Sashe 48
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tabbas da Rukayya ce ita kadai da tuni yace ta koma gidansu, to amma Amira ma tana nan. Sun yi bake-bake sun hanashi sakat a gidan ita kuma Aishan taki ta bashi fuska. Lokutan da yake samunta ita kadai kuma yawanci da yamma na, ya san idan ya takura sai ya karya musu azumin don haka ya hakura wadannan kwana biyun tsakaninta da shi sai kallo daga nesa; gaba daya taki sauraronsa.
___
Ranar Talata aka tashi da sallah karama; tun asuba ita da su Rukayya suka fada kicin, da yake abincin ba mai yawa takeyi ba nan da nan suka hada tuwon shinkafa da miyar gyada, ga kuma funkaso da farfaesun kaji. Amira ta hada kunun aya suka zuba a firji.
Karfe takwas saura Abban ya fito a shirye, yayi mata sallama sannan ya wuce gidan Zahra.
Suma duk sun gama wani shirin Sallah sai tuwo wanda Jummai take karasa kwashewa. Sadiku kawai ya dauka suka wuce masallacin idi.
Bayan sun dawo daga idi ne kamar yanda aka saba duk shekara ya kirawo Sadiku ya bashi abincin sallar gidan Aisha ya hada da na gidan Mommy yace Ali direba ya kaishi tare da Nana da Ummi su kaiwa Hajiya.
A falon Aishan ya zauna ta kawo masa abinci; ta sha kwalliyar sallarta cikin leshinta me ruwan hoda, tayi kyau matuka sai dai kawai yanda take daure fuska ne yake gundurar dashi.
Yana zaune a falo yayinda Aishan take kwashe kwanukan da yaci abinci Rukayya da Amira suka fito daga daki, bayan sun gaisheshi yace
‘Iyye, anko kuka yi ne keda kawar taki Rukayya?’
‘Eh Abba Anti ce tayi mana wannan kayan.’
‘Iyye ‘yan man Anti. Bari ni kuma na baku barka da da sallah kada ayi ta yawo jakar ‘yan mata ba ko sisi.’
Ya zaro sabbin kudi 'yan Naira hamsin ya basu kowa dari biyar, sukayi godiya suka wuce kicin inda suka jiyo motsin Aishan.
Suna shiga Amira ta mariraice tace
‘Um Anti don Allah ki bamu kudin mota muje gidan Anti Hida, itama Rukayyan tana son zuwa wallahi.’
Ta kyalkyale da dariya
‘Lallai yaran nan, na baku kudin mota ku tafi a motar haya ko? To ba inda zaku je. In dai cikin gari ne na gaya muku ku shirya gobe sai muje ko kuma ku bari da yamma ma je tare.’
Amira ta sake mararaicewa
‘Anti don Allah, wallahi zamu gane ko Rukayya. Kinga Anti idan bamu je da wuri ba kafin muje duk su Farha sun je kuma Baban Anwar zai kai su cikin gidan sarki banda mu.’
‘To ke Amira duk shekara ai dake ake zuwa gidan sarkin menene idan yau daya baki je ba, kya je da Babbar sallah.’
‘Anti da Rukayya nake so na nunawa bata taba shiga gidan sarki ba ita.’
Kafin ta basu amsa Abba ya taso ya tsaya a bayan su, yace
‘Wai ina za aje ne ake ta magiya haka.’
Aishan ce ta amsa
‘Wai gidan Zahida suke son zuwa a motar haya don bazasu jirani muje gobe ba.’
‘A’a gidan Zahida ai ba matsala bane, bari na kirawo Aliko ya kai ku in ya so idan kuka gama sai kuyi waya na turo shi ya dauko ku.’
Gaba daya suka hada baki suna masa godiya, suka koma dakin da gudu suka fara shiri.
Ta ajiye kwanukan da take kifewa ta nufo kicin din da niyyar fita tana fadin
‘Bari na shirya sai mu tafi tare in ya so gobe na huta.’
Tana zuwa zata wuce ya dan matso ya takureta a bakin kofar ya kawo bakinsa kusa da kunnenta ya rada mata
‘Ban barki ba.’
Ya hura mata iska a kunnen nata har ta dan noke sannan ya wuce inda ya taso ya dauki wayarsa ya kirawo Aliko; wanda dama yana gidan Mommy.
Ta karasa ta ja kujerar dining table ta zauna ta dafe goshi tana tunani.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
27
Takaicinsa ne ya kuleta, tunda take aurensa bai taba cewa ya hanata fita unguwa ba sai yau. Ta san manufarsa amma bata jin zata iya bashi hadin kai; haka kawai matarsa ta dawo ya sake mantawa da ita.
Tana nan su Amira suka fito sukayi mata sallama suna ta jin dadi suka fice.
Ta mike ta shige dakinta ta turo kofar.
Tana jinsa yana nemanta bayan ya sallami direban. Sai da ya duba kichin da dakinsa sannan ya shigo dakin nata.
Tana kashingide a gefen gadonta ta jingine kanta jikin gadon; bata amsa sallamar da yayi ba haka ya karasa inda take.
‘Aisha.’
Ta share hawayen da yake fuskarta tana shesshekar kuka. Da sauri ya karasa ya zauna a gefenta cikin matsananciyar damuwa.
‘Aisha kukan me kike yi? Don na hanaki fita ne kike kuka? In dai wannan ne idan nayi sallar la’asar s na kaiki da kaina.’
Ta sake share hawaye ta muskuta ba tare da tace masa komai. Sukayi shiru na dan lokaci yana tunanin ta inda zai fara.
Ya gyara zama ya dafa cinyarta sannan yace
‘Don Allah ki daina kukan nan Aisha, kin san bana son damuwarki.’
Suka sake yin shiru ba tare da ta motsa ba, ya gaji da sauraron ta tayi magana batayi ba. Ya dawo gabanta ya tsuguna daga gaban gadon yanda zai dinga ganin fuskarta. Yace
‘Aisha don Allah kiyi hakuri, ki gaya min me ya saki kukan nan. Idan rashin zuwa wajenki ne da bana yi wallahi ba yin kaina bane, abun ne yafi karfina. Yanzu kuma da kika ganni Allah ya kawo karshen abun ne don malamin da ya warware abun ma yana tunanin aljanu ne ko tsafi, ai sai mu godewa Allah da abun ya tsaya haka ko? Kiyi hakuri Aisha, kin san ba zan taba gudunki ba.’
Suka sake yin shiru na dan lokaci.
‘Aisha, don Allah kiyi hakuri ki daina fushin nan kin san bana son kukan ki kuma bana son kina fushi da ni. Kiyi hakuri kin ji.’
Ta kalleshi yanda ya tsuguna a gabanta ta share ragowar hawayen fuskarta tace
‘Ni ba fushi nakeyi ba.’
‘To me yasa ki kuka? Um?’
Ya taso ya dawo kan gadon gefenta, ya kama hannunta, tana nokewa yana jan hannun yana fadin
‘Bana son kukan nan.’
So yake ta saki jiki ya janyota jikinsa amma ta ki, don haka ya kara dagewa ya janyota har saida ta dan fado jikinsa. Ya sa hannunsa yana goge mata hawayen, daya hannun kuma yana janyo kafadarta don ta kara kwantawa a jikinsa.
‘Shikenan, ni dama ba fushi nayi ba. Amma dai ina so ka koma can gidan idan Mommy din ta dawo sai ka fara rabon kwanan ta kanta sai a cigaba.’
Ya leka fuskarta suka hada ido, yace
‘No, ai ba sai an yi haka ba tunda dama kwanan a rabe yake ko?’
Ya dan muskuta ya kawo bakinsa daidai kunneta sannan yace a can kasan makoshinsa
‘Kin san fa nayi kewarki ba kadan ba…'
Ya cigaba da lalube jikinta sako da Loko, tun tana kokarin kwacewa har ta hakura ta bada kai bori ya hau.
Nan suka balbalce har aka fara kiran sallar la’asar; yana ta tsara mata dadadan kalamansa na lallashi da ban hakuri.
‘La’asar fa nake ji kamar, ko azahar fa bamuyi ba.’
Ta fada tana shirin mikewa, yayi murmushi yace
‘Subhanallah, kin san an fara kiran azahar lokacin da na shigo kuma sai na manta.’
Nan da nan suka fada wanka.
Sai da suka shirya suka yi Sallah sannan ya sanar da ita ta kirawo su Rukayya tace idan anyi sallar isha’i zai kaita ta su daukosu.
Ya san duk halin da aka shiga dole ‘yanuwanta sun sani don haka zai yi amfani da wannan damar ya nunawa ‘yan uwanta cewa komai ya dawo dai-dai.
__
Tun washegarin Sallah yara suke shirin taren Mommy, don ya zama saura kwana biyu kenan ta dawo. Ko ina an share an goge tsaf banda dakinta wanda ta bayar da umarni kada a bude mata.
Rukayya ta hada kayan hadi zata yiwa Mommy cake, ta so ace ita da Amira ne zasu yi cake din sai dai tana tsoron ta shiga da Amira gidan Yusra tayi mata wulakanci don ta san Amiran ma ba zata dauki raini ba musamman tunda kusan sa’ar Yusran ce. Tana hada kan kayan cake din Yusra tana mata dariya a kan bata iya wani cake ba ta bari kawai suyi order kada ta bawa Mommy kunya; ita dai ta kafe a kan lallai sai tayi cake.
Kuma daga karshe da tayi cake din kowa sai da ya yaba.
…………
Wunin ranar Sallah gaba daya tana ta faman kiran Abban yana gaya mata baya tare da yara, bai gaya mata inda yake ba amma ta san yana gidan Aisha. Ta gaji da wannan abun takaicin gashi bata taho da wayarta ba balle ta kirawo yaron Malam, don haka tun safe take faman kiran Amina amma bata dauka ba. Don haka kusan ba a hayyacinta ta wuni ba. Ya kamata ace taje ta karasa sayayya amma ta kasa zuwa; kudin ma duk da ta riga ta kashe mafi yawa amma dai tana jin ba zata sake kashe kudi ba don ta san idan ta dawo tana bukatar kudi sosai; a halin yanzu ma duk tunaninta yana kan yanda zata sami kudi ne don ta fara tunanin canza malami tunda shi yaron Malam kamar aikinsa baya nisan zango.
Sai dare ta sami Amina, tayi mata bayanin halin da ake ciki. Suna ajiye waya ta tura mata lambar yaron Malam.
Kauyen su yaron Malam babu network sosai don haka duk kokarinta na ganin ta sameshi basu iya magana ba; shi baya jinta kwata-kwata. Daga karshe dai ya gaji ya turo mata sako cewa suyi magana ta Whatsapp kawai. Kwana biyun nan jinta take kamar a kan kaya, don haka ba cikin nutsuwa ta karasa su ba.
-------
Ranar Juma’a itace ta kama kwana hudu ga Sallah kuma tayi dai-dai da ranar da Zahra Uwar Saddiku zata dawo daga kasa mai tsarki.
Tun dare ta kirawo Abban ta sanar da shi jirginsu zai sauka da misalin karfe biyar na yamma; ta so kwarai ya zo daukanta da kanshi a airport sai dai ya sanar da ita zai fita bayan la’asar don haka dai Malam Ali ne zai zo.
___
Ranar Talata aka tashi da sallah karama; tun asuba ita da su Rukayya suka fada kicin, da yake abincin ba mai yawa takeyi ba nan da nan suka hada tuwon shinkafa da miyar gyada, ga kuma funkaso da farfaesun kaji. Amira ta hada kunun aya suka zuba a firji.
Karfe takwas saura Abban ya fito a shirye, yayi mata sallama sannan ya wuce gidan Zahra.
Suma duk sun gama wani shirin Sallah sai tuwo wanda Jummai take karasa kwashewa. Sadiku kawai ya dauka suka wuce masallacin idi.
Bayan sun dawo daga idi ne kamar yanda aka saba duk shekara ya kirawo Sadiku ya bashi abincin sallar gidan Aisha ya hada da na gidan Mommy yace Ali direba ya kaishi tare da Nana da Ummi su kaiwa Hajiya.
A falon Aishan ya zauna ta kawo masa abinci; ta sha kwalliyar sallarta cikin leshinta me ruwan hoda, tayi kyau matuka sai dai kawai yanda take daure fuska ne yake gundurar dashi.
Yana zaune a falo yayinda Aishan take kwashe kwanukan da yaci abinci Rukayya da Amira suka fito daga daki, bayan sun gaisheshi yace
‘Iyye, anko kuka yi ne keda kawar taki Rukayya?’
‘Eh Abba Anti ce tayi mana wannan kayan.’
‘Iyye ‘yan man Anti. Bari ni kuma na baku barka da da sallah kada ayi ta yawo jakar ‘yan mata ba ko sisi.’
Ya zaro sabbin kudi 'yan Naira hamsin ya basu kowa dari biyar, sukayi godiya suka wuce kicin inda suka jiyo motsin Aishan.
Suna shiga Amira ta mariraice tace
‘Um Anti don Allah ki bamu kudin mota muje gidan Anti Hida, itama Rukayyan tana son zuwa wallahi.’
Ta kyalkyale da dariya
‘Lallai yaran nan, na baku kudin mota ku tafi a motar haya ko? To ba inda zaku je. In dai cikin gari ne na gaya muku ku shirya gobe sai muje ko kuma ku bari da yamma ma je tare.’
Amira ta sake mararaicewa
‘Anti don Allah, wallahi zamu gane ko Rukayya. Kinga Anti idan bamu je da wuri ba kafin muje duk su Farha sun je kuma Baban Anwar zai kai su cikin gidan sarki banda mu.’
‘To ke Amira duk shekara ai dake ake zuwa gidan sarkin menene idan yau daya baki je ba, kya je da Babbar sallah.’
‘Anti da Rukayya nake so na nunawa bata taba shiga gidan sarki ba ita.’
Kafin ta basu amsa Abba ya taso ya tsaya a bayan su, yace
‘Wai ina za aje ne ake ta magiya haka.’
Aishan ce ta amsa
‘Wai gidan Zahida suke son zuwa a motar haya don bazasu jirani muje gobe ba.’
‘A’a gidan Zahida ai ba matsala bane, bari na kirawo Aliko ya kai ku in ya so idan kuka gama sai kuyi waya na turo shi ya dauko ku.’
Gaba daya suka hada baki suna masa godiya, suka koma dakin da gudu suka fara shiri.
Ta ajiye kwanukan da take kifewa ta nufo kicin din da niyyar fita tana fadin
‘Bari na shirya sai mu tafi tare in ya so gobe na huta.’
Tana zuwa zata wuce ya dan matso ya takureta a bakin kofar ya kawo bakinsa kusa da kunnenta ya rada mata
‘Ban barki ba.’
Ya hura mata iska a kunnen nata har ta dan noke sannan ya wuce inda ya taso ya dauki wayarsa ya kirawo Aliko; wanda dama yana gidan Mommy.
Ta karasa ta ja kujerar dining table ta zauna ta dafe goshi tana tunani.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
27
Takaicinsa ne ya kuleta, tunda take aurensa bai taba cewa ya hanata fita unguwa ba sai yau. Ta san manufarsa amma bata jin zata iya bashi hadin kai; haka kawai matarsa ta dawo ya sake mantawa da ita.
Tana nan su Amira suka fito sukayi mata sallama suna ta jin dadi suka fice.
Ta mike ta shige dakinta ta turo kofar.
Tana jinsa yana nemanta bayan ya sallami direban. Sai da ya duba kichin da dakinsa sannan ya shigo dakin nata.
Tana kashingide a gefen gadonta ta jingine kanta jikin gadon; bata amsa sallamar da yayi ba haka ya karasa inda take.
‘Aisha.’
Ta share hawayen da yake fuskarta tana shesshekar kuka. Da sauri ya karasa ya zauna a gefenta cikin matsananciyar damuwa.
‘Aisha kukan me kike yi? Don na hanaki fita ne kike kuka? In dai wannan ne idan nayi sallar la’asar s na kaiki da kaina.’
Ta sake share hawaye ta muskuta ba tare da tace masa komai. Sukayi shiru na dan lokaci yana tunanin ta inda zai fara.
Ya gyara zama ya dafa cinyarta sannan yace
‘Don Allah ki daina kukan nan Aisha, kin san bana son damuwarki.’
Suka sake yin shiru ba tare da ta motsa ba, ya gaji da sauraron ta tayi magana batayi ba. Ya dawo gabanta ya tsuguna daga gaban gadon yanda zai dinga ganin fuskarta. Yace
‘Aisha don Allah kiyi hakuri, ki gaya min me ya saki kukan nan. Idan rashin zuwa wajenki ne da bana yi wallahi ba yin kaina bane, abun ne yafi karfina. Yanzu kuma da kika ganni Allah ya kawo karshen abun ne don malamin da ya warware abun ma yana tunanin aljanu ne ko tsafi, ai sai mu godewa Allah da abun ya tsaya haka ko? Kiyi hakuri Aisha, kin san ba zan taba gudunki ba.’
Suka sake yin shiru na dan lokaci.
‘Aisha, don Allah kiyi hakuri ki daina fushin nan kin san bana son kukan ki kuma bana son kina fushi da ni. Kiyi hakuri kin ji.’
Ta kalleshi yanda ya tsuguna a gabanta ta share ragowar hawayen fuskarta tace
‘Ni ba fushi nakeyi ba.’
‘To me yasa ki kuka? Um?’
Ya taso ya dawo kan gadon gefenta, ya kama hannunta, tana nokewa yana jan hannun yana fadin
‘Bana son kukan nan.’
So yake ta saki jiki ya janyota jikinsa amma ta ki, don haka ya kara dagewa ya janyota har saida ta dan fado jikinsa. Ya sa hannunsa yana goge mata hawayen, daya hannun kuma yana janyo kafadarta don ta kara kwantawa a jikinsa.
‘Shikenan, ni dama ba fushi nayi ba. Amma dai ina so ka koma can gidan idan Mommy din ta dawo sai ka fara rabon kwanan ta kanta sai a cigaba.’
Ya leka fuskarta suka hada ido, yace
‘No, ai ba sai an yi haka ba tunda dama kwanan a rabe yake ko?’
Ya dan muskuta ya kawo bakinsa daidai kunneta sannan yace a can kasan makoshinsa
‘Kin san fa nayi kewarki ba kadan ba…'
Ya cigaba da lalube jikinta sako da Loko, tun tana kokarin kwacewa har ta hakura ta bada kai bori ya hau.
Nan suka balbalce har aka fara kiran sallar la’asar; yana ta tsara mata dadadan kalamansa na lallashi da ban hakuri.
‘La’asar fa nake ji kamar, ko azahar fa bamuyi ba.’
Ta fada tana shirin mikewa, yayi murmushi yace
‘Subhanallah, kin san an fara kiran azahar lokacin da na shigo kuma sai na manta.’
Nan da nan suka fada wanka.
Sai da suka shirya suka yi Sallah sannan ya sanar da ita ta kirawo su Rukayya tace idan anyi sallar isha’i zai kaita ta su daukosu.
Ya san duk halin da aka shiga dole ‘yanuwanta sun sani don haka zai yi amfani da wannan damar ya nunawa ‘yan uwanta cewa komai ya dawo dai-dai.
__
Tun washegarin Sallah yara suke shirin taren Mommy, don ya zama saura kwana biyu kenan ta dawo. Ko ina an share an goge tsaf banda dakinta wanda ta bayar da umarni kada a bude mata.
Rukayya ta hada kayan hadi zata yiwa Mommy cake, ta so ace ita da Amira ne zasu yi cake din sai dai tana tsoron ta shiga da Amira gidan Yusra tayi mata wulakanci don ta san Amiran ma ba zata dauki raini ba musamman tunda kusan sa’ar Yusran ce. Tana hada kan kayan cake din Yusra tana mata dariya a kan bata iya wani cake ba ta bari kawai suyi order kada ta bawa Mommy kunya; ita dai ta kafe a kan lallai sai tayi cake.
Kuma daga karshe da tayi cake din kowa sai da ya yaba.
…………
Wunin ranar Sallah gaba daya tana ta faman kiran Abban yana gaya mata baya tare da yara, bai gaya mata inda yake ba amma ta san yana gidan Aisha. Ta gaji da wannan abun takaicin gashi bata taho da wayarta ba balle ta kirawo yaron Malam, don haka tun safe take faman kiran Amina amma bata dauka ba. Don haka kusan ba a hayyacinta ta wuni ba. Ya kamata ace taje ta karasa sayayya amma ta kasa zuwa; kudin ma duk da ta riga ta kashe mafi yawa amma dai tana jin ba zata sake kashe kudi ba don ta san idan ta dawo tana bukatar kudi sosai; a halin yanzu ma duk tunaninta yana kan yanda zata sami kudi ne don ta fara tunanin canza malami tunda shi yaron Malam kamar aikinsa baya nisan zango.
Sai dare ta sami Amina, tayi mata bayanin halin da ake ciki. Suna ajiye waya ta tura mata lambar yaron Malam.
Kauyen su yaron Malam babu network sosai don haka duk kokarinta na ganin ta sameshi basu iya magana ba; shi baya jinta kwata-kwata. Daga karshe dai ya gaji ya turo mata sako cewa suyi magana ta Whatsapp kawai. Kwana biyun nan jinta take kamar a kan kaya, don haka ba cikin nutsuwa ta karasa su ba.
-------
Ranar Juma’a itace ta kama kwana hudu ga Sallah kuma tayi dai-dai da ranar da Zahra Uwar Saddiku zata dawo daga kasa mai tsarki.
Tun dare ta kirawo Abban ta sanar da shi jirginsu zai sauka da misalin karfe biyar na yamma; ta so kwarai ya zo daukanta da kanshi a airport sai dai ya sanar da ita zai fita bayan la’asar don haka dai Malam Ali ne zai zo.