Sashe 79
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
‘To duka bayanan nata wallahi ba ganewa nayi ba saboda tana cikin damuwa, kamar dai tace jiya da safe ya fita shine aka kirawo ta akace kamar sun ci wani abu suna asibiti. To tace kai kadai ka zo ka ganshi kuma baka bata wani bayani ba, shi yasa ma take cikin damuwa.’
Ya jijjaga kai.
Nan yayi mata bayanin ainahin abinda ya faru sannan ya kara da
‘Saboda bata son bacin ran shi tana kallo tun yana SS 2 yake shaye-shaye gashi yanzu har ya zama addicted, jiyan da ba dan Allah ya sa da kwanansu a gaba ba da sai dai mu dauki gawarsu. Yau da na fita daga nan kuma makarantarsu naje ashe ma shi ba karatun yake yi ba, tunda jarrabawar da yace mata sun gama ta bashi kudin party harda mota ya tafi an ce guda biyu kawai ya rubuta a cikin paper goma sha daya; kin ga babu maganar karatu ko.’
Kallonsa kawai take tana mamaki tana jijjiga kai, tace
‘Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun! Ita kuwa Zahra garin yaya tayi haka?’
Nan ta gaya masa yanda suka yi da Zahran a kan maganar zargin da takeyi, sannan ta sake bashi hakuri.
Nan ya tashi yayi mata jagora har dakin Saddikun, ta dai samu natsuwa yanda taga Saddikun tunda a hayyacinsa yake har hira ma suka yi kuma ya gaya mata babu inda yake masa ciwo don likitan ma yace da safe zasu sallameshi.
Bayan sun fito ne Abban yake gaya mata ya riga ya sami rehabilitation center da zai kai Saddikun, wanda a yanda ya tsara daga nan asibitin kai tsaye center din zasu wuce.
Tace hakan yayi domin itama tana so taga Saddikun ya zama mutum, sai dai ta roki Abban a kan ya taimaka ya bari Zahra ta ga Saddikun kafin a tafi da shi rehabilitation center din tunda ya ce da ita wata shida zai yi a can kuma shi kadai zai dinga zuwa yana ganinsa. Yayi mata alkawarin gobe da safe zai kawo Zahran ta ganshi inda daga nan zai daukeshi su wuce.
Sukayi sallama ta kama hanyar gida shi kuma ya koma office.
__
Kai tsaye daga asibiti gidan Zahra ta koma saboda yanda take cike da takaicin abun da Zahran tayi. Bayan ta sanar da ita Saddikun yana nan kamar ma lafiyarsa kalau sai kuma ta hau ta da fada.
Sai da tayi mai isarta sannan tace
‘Shima kansa Abban haushin ki yake ji saboda yanda kika tsaya kika bari Saddiku ya lalace kuma kika dinga hanashi yayi masa fada, shi ya sa kika ga yayi banza dake. Don haka idan ya dawo ki lallaba ki bashi hakuri tunda gaskiya dai da laifinki don shi da kansa yace ke kika bashi kudin party din. Ki samu ki bashi hakuri don gaskiya yayi fushi sosai, kuma idan an kai Saddikun rehabilitation center ki kawar da idonki a samu ya sami lafiya tunda dai kin tabbatar ubansa ba zai cutar da shi ba.’
‘Wallahi Yaya wannan wulakancin da yake yawan yi min tunzura shi matarsa take tunda da ai ba haka yake ba.’
‘Ba zamu iya gane hakan ba sai lokacin da yayi fushi da ke ba tare da wani dalili ba don yanzu kam kin yi abun fushi. Kawai ki gyara kuma ki bashi hakuri.'
Ta riga ta san daman haka Yaya zata ce don haka tayi shiru.
Daga baya YayaMurjan tayi mata sallama ta tafi.
__
Duk yanda yake jin haushin Zahra ya san dole yau ya ganta tunda kwananta ne. Sai da ya gama duk abinda zai yi ya ci abincin dare a gidan Aisha sannan wajen tara da rabi ya shiga gidan Zahra.
Duk yanda ya so ya kyaleta bata bashi dama ba saboda yanda ta sameshi a daki ta saka shi a gaba da kuka tana bashi hakuri. Ta bashi tausayi sannan kuma baya son ganinta a damuwa don haka da wuri ya nuna mata ya hakura. Ya dan ci abincin daren da ta dafa duk da a koshe yake. Haka suka kwana babu yabo babu fallasa.
Gari yana wayewa bayan sun gama cin abinci yara sun tafi makaranta ya daukesu ita da Yusra suka wuce asibitin.
Sai a lokacin Zahra ta sami natlsuwa da taga Saddikun, suka dan taba hira har ta tambayeshi ina motarta. Sai a lokacin ya tuna da motar inda yace mata bai sani ba sai dai ko ta tambayi Abba don wayarsa ma Abban aka bawa kuma har yanzu Abban bai bashi wayar ba. A halin da ake ciki ba zata iya maganar motar ba don lallabawa takeyi ta kankarowa kanta mutunci don haka tayi shiru.
Basu dade ba Yaya Bello ya iso ya samesu, suka gaisa da Zahran sannan ya jajanta mata jikin Saddikun. Shi da Abba suka shiga ofishin likitan, sai da suka fi minti talatin suna tattaunawa sannan suka fito; domin likitan ne ya hadasu da masu rehabilitation center din. Suna fitowa aka rubutawa Saddiku sallama.
Yusra ta taya Muhammadu suka kwaso kwanukan abinci wadanda duk na Aisha ne suka zuba a motar Malam Ali da yake jiransu, Abba ya bawa Muhammadu kudin mota yace ya wuce gida. Har ya kama hanya Yusra tace masa
‘Yaya Muhammadu kwanukan ba na gidanku bane ko a kawo daga baya.’
Yace
‘Ba na gidanmu bane na gidanku ne fa.’
Kafin suce wani abu Abba yace
‘Na Antinki ne idan kun je gida Malam Ali zai kai mata.’
Sai da Zahra tayi da gaske sannan ta danne damuwarta kada Abban ya ga sauyi a fuskarta; wato mutan gidan Bello da Aisha sun fita mahimmanci a rayuwar yaranta shi yasa ya danka musu Saddikun ya hanata ganinsa bayan babu wanda ya haifar mata yaron. Lallai!
Daga gefe guda likitan ne tsaye da Yaya Bello da Abban suna magana, bayan Saddikun ya zuba kayan hannunsa a motar Malam Ali ya karasa ya cewa Abban ya fito.
Abban ya dubeshi yace
‘Kaje ka yiwa Mommynka Sallama daga nan zamu wuce da kai makaranta ni da Yaya zamu kai ka.’
Ya amsa ya wuce wajen su Mommy din.
Tayi zaton da ita za aje taga makarantar amma Abban yace ba haka za ayi ba su wuce ita da Yusra Malam Ali ya mayar da su gida, shi da Yaya Bello zasu kai Saddikun.
Shi kanshi Abban sai da ya kula da yanda ta fusata, ta shige motar ta rufe domin Yaya Bello ma da ya taho yayi musu sallama sai hakura yayi ya tsaya wajen Abban yayinda Malam Ali yaja motar.
Abba yaja motar shi da Yaya Bellon suka nufi kan titin gwarzo road inda daga nan ne zasu kara neman kwatancen makarantar.
Har suka isa gida Zahra ba tayi magana ba saboda yanda zuciyarta take tafasa; wato yanzu kenan Bello shine zai dinga tsarawa yaranta rayuwa saboda sun mayar da ita ‘yar iska shi da dan uwansa. Za a kai mata yaro makaranta amma bata ma isa a kaita ta ga wajen ba kenan idan wani abu ya sami Abban Bello ne kawai ya san inda Saddiku yake.
Gaskiya ba zata jure ba, wulakancin ya isa. Bata san me ta tsarewa Aisha da Bello ba suka janye mata hankalin miji, amman dole ta dauki mataki.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
39
Sai da aka bawa su Abban Sadik takardu suka cike sannan aka nuna musu dakin Saddiku, bayan nan kuma aka yi musu bayani cewa ba zasu ziyarceshi ba sai bayan sati biyu. Babu waya a hannunsa don haka aka basu lambar wayar da za a iya kira ayi magana da shi. Mutum biyu kawai ake so wadanda sune zasu dinga ziyartar sa don haka Abba ya sa sunanshi da na Yaya Bello a kan su kadai ne za a dinga bari suna ganinsa. Sukayi masa sallama suka taho zuciyar Abban cike da damuwa yana fatan Allah ya sa kafin ya dawo Saddikun ya fara samun natsuwa.
Haka suka fito suka bar Saddikun shima yana matse hawaye yayinda kwakwalwarsa take kokarin gamsar da shi cewa iyayen nasa basu daina son sa ba.
__
Tunda aka kai Saddiku makarantar nan Zahra ta kasa nutsuwa. A da idan tana cikin damuwa Abban ne yake kwantar mata da hankali, yanzu kuma da take cikin tsananin bukatar hakan yayi burus da ita. Bai taba hanata kwananta ba amma dai babu wata hira da take shiga tsakaninsu; ita tana jin haushinsa kuma tana fushi yayinda shi yake ganin shine ya kamata yayi fushi ba ita ba. A halin yanzu ma kwata-kwata baya jin Zahra a ransa kamar yanda yake jinta a da.
Kusan kwana goma kenan da kai Saddikun amma duk ta rame tana neman fita hayyacinta saboda damuwa da rashin bacci, gashi kullum ta dan sami baccin sai ta yi mafarkin Saddikun a wani yanayi mara dadi.
Ranar asabar ce don haka yara sun tafi tahfiz, don haka ta koma dakinta ta kwanta tunda maigidan ba awajenta yake ba. Tana kwanciya bacci ya kwasheta.
Yana zaune a wani waje mai kyau da haske, shimfidun wajen farare ne tas haka ma kujerun. Yana zaune a kan kujera cikin shigar fararen kaya, sai dai abinda ya firgita ta shine yanda duk kyan wajen da kuma kyan shigar Saddikun kuka kawai yake faman yi yana matse hawaye. Magana take yi masa iya karfinta amma ko jinta bayayi, kuka yake mai ban tausayi harda shessheka.
Haka ta farka a firgice.
Irin wadannan mafarkan da takeyi su suke daga mata hankali; ta san dai kuka ba alkhairi bane to me yasa take ganin Saddiku yana kuka?
A hankali ta sauko daga kan gadon, har zata tashi sai kuma ta koma ta zauna. Ta mika hannu ta dauko wayarta a kan durowar gefen gado ta lalubo lambar Abban Saddiku ta buga masa; bayan ya dauka ta sanar da shi tana so taje gidan Yaya Murja. Ba tare da bata lokaci ba ya bata dama tunda Malam Ali yana nan.
Hijab kawai ta saka saboda bata ma da kuzarin canza kaya, ba tare da bata lokaci ba Malam Ali ya dauketa suka fice.
Ya jijjaga kai.
Nan yayi mata bayanin ainahin abinda ya faru sannan ya kara da
‘Saboda bata son bacin ran shi tana kallo tun yana SS 2 yake shaye-shaye gashi yanzu har ya zama addicted, jiyan da ba dan Allah ya sa da kwanansu a gaba ba da sai dai mu dauki gawarsu. Yau da na fita daga nan kuma makarantarsu naje ashe ma shi ba karatun yake yi ba, tunda jarrabawar da yace mata sun gama ta bashi kudin party harda mota ya tafi an ce guda biyu kawai ya rubuta a cikin paper goma sha daya; kin ga babu maganar karatu ko.’
Kallonsa kawai take tana mamaki tana jijjiga kai, tace
‘Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun! Ita kuwa Zahra garin yaya tayi haka?’
Nan ta gaya masa yanda suka yi da Zahran a kan maganar zargin da takeyi, sannan ta sake bashi hakuri.
Nan ya tashi yayi mata jagora har dakin Saddikun, ta dai samu natsuwa yanda taga Saddikun tunda a hayyacinsa yake har hira ma suka yi kuma ya gaya mata babu inda yake masa ciwo don likitan ma yace da safe zasu sallameshi.
Bayan sun fito ne Abban yake gaya mata ya riga ya sami rehabilitation center da zai kai Saddikun, wanda a yanda ya tsara daga nan asibitin kai tsaye center din zasu wuce.
Tace hakan yayi domin itama tana so taga Saddikun ya zama mutum, sai dai ta roki Abban a kan ya taimaka ya bari Zahra ta ga Saddikun kafin a tafi da shi rehabilitation center din tunda ya ce da ita wata shida zai yi a can kuma shi kadai zai dinga zuwa yana ganinsa. Yayi mata alkawarin gobe da safe zai kawo Zahran ta ganshi inda daga nan zai daukeshi su wuce.
Sukayi sallama ta kama hanyar gida shi kuma ya koma office.
__
Kai tsaye daga asibiti gidan Zahra ta koma saboda yanda take cike da takaicin abun da Zahran tayi. Bayan ta sanar da ita Saddikun yana nan kamar ma lafiyarsa kalau sai kuma ta hau ta da fada.
Sai da tayi mai isarta sannan tace
‘Shima kansa Abban haushin ki yake ji saboda yanda kika tsaya kika bari Saddiku ya lalace kuma kika dinga hanashi yayi masa fada, shi ya sa kika ga yayi banza dake. Don haka idan ya dawo ki lallaba ki bashi hakuri tunda gaskiya dai da laifinki don shi da kansa yace ke kika bashi kudin party din. Ki samu ki bashi hakuri don gaskiya yayi fushi sosai, kuma idan an kai Saddikun rehabilitation center ki kawar da idonki a samu ya sami lafiya tunda dai kin tabbatar ubansa ba zai cutar da shi ba.’
‘Wallahi Yaya wannan wulakancin da yake yawan yi min tunzura shi matarsa take tunda da ai ba haka yake ba.’
‘Ba zamu iya gane hakan ba sai lokacin da yayi fushi da ke ba tare da wani dalili ba don yanzu kam kin yi abun fushi. Kawai ki gyara kuma ki bashi hakuri.'
Ta riga ta san daman haka Yaya zata ce don haka tayi shiru.
Daga baya YayaMurjan tayi mata sallama ta tafi.
__
Duk yanda yake jin haushin Zahra ya san dole yau ya ganta tunda kwananta ne. Sai da ya gama duk abinda zai yi ya ci abincin dare a gidan Aisha sannan wajen tara da rabi ya shiga gidan Zahra.
Duk yanda ya so ya kyaleta bata bashi dama ba saboda yanda ta sameshi a daki ta saka shi a gaba da kuka tana bashi hakuri. Ta bashi tausayi sannan kuma baya son ganinta a damuwa don haka da wuri ya nuna mata ya hakura. Ya dan ci abincin daren da ta dafa duk da a koshe yake. Haka suka kwana babu yabo babu fallasa.
Gari yana wayewa bayan sun gama cin abinci yara sun tafi makaranta ya daukesu ita da Yusra suka wuce asibitin.
Sai a lokacin Zahra ta sami natlsuwa da taga Saddikun, suka dan taba hira har ta tambayeshi ina motarta. Sai a lokacin ya tuna da motar inda yace mata bai sani ba sai dai ko ta tambayi Abba don wayarsa ma Abban aka bawa kuma har yanzu Abban bai bashi wayar ba. A halin da ake ciki ba zata iya maganar motar ba don lallabawa takeyi ta kankarowa kanta mutunci don haka tayi shiru.
Basu dade ba Yaya Bello ya iso ya samesu, suka gaisa da Zahran sannan ya jajanta mata jikin Saddikun. Shi da Abba suka shiga ofishin likitan, sai da suka fi minti talatin suna tattaunawa sannan suka fito; domin likitan ne ya hadasu da masu rehabilitation center din. Suna fitowa aka rubutawa Saddiku sallama.
Yusra ta taya Muhammadu suka kwaso kwanukan abinci wadanda duk na Aisha ne suka zuba a motar Malam Ali da yake jiransu, Abba ya bawa Muhammadu kudin mota yace ya wuce gida. Har ya kama hanya Yusra tace masa
‘Yaya Muhammadu kwanukan ba na gidanku bane ko a kawo daga baya.’
Yace
‘Ba na gidanmu bane na gidanku ne fa.’
Kafin suce wani abu Abba yace
‘Na Antinki ne idan kun je gida Malam Ali zai kai mata.’
Sai da Zahra tayi da gaske sannan ta danne damuwarta kada Abban ya ga sauyi a fuskarta; wato mutan gidan Bello da Aisha sun fita mahimmanci a rayuwar yaranta shi yasa ya danka musu Saddikun ya hanata ganinsa bayan babu wanda ya haifar mata yaron. Lallai!
Daga gefe guda likitan ne tsaye da Yaya Bello da Abban suna magana, bayan Saddikun ya zuba kayan hannunsa a motar Malam Ali ya karasa ya cewa Abban ya fito.
Abban ya dubeshi yace
‘Kaje ka yiwa Mommynka Sallama daga nan zamu wuce da kai makaranta ni da Yaya zamu kai ka.’
Ya amsa ya wuce wajen su Mommy din.
Tayi zaton da ita za aje taga makarantar amma Abban yace ba haka za ayi ba su wuce ita da Yusra Malam Ali ya mayar da su gida, shi da Yaya Bello zasu kai Saddikun.
Shi kanshi Abban sai da ya kula da yanda ta fusata, ta shige motar ta rufe domin Yaya Bello ma da ya taho yayi musu sallama sai hakura yayi ya tsaya wajen Abban yayinda Malam Ali yaja motar.
Abba yaja motar shi da Yaya Bellon suka nufi kan titin gwarzo road inda daga nan ne zasu kara neman kwatancen makarantar.
Har suka isa gida Zahra ba tayi magana ba saboda yanda zuciyarta take tafasa; wato yanzu kenan Bello shine zai dinga tsarawa yaranta rayuwa saboda sun mayar da ita ‘yar iska shi da dan uwansa. Za a kai mata yaro makaranta amma bata ma isa a kaita ta ga wajen ba kenan idan wani abu ya sami Abban Bello ne kawai ya san inda Saddiku yake.
Gaskiya ba zata jure ba, wulakancin ya isa. Bata san me ta tsarewa Aisha da Bello ba suka janye mata hankalin miji, amman dole ta dauki mataki.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
39
Sai da aka bawa su Abban Sadik takardu suka cike sannan aka nuna musu dakin Saddiku, bayan nan kuma aka yi musu bayani cewa ba zasu ziyarceshi ba sai bayan sati biyu. Babu waya a hannunsa don haka aka basu lambar wayar da za a iya kira ayi magana da shi. Mutum biyu kawai ake so wadanda sune zasu dinga ziyartar sa don haka Abba ya sa sunanshi da na Yaya Bello a kan su kadai ne za a dinga bari suna ganinsa. Sukayi masa sallama suka taho zuciyar Abban cike da damuwa yana fatan Allah ya sa kafin ya dawo Saddikun ya fara samun natsuwa.
Haka suka fito suka bar Saddikun shima yana matse hawaye yayinda kwakwalwarsa take kokarin gamsar da shi cewa iyayen nasa basu daina son sa ba.
__
Tunda aka kai Saddiku makarantar nan Zahra ta kasa nutsuwa. A da idan tana cikin damuwa Abban ne yake kwantar mata da hankali, yanzu kuma da take cikin tsananin bukatar hakan yayi burus da ita. Bai taba hanata kwananta ba amma dai babu wata hira da take shiga tsakaninsu; ita tana jin haushinsa kuma tana fushi yayinda shi yake ganin shine ya kamata yayi fushi ba ita ba. A halin yanzu ma kwata-kwata baya jin Zahra a ransa kamar yanda yake jinta a da.
Kusan kwana goma kenan da kai Saddikun amma duk ta rame tana neman fita hayyacinta saboda damuwa da rashin bacci, gashi kullum ta dan sami baccin sai ta yi mafarkin Saddikun a wani yanayi mara dadi.
Ranar asabar ce don haka yara sun tafi tahfiz, don haka ta koma dakinta ta kwanta tunda maigidan ba awajenta yake ba. Tana kwanciya bacci ya kwasheta.
Yana zaune a wani waje mai kyau da haske, shimfidun wajen farare ne tas haka ma kujerun. Yana zaune a kan kujera cikin shigar fararen kaya, sai dai abinda ya firgita ta shine yanda duk kyan wajen da kuma kyan shigar Saddikun kuka kawai yake faman yi yana matse hawaye. Magana take yi masa iya karfinta amma ko jinta bayayi, kuka yake mai ban tausayi harda shessheka.
Haka ta farka a firgice.
Irin wadannan mafarkan da takeyi su suke daga mata hankali; ta san dai kuka ba alkhairi bane to me yasa take ganin Saddiku yana kuka?
A hankali ta sauko daga kan gadon, har zata tashi sai kuma ta koma ta zauna. Ta mika hannu ta dauko wayarta a kan durowar gefen gado ta lalubo lambar Abban Saddiku ta buga masa; bayan ya dauka ta sanar da shi tana so taje gidan Yaya Murja. Ba tare da bata lokaci ba ya bata dama tunda Malam Ali yana nan.
Hijab kawai ta saka saboda bata ma da kuzarin canza kaya, ba tare da bata lokaci ba Malam Ali ya dauketa suka fice.