Sashe 18
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
‘Ka san dai fushinka baya min dadi, don Allah kayi hakuri in dai nice ba zan sake ba.’
Ya juyo gaba daya ya tsaya yana kallonta, har ya bude baki zai yi magana sai kuma ya fasa. Yadan matso kusa da ita sannan yace
‘In dai baki sake ba ya wuce.’
‘In sha Allah ba zan sake ba.’
Ya mayar mata da murmushin da take ta yi masa sannan ya juya ya wuce gaban wardrobe ya debo kayan baccinsa ya fara canzawa.
Tace
‘Idan ka shirya na saka abincin dare.’
‘Ok, yanzu zan sauko.’
Ta juya ta fice daga dakin cike da takaici bashi hakurin da tayi.
Bayan sun gama cin abinci suka zauna a falonsa suka dan taba hira, da ta kula ya fara jin bacci ta tashi ta shige dakinta ta sake shiryowa ta sa rigar bacci ta fito ta shige dakinsa.
A dabi’arsa baya neman matarsa sai yayi bacci kai daya, lokacin dare ya raba sosai kuma dukansu sun rage baccin. Ga mamakinsa yau yana kwanciya ta fara lalubensa, bai kawo wani abu don wannan ba bakon abu bane tunda matarsa ce; kawai dai ya san ta saba jira sai sun rage baccin musamman da yake mafi yawa cin lokuta kafin ya kwanta ita din bacci ya dauketa.
Haka sukayita fama; yana yi yana mamakin yanda yau gaba daya take kamar a gigice tunda ya riga ya saba shi yake sarrafata kuma a hankali yanda yake so. Bai yi mamaki sosai ba don ya san akwai abubuwan da mata suke Sha musamman don wannan harkar, don haka yake tunanin itama wani abun ta sha.
Suna gamawa kamar yanda ya saba ya zare jikinsa yaje yayi wanka, bayan ya fito ya tabata yace mata taje tayi wanka ko kuma tayi alwala idan ba yanzu zata yi wankan ba. Haka ta tashi taje ta wanko jikinta tayi alwala ta fito ta sake kwanciya.
Can cikin dare baccinsa yayi nauyi ta sake lalubarsa, kamar a mafarki ya farka. Ya gyara kwanciya yace
‘Yau bakya jin bacci kenan?’
Tayi ‘yar dariya ta amsa
‘Um.’
Suka cigaba. Baya son ya rasa sallar asuba a masallaci don haka suna gamawa ya tashi yayi wanka, itama ta tashi tayi nata wankan lokacin wajen karfe uku da rabi na dare. Suka koma suka sake kwanciya.
Ko da yaje masallaci ya dawo yaci burin biyan bashin baccin da ya ci, saida yayiwa sakatarensa message yace masa zai dan makara don ya samu yayi bacci sannan ya koma ya kwanta.
Tana idar da sallah itama ta dawo ta kwanta, yayi zaton bacci zasuyi kamar yanda suka saba don wani lokacin sai wajen karfe shida take tashi ta shiga kicin don shirya ‘yan makaranta.
Tana kwanciya ta laluboshi, duk yadda ya so ya kyaleta kasawa yayi; ba wai saboda yana bukatarta a wannan lokacin ba sai don yana ganin matarsa ce ba zai iya kyaleta ba musamman da wannan bukatar. Suna gamawa lokacin har shida ta gota don haka a gurguje ta mayar da kayanta ta wuce kasa don shirya ‘yan makaranta. Ta fuskanci gajiyawarsa wanda dama haka takeso; so take ta sauke masa duk wata sha’awa da yake da ita saboda idan yaje kwanan Aisha sai ya kwanta yayi ta baccin a can ba tare da ya kusanceta ba.
Tana fita daga dakin ya tashi ya shiga wanka, bayan ya fito daga wankan ya zauna a kujerar gaban mudubi ya kafa tagumi; me ya sami matar nan ne? Ko ma me ta sha gaskiya yau ta jigata shi. Bacci yake so ya koma amma ya hakura saboda yana tunanin idan ta sameshi a kwance bayan yara sun tafi makaranta to lallai zata sake nemansa shi kuwa ya san ba zai iya ba. Don haka nan da nan ya shirya ya sauko dai-dai lokacin yara sun fice.
Ta saka mishi abincinsa wanda yana gama ci yayi mata sallama ya fice, gidan Aisha ya shiga don ya dubata inda ta sanar da shi sati mai zuwa zata koma aiki. Yayi mata sallama ya fice bayan ya sanar da ita zasu dinga fita da yara idan Malam Sule ya ajiyeta sai ya wuce da su.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
12
Kwanakin nan biyu haka Abban Sadik yayisu babu baccin kirki saboda yanda suke kwana hidima, har Allah-Allah ya dinga yi kwanan Zahra ya kare ya koma wajen Aisha.
Ranar da zai koma wajen Aisha kuwa da wuri ya dawo daga wajen aiki, ana cikin kiran sallar isha’i .
Wajen Zahra ya wuce kai tsaye, bayan sun masa sannu da zuwa ita da yaran ya amsa ya dubeta yace
‘Bari na wuce don yau a gajiye nake wallahi, don Allah da zarar karfe tara tayi ki rufe gidan nan kar a sake budewa sai da safe.’
‘To in Sha Allah zan rufe.’
Yayi musu sallama ita da yaran ya fice.
Ta bi bayansa da kallo tana murmushin jin dadi, domin aikin da tayi ta san yau din nan idan banda bacci babu abinda zai iya.
Hakan kuwa aka yi; ita Aisha bata kawo komai domin bata da matsala da hakan, suka kwana suna baccinsu har asuba. Ko da gari ya waye haka suka gama hirarrakinsu ya shirya yayi tafiyarsa aiki.
Har saida aka sake kwana bayan ya dawo daga masallaci sannanne wani abu ya shiga tsakanin sa da Aisha, a nutse yanda ya saba kuma yanda yake so suka farantawa juna. Da dare yayi kuma ya koma kwanan Zahra.
Yana fargaba da addu’ar Allah ya sa yau bata sha abinda ta sha wancan karon ba don gaskiya ya fi so yaji dadi yana cikin hayyacinsa.
Yanda akayi wancan karon din kuwa haka aka sakeyi, babu yanda ya iya haka ya dinga hakura da baccinsa. Saida ya koma wajen Aisha sannan ya maimaita mata yanda yayi.
Haka suka cigaba da yi duk da ita Aisha bata dauki abun a matsala ba, sau dayan nan ya isheta musamman da yake yana daukan lokaci ya tabbatar bukatarta ta biya. Haka rayuwa ta cigaba.
Zahra bata taba shiga gidan Aisha ba kuma bata turo yaranta, tunda tana amarya dai data tura Yusra da waya ta dauko mata hoton falon bata sake tura su ba. Rukayya ce kawai take zuwa tayata kwana, itama don babu yanda Zahran zata yi ne. Sai kuma Allah ya sa Aishan da Rukayya jininsu ya hadu sosai, don haka Rukayyan take jin dadi zuwa kwana; duk da dai idan gari ya waye ta fito daga gidan Mommy hanata komawa takeyi har sai wani daren.
_
Yanda ya saba duk karamar sallah kaya kala uku yake yiwa kowa, tsakanin Zahra da yaranta. Idan kuma babbar sallah ta zo to kaya kala daya yake musu, sannan kuma ya kawo sa da rago wanda za a yanka na layya.
Ranar asabar ce don haka yana gida da yamma, suna zaune shida Zahra a falonsa suna hira; da yake yaran duk sun tafi islamiyya. Ya dubeta yace
‘Sallah fa ta matso, ya za ayi ne da kayan sallarku?’
Tayi ‘yar dariya
‘Yanda aka saba mana, ka san dai a wajena ake siya ko business din nawa ya dan samu cigaba.’
‘Hakane, to zan tura miki dubu dari da hamsin, yara kowa dubu ashirin ke kuma hamsin. In ya so sai ki kawo muku abinda kike so, ita kuma kanwarki itama sai na tura mata hamsin din.’
Ta langabe kai
‘Haba yallabai, to ita ba zata yi min cinikin ba? Ka turo har natan mana na dai san ba zai wuce leshi ba. Za a kawo su kala-kala in ya so sai tazo ta zaba.’
‘E kuma kinga hakan ma zaifi, ta huta da shiga kasuwa.’
‘Kwarai kuwa. Amma gaskiya da zaka karawa yara ko da dubu biyar-biyar ce ka san fa kayan yanzu sun dan kara kudi.’
‘A’a hakan ma zai isa. Kin san fa Babbar Sallah ce dole sai na tanadi abun layya. Ni ban ma sani ba na siyo sa kamar yanda na saba ko kuma na siyo muku raguna dai-dai ke da kanwarki yara kuma a basu biyu.’
‘Haba dai, ai sa ya fi auki. Idan ka siyo mana sa daya da rago ya ishemu gaba daya idan muka hadu muka soya sai a raba. Sai dai idan ita Aishan ta fi son rago sai a bata nata.’
‘A’a na san bata da matsala, bari dai naje kasuwar naji farashin dabbobin tukunna sai ayi wanda ya samu.’
Suka gama hirarrakinsu daga baya ta barshi a nan ta shiga kicin dora abincin dare.
……..
Sallah saura sati biyu Aisha ta tashi da wani zazzabi, da kanshi ya kaita asibiti. Aka yi mata duk wasu gwaje-gwaje da suka dace, aka tabbatar bata dauke da juna biyu, sai dai malaria don haka aka rubuta mata magunguna suka kamo hanya.
Har suka zo gida yana tsokanarta a kan shi ya fara murna har ya gama shawara idan mace ta haifa Aisha zai mayar idan kuma namiji ne Muhammad. Haka suka tsaya a chemist aka yi mata allurai sannan suka dawo gidan.
Kwana biyu ta fara warwarewa, da daddare suna zaune a falo ya mike kafafunsa ta tada kai da cinyoyinsa ta kwanta suna hira kuma suna kallon TV.
Yace
‘Wai Sallah ta kusa ke ko labarin kayan Sallah ba kya yi balle na abun layya.’
Tayi dariya tace
‘Wai da yake ba ni zanyi ba, kuma na san mai yi yana sane da lokacin.’
‘Lallai ne baki da matsala. To akwai leshina a wajen yayarki, gobe sai ki shiga ki zabi daya. Kin san tana sayar da kayan sawa shi yasa kawai nake sayen kayan sallar a wajenta.’
Ranta ya sosu, Yaya za ayi yace matarsa ce zata saya mata kayan Sallah ko an gaya masa ita babu masu sayar da kayan a danginta. Bata son ta ja maganar yaga kamar ta damu; kuma da yake tana da ragowar kaya a akwatin lefenta sai abun bai dameta ba sannan kuma akwai leshi da suka siya ita da ‘yan gidansu wanda daga Switzerland suka tura kudi aka siyo musu don nata ma yana wajen tele inda Zahida ta kai musu dinki, don haka tace
‘Ka gani ni dai ina fama da kaina gobe ban san yanda zan tashi ba, idan ka je kawai ka zabo min wanda ya burgeka.’
Ya juyo gaba daya ya tsaya yana kallonta, har ya bude baki zai yi magana sai kuma ya fasa. Yadan matso kusa da ita sannan yace
‘In dai baki sake ba ya wuce.’
‘In sha Allah ba zan sake ba.’
Ya mayar mata da murmushin da take ta yi masa sannan ya juya ya wuce gaban wardrobe ya debo kayan baccinsa ya fara canzawa.
Tace
‘Idan ka shirya na saka abincin dare.’
‘Ok, yanzu zan sauko.’
Ta juya ta fice daga dakin cike da takaici bashi hakurin da tayi.
Bayan sun gama cin abinci suka zauna a falonsa suka dan taba hira, da ta kula ya fara jin bacci ta tashi ta shige dakinta ta sake shiryowa ta sa rigar bacci ta fito ta shige dakinsa.
A dabi’arsa baya neman matarsa sai yayi bacci kai daya, lokacin dare ya raba sosai kuma dukansu sun rage baccin. Ga mamakinsa yau yana kwanciya ta fara lalubensa, bai kawo wani abu don wannan ba bakon abu bane tunda matarsa ce; kawai dai ya san ta saba jira sai sun rage baccin musamman da yake mafi yawa cin lokuta kafin ya kwanta ita din bacci ya dauketa.
Haka sukayita fama; yana yi yana mamakin yanda yau gaba daya take kamar a gigice tunda ya riga ya saba shi yake sarrafata kuma a hankali yanda yake so. Bai yi mamaki sosai ba don ya san akwai abubuwan da mata suke Sha musamman don wannan harkar, don haka yake tunanin itama wani abun ta sha.
Suna gamawa kamar yanda ya saba ya zare jikinsa yaje yayi wanka, bayan ya fito ya tabata yace mata taje tayi wanka ko kuma tayi alwala idan ba yanzu zata yi wankan ba. Haka ta tashi taje ta wanko jikinta tayi alwala ta fito ta sake kwanciya.
Can cikin dare baccinsa yayi nauyi ta sake lalubarsa, kamar a mafarki ya farka. Ya gyara kwanciya yace
‘Yau bakya jin bacci kenan?’
Tayi ‘yar dariya ta amsa
‘Um.’
Suka cigaba. Baya son ya rasa sallar asuba a masallaci don haka suna gamawa ya tashi yayi wanka, itama ta tashi tayi nata wankan lokacin wajen karfe uku da rabi na dare. Suka koma suka sake kwanciya.
Ko da yaje masallaci ya dawo yaci burin biyan bashin baccin da ya ci, saida yayiwa sakatarensa message yace masa zai dan makara don ya samu yayi bacci sannan ya koma ya kwanta.
Tana idar da sallah itama ta dawo ta kwanta, yayi zaton bacci zasuyi kamar yanda suka saba don wani lokacin sai wajen karfe shida take tashi ta shiga kicin don shirya ‘yan makaranta.
Tana kwanciya ta laluboshi, duk yadda ya so ya kyaleta kasawa yayi; ba wai saboda yana bukatarta a wannan lokacin ba sai don yana ganin matarsa ce ba zai iya kyaleta ba musamman da wannan bukatar. Suna gamawa lokacin har shida ta gota don haka a gurguje ta mayar da kayanta ta wuce kasa don shirya ‘yan makaranta. Ta fuskanci gajiyawarsa wanda dama haka takeso; so take ta sauke masa duk wata sha’awa da yake da ita saboda idan yaje kwanan Aisha sai ya kwanta yayi ta baccin a can ba tare da ya kusanceta ba.
Tana fita daga dakin ya tashi ya shiga wanka, bayan ya fito daga wankan ya zauna a kujerar gaban mudubi ya kafa tagumi; me ya sami matar nan ne? Ko ma me ta sha gaskiya yau ta jigata shi. Bacci yake so ya koma amma ya hakura saboda yana tunanin idan ta sameshi a kwance bayan yara sun tafi makaranta to lallai zata sake nemansa shi kuwa ya san ba zai iya ba. Don haka nan da nan ya shirya ya sauko dai-dai lokacin yara sun fice.
Ta saka mishi abincinsa wanda yana gama ci yayi mata sallama ya fice, gidan Aisha ya shiga don ya dubata inda ta sanar da shi sati mai zuwa zata koma aiki. Yayi mata sallama ya fice bayan ya sanar da ita zasu dinga fita da yara idan Malam Sule ya ajiyeta sai ya wuce da su.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
12
Kwanakin nan biyu haka Abban Sadik yayisu babu baccin kirki saboda yanda suke kwana hidima, har Allah-Allah ya dinga yi kwanan Zahra ya kare ya koma wajen Aisha.
Ranar da zai koma wajen Aisha kuwa da wuri ya dawo daga wajen aiki, ana cikin kiran sallar isha’i .
Wajen Zahra ya wuce kai tsaye, bayan sun masa sannu da zuwa ita da yaran ya amsa ya dubeta yace
‘Bari na wuce don yau a gajiye nake wallahi, don Allah da zarar karfe tara tayi ki rufe gidan nan kar a sake budewa sai da safe.’
‘To in Sha Allah zan rufe.’
Yayi musu sallama ita da yaran ya fice.
Ta bi bayansa da kallo tana murmushin jin dadi, domin aikin da tayi ta san yau din nan idan banda bacci babu abinda zai iya.
Hakan kuwa aka yi; ita Aisha bata kawo komai domin bata da matsala da hakan, suka kwana suna baccinsu har asuba. Ko da gari ya waye haka suka gama hirarrakinsu ya shirya yayi tafiyarsa aiki.
Har saida aka sake kwana bayan ya dawo daga masallaci sannanne wani abu ya shiga tsakanin sa da Aisha, a nutse yanda ya saba kuma yanda yake so suka farantawa juna. Da dare yayi kuma ya koma kwanan Zahra.
Yana fargaba da addu’ar Allah ya sa yau bata sha abinda ta sha wancan karon ba don gaskiya ya fi so yaji dadi yana cikin hayyacinsa.
Yanda akayi wancan karon din kuwa haka aka sakeyi, babu yanda ya iya haka ya dinga hakura da baccinsa. Saida ya koma wajen Aisha sannan ya maimaita mata yanda yayi.
Haka suka cigaba da yi duk da ita Aisha bata dauki abun a matsala ba, sau dayan nan ya isheta musamman da yake yana daukan lokaci ya tabbatar bukatarta ta biya. Haka rayuwa ta cigaba.
Zahra bata taba shiga gidan Aisha ba kuma bata turo yaranta, tunda tana amarya dai data tura Yusra da waya ta dauko mata hoton falon bata sake tura su ba. Rukayya ce kawai take zuwa tayata kwana, itama don babu yanda Zahran zata yi ne. Sai kuma Allah ya sa Aishan da Rukayya jininsu ya hadu sosai, don haka Rukayyan take jin dadi zuwa kwana; duk da dai idan gari ya waye ta fito daga gidan Mommy hanata komawa takeyi har sai wani daren.
_
Yanda ya saba duk karamar sallah kaya kala uku yake yiwa kowa, tsakanin Zahra da yaranta. Idan kuma babbar sallah ta zo to kaya kala daya yake musu, sannan kuma ya kawo sa da rago wanda za a yanka na layya.
Ranar asabar ce don haka yana gida da yamma, suna zaune shida Zahra a falonsa suna hira; da yake yaran duk sun tafi islamiyya. Ya dubeta yace
‘Sallah fa ta matso, ya za ayi ne da kayan sallarku?’
Tayi ‘yar dariya
‘Yanda aka saba mana, ka san dai a wajena ake siya ko business din nawa ya dan samu cigaba.’
‘Hakane, to zan tura miki dubu dari da hamsin, yara kowa dubu ashirin ke kuma hamsin. In ya so sai ki kawo muku abinda kike so, ita kuma kanwarki itama sai na tura mata hamsin din.’
Ta langabe kai
‘Haba yallabai, to ita ba zata yi min cinikin ba? Ka turo har natan mana na dai san ba zai wuce leshi ba. Za a kawo su kala-kala in ya so sai tazo ta zaba.’
‘E kuma kinga hakan ma zaifi, ta huta da shiga kasuwa.’
‘Kwarai kuwa. Amma gaskiya da zaka karawa yara ko da dubu biyar-biyar ce ka san fa kayan yanzu sun dan kara kudi.’
‘A’a hakan ma zai isa. Kin san fa Babbar Sallah ce dole sai na tanadi abun layya. Ni ban ma sani ba na siyo sa kamar yanda na saba ko kuma na siyo muku raguna dai-dai ke da kanwarki yara kuma a basu biyu.’
‘Haba dai, ai sa ya fi auki. Idan ka siyo mana sa daya da rago ya ishemu gaba daya idan muka hadu muka soya sai a raba. Sai dai idan ita Aishan ta fi son rago sai a bata nata.’
‘A’a na san bata da matsala, bari dai naje kasuwar naji farashin dabbobin tukunna sai ayi wanda ya samu.’
Suka gama hirarrakinsu daga baya ta barshi a nan ta shiga kicin dora abincin dare.
……..
Sallah saura sati biyu Aisha ta tashi da wani zazzabi, da kanshi ya kaita asibiti. Aka yi mata duk wasu gwaje-gwaje da suka dace, aka tabbatar bata dauke da juna biyu, sai dai malaria don haka aka rubuta mata magunguna suka kamo hanya.
Har suka zo gida yana tsokanarta a kan shi ya fara murna har ya gama shawara idan mace ta haifa Aisha zai mayar idan kuma namiji ne Muhammad. Haka suka tsaya a chemist aka yi mata allurai sannan suka dawo gidan.
Kwana biyu ta fara warwarewa, da daddare suna zaune a falo ya mike kafafunsa ta tada kai da cinyoyinsa ta kwanta suna hira kuma suna kallon TV.
Yace
‘Wai Sallah ta kusa ke ko labarin kayan Sallah ba kya yi balle na abun layya.’
Tayi dariya tace
‘Wai da yake ba ni zanyi ba, kuma na san mai yi yana sane da lokacin.’
‘Lallai ne baki da matsala. To akwai leshina a wajen yayarki, gobe sai ki shiga ki zabi daya. Kin san tana sayar da kayan sawa shi yasa kawai nake sayen kayan sallar a wajenta.’
Ranta ya sosu, Yaya za ayi yace matarsa ce zata saya mata kayan Sallah ko an gaya masa ita babu masu sayar da kayan a danginta. Bata son ta ja maganar yaga kamar ta damu; kuma da yake tana da ragowar kaya a akwatin lefenta sai abun bai dameta ba sannan kuma akwai leshi da suka siya ita da ‘yan gidansu wanda daga Switzerland suka tura kudi aka siyo musu don nata ma yana wajen tele inda Zahida ta kai musu dinki, don haka tace
‘Ka gani ni dai ina fama da kaina gobe ban san yanda zan tashi ba, idan ka je kawai ka zabo min wanda ya burgeka.’