ya daina zuwa gidan Yaya Bello ko kuma a kalla idan ya je ya daina dadewa abun yaci tura. Tunda yace mata a can yake cin abincin rana ta fara zargin wani abun suke barbada masa a abincin shi yasa ya kasa rabuwa da su.
Sau biyu tana turawa Yaron Malam kudi yayi mata aikin da zai raba Abban da Yaya Bello amma ko sauyi bata gani ba. Daga karshe Yaron Malam din ya sanar da ita aikin ba zai yiwu ba domin mutumin da ta bayar da bayaninsa idan sun tashi zasuyi aiki ko ganinsa basa iya yi.
Sosai abun ya bata mata rai amma babu yanda zatayi tunda tana tsoron zuwa Doguwa da cikin jikinta; musamman da yake sau biyu tana yin scanning a gurare daban-daban kuma duka biyun sun tabbatar mata namiji take dauke da shi; bata son wani abu ya sameshi.
Haka ta hakura ta daga musu kafa, amma tayi alkawarin idan ta haihu da zarar tayi arba’in zata je Doguwa duk sai tayi maganinsu ko waye malamin Yaya Bello bai isa ya mallake mata miji ba.
Yau din ma bayan ya gama cin abincin safe tana kallonsa ya shiryo ya fito, tun safe take masa korafin bata jin dadi da nufin ya fasa fitar amma bai ma kulata ba. Kawai sai ya sanar da ita idan da matsala tayi masa waya sai ya dawo. Da kyar ta bude baki tayi masa a dawo lafiya shi kuwa ya amsa ya fice ya kama hanya lokacin wajen karfe goma.
Kai tsaye gidan Hajiya ya wuce don ya san a yanzu Yaya Bello yana can, domin tunda diabetes dinta ya tashi da azumi da kanshi yake zuwa yana bata abincin safe da na dare. Sosai suke lallabata saboda bayan diabetes din kuma to tana yi musu rikici irin na tsufa domin ko abincin ma idan ta ga dama sai tace sai taci abinda likita ya hanata ci. Haka dai suke ta fama.
Lokacin da Abban ya shiga gidan Hajiya ta gama cin abincinta, suna zaune dai a falo suna hira ita da Yaya Bello. Nan ya zauna suka cigaba da hirarrakinsu gaba daya.
Can zuwa shabiyu lokacin har Hajiya ta fara gyangyadi a falon, sukayi mata sallama domin ta samu tayi baccinta. Suna fita suka nufi gidan Yaya Bello a motar Abba tunda shi Yaya Bello bai zo da mota ba.
__
Lokacin da Yaya Bello da Abban Saddiku suke shiga gidan Yaya Bellon yayi daidai da lokacin da Aisha suke fitowa tare da Asma’u yayinda Anti Zalihan take biye dasu tana yiwa Aisha sallama da godiya.
Kana shiga gate din gidan dan karamin farfajiya ne inda daga nan zaka shiga wata kofar mai irin siririn soron nan sannan ka fada tsakar gidan. Kasancewar kofar falon baki wanda take a farfajiyar farko a rufe take sai Yaya Bello ya wuce gaba suka nufi cikin gidan ta wannan soron.
Suna daf da kaiwa karshen soron Aisha ta sako kai Asma’u na biye da ita. Ganin Yaya Bello ta tsaya ta fara kokarin kaucewa ta bashi hanya ya shige, tana shirin rage tsawo ta gaisheshi ta hango Abban Sadik a bayansa.
Take ta manta da gaisuwar da take niyyar yi ta bi shi da kallo baki a bude. Ta kusan shekara biyu rabon da ta ganshi kamar haka, ya dan yi kiba amma kuma ya kara tsufa. Yanda take binsa da kallo shima haka yake binta da kallon.
Yaya Bello ne ya katse musu kallon yace
‘A’a! Aisha. Sannu da zuwa.’
Ta kauda kanta ta rage tsawo ta gaishe da Yaya Bello. Bayan ya amsa ya juya bayansa ya dubi Abba yace
‘To kai kaga amarya ta biyoka fa.’
Kamar bai ji abinda yace ba ya bude baki a hankali har yanzu idonsa a kan Aishan cike da tsananin mamaki yace
‘Aisha! Daman nan kika dawo?’
Ta kawar da kai ta dan share kwallar da ta fito daga idonta, a dai-dai lokacin Asma’u ta koma cikin tsakar gidan ta zauna a kan kujera domin jiransu.
Cike da mamaki Yaya Bello ya fara binsu da kallo daya bayan daya yana kokarin ya fahimci abinda yake faruwa. Ya gyara tsayuwa yace
‘A’a! Me yake faruwa ne? Me yake faruwa ne? Ya zaka ce nan ta dawo bayan da na fita ma bata zo ba.’
Kafin ya bashi amsa ya kama hannunsa ya dubi Aishan yana nuna mata cikin gidan yana fadin
‘Mu koma naji abinda yake faruwa, kunata kallon juna kamar wasu baki.’
Ta bude baki zata yi magana yayinda Yaya Bello ya janyo Abban suka nufi cikin, bata da wani zabi don haka ta wuce gaba suka bita a baya domin idan ta tsaya wajen ma ba zai isa su wuce ba.
A falon suka ci karo da Anti Zalihan ta mike tsaye tana fadin
‘A’a, kin tsintosu Aisha.’
Babu wanda ya amsa mata don haka ta matsa Abban Sadik da Yaya Bello suka zauna a kujerar zaman mutum uku yayinda ita da Aishan suka zauna a kujerun zaman mutum daya. Yaya Bello ya dubi Aishan yace
‘Aisha me yake faruwa ne, kamar mamakin ganin juna kukeyi ke har kina share kwalla. Me yake faruwa ne?’
Bata sami bakin bayar da amsa ba saboda hawayen da take ta faman tokarewa ne ya kwace ya wanke mata fuska gaba daya, ta sa hannu ta fara share hawayen.
Cikin tsananin damuwa da mamaki Yaya Bello ya gyara zama yana dubansu daga wannan ya dubi wannan. Yace
‘Yusufa wai me yake faruwa ne? Kayi min bayani.’
Ya sa hannu ya goge fuskarsa yana muttsike ido kamar wanda ya tashi daga bacci, a hankali ya bude baki yace
‘Yaya babu komai fa, na dai dade ban ga Aishan bane kawai.’
Ya dubi Aishan wadda ta sunkuyar da kai tana share hawaye yace
‘Ikon Allah! To yaji tayi ko rabuwa kuka yi amma baku sanar ba.’
Gaba daya su suka yi shiru kowa yana ta faman zare ido, itama Anti Zulaiha sai kallonsu take tana mamaki don bata ma fahimci kan zancen ba. Yaya Bello ya katse shirun ya dubi Aishan yace
‘Aisha me yake faruwa ne? Ya sake ki ne ko me ya faru?’
Ta share hawaye tace
‘A’a bai sake ni ba, ya dai kusa shekara biyu bai zo gidan da nake ba shi yasa muka dade bamu hadu ba.’
Yaya Bello ya sake shiga rudani, ya kalli Aishan ya kalli Yusuf din. Aisha ta sake share hawaye, ta bashi labarin yanda abubuwan suka faru. Binta kawai yake da kallo yana mamaki. Ya dubi Abban Sadik din yace
‘Yusufa kai kuma kana auren mace kawai sai baka ganta ba kuma ba zaka nemeta ba?’
Ya share gumi yace
‘Wallahi Yaya ni kaina har yanzu ina mamaki, don ni sai yanzu ma fa da na ganta na tuna da ita. Na kasa gane me yake faruwa ma gaba daya wallahi.’
‘Ikon Allah! To ni kaina ma ban fahimceku ba. Amma Yusufa ya za ayi ace kai da matarka kuma ga gidan da take kusa da daya gidan amma kace wai ka kusa shekara baku hadu ba. Wannan din wacce irin rayuwa ce?’
‘Wallahi Yaya nima sai yanzun nake mamaki, kamar ma gaba daya mantawa nayi da wani bangaren na rayuwata. Gaba daya ma na kasa ganewa.’
Sukayi shiru kowa da abinda yake ransa. Jimawa kadan Anti Karima tayi gyaran murya tace
‘Gaskiya Abban Muhammad ni ina ga ka kirawo Malam Sama’ila tunda yau asabar watakila yana gida, domin wannan abun yayi kama da aljannu ko shaidanu. Gara ka gane kan komai a dauki mataki kafin su bar nan su sake komawa ruwa.’
Yace
‘Hakane gaskiya, bari nayi masa waya na san yanzu zai shigo in sha Allah.’
Ya dauko waya ya kirawoshi, yace masa yana bakin titi zai fita amma yanzu zai dawo.
Sukayi shiru suna jiransa.
Jimawa kadan Yaya Bello ya kasa hakuri ya kirawo Muhammad yace masa ya fita waje da zarar Malam Sama’ila ya zo su shigo tare. Yana fitowa suka hadu suka shigo ya nuna masa falon.
Bayan sun gaisa Abban Muhammad yayi masa bayanin abinda yake faruwa, ya rufe da
‘To Malam Sama’ila abun ne naga kamar na mutanen boye, to shine nace gara ka zo muji ko da akwai abinda za a taimaka da shi.’
Yayi shiru yana jijjiga kai, jimawa kadan yace