Sashe 41
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Motsi ta sake ji kamar an tsallake kafafunta sai dai bata ga wanda ya tsallake din ba, kafin tayi wani abu taji kamar an cafke cibiyarta wanda ya sa mararta tayi wani irin suka gumi ya karyo mata. Ko minti daya ba ayi ba taji an finciki cibiyarta kwatankwacin yanda ake balle murfin kwalabar lemo; da hanzari ta kai hannu ta dafe cibiyarta tana fadin
‘La ilaha illallah, wayyo!’
Gumi ya cigaba da karyo mata saboda yanda mararta take kara kartawa da ciwo. Ta dan muskuta ta gyara zama ta cigaba da ambaton
‘hasbunallahu wa ni’imal wakil’.
A hankali ta dan fara samun natsuwa, dakin ya dawo dai-dai sai dai mararta da bata daina murdawa ba.
Ta tuna sallar dare ma ta tashi yi don haka a hankali ta zuro kafafunta daga kan gadon don taje bandaki tayiwo alwala.
Yanda taji danshi a jikinta ta tabbatar fitsari tayi ko kuma jini ne yake binta, cikin hanzari ta karasa bandaki. Tana kwabe kayanta taga jini ne yake binta gashi mararta tana kara kartawa. Da kyar ta daure ta wanke jikinta sannan ta lallabo ta dawo dakin ta kwanta. Ta duba wayar tata taga karfe uku da minti biyar na dare, ta gyara kwanciyarta ta kashe fitilar wayar don yanzu babu wanda zata iya tashi daga barci.
Haka ta kwanta tanata juyi tana ambaton Allah ga mararta tana ciwo har akayi kiran asuba. Ta lallaba ta hada ruwan zafi tayi wanka sannan ta hada shayi. Ta dawo ta zauna a kan dining table ta saka kofin shayin a gaba tana kallonsa; karo na biyu kenan tana barar da ciki a gidan nan, to me yake faruwa? Ta san dai bawa baya wuce kaddararsa amma abun ya fara bata tsoro musamman na jiya da daddare da yayi kama da zuwa akayi musamman aka cire cikin aka tafi.
Kusan shekaru hudu kenan da aurensu amma bazata iya cewa sunyi wata shida cikin nutsuwa ba, fitna daga wannan sai wannan.
Yanzu gashi sati wajen uku kenan an shiga na hudu rabon da Yusuf yazo inda take, sai dai kawai waya. Wayar ma yanzu ba kullum yake kira ba.
Saida shayin nan ya fara hucewa sannan ta dauka ta sha. Ta sami Panadol ta sha saboda yanda mararta take ciwo sannan ta koma ta kwanta a kan doguwar kujera.
Sai wajen bakwai da rabi na safe sannan ta kirawo Yaya Zuwaira ta sanar da ita halin da take ciki, wajen takwas da rabi ta iso gidan suka kama hanyar asibiti.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
24
Suna zuwa asibiti suka wuce emergency, nan take likita yace suyi scanning. Bayan sun kawo sakamakon likita yayi musu bayani cewa cikin ya fita amma za a yi mata wankin ciki. A nan suka sami waje Zuwaira tace Aishan ta zauna zata je ta biya kudin ta dawo.
Bayan ta dawo kafin su koma waje likita ta dubeta tace
‘Wai kin gaya masa kuwa?’
Ta kau da kai
‘To me zan ce masa baya iya zuwa kusa dani, ni ban gaya masa ba.’
‘To bari na dawo sai na gaya masa, ai gara ya sani ko don ya san cikin jikinki ya bare.’
Ta wuce ta barta a nan.
Bayan ta biya ta dawo aka shiga da Aisha dakin wankin cikin, ita kuma Zuwaira ta zauna tana jiransu.
---------
Yana hanyar tafiya office wayarsa tayi kara, yana dubawa yaga Zuwaira. Da rawar jiki ya dauki wayar wanda shi kansa bai san dalilin hakan ba. Bayan sun gaisa ta sanar da shi Aisha tayi bari suna Asibitin Nassarawa.
Nan take ya juya kan motar ya kama hanyar asibitin.
Yana shiga asibitin yayi tambaya aka nuna masa inda suke, kai tsaye ya wuce.
Kafin ya karasa wajen ya hango Zuwaira a zaune a kan kujera tana jira a fito da Aisha daga wankin cikin.
Yana dab da karasawa nurse ta bude kofar dakin wankin cikin Aisha ta fito, nurse din tana mata sannu tana kokarin dafa ta. Zuwaira ta mike da hanzari ta nufota daidai lokacin da Abban ya karaso kusa da ita.
‘Aisha.’
Ya kirawo sunanta, ta kalleshi suka hada ido.
Ta dauke kanta tana kokarin mikewa sosai saboda yanda take jin jikinta babu kwari.
Kafin ta karasa mikewa ya tareta, gaba daya ya rungumeta yana mayar da numfashi. Suka dauki kamar minti daya bashi da niyyar sakinta. Yaya Zuwaira tana tsaye tana kallon ikon Allah ita kuwa nurse tuni ta wuce ta basu waje.
Bashi da niyyar sakinta don haka ta dan fara mutsu-mutsu tana son ta zare jikinta.
‘Akwai mutane fa.’
Ta rada masa.
Ya saketa, sai dai yana rike da hannunta yana kallon fuskarta. Cikin damuwa da tausayawa yace
‘Sannu.’
Ta daga masa kai.
Suka karasa suka zauna a kan kujera suna jiran a rubuta mata sallama.
Tana ta faman gyara zama don haka ya matsa ya janyota jikinsa ta kwanta.
Suna nan zaune likita ya fito daga dakin wankin cikin ya shige ofishinsa. Zuwaira ce ta mike ta bishi don shi baya jin zai iya barin Aisha a nan ita kadai ba.
Jimawa kadan Zuwaira ta fito rike da takardu, ta mikawa Abban takardun tace
‘Ga wanna magunguna aka rubuta, likitan yace zamu iya tafiya. Idan taci abinci ta huta zata ji kwari a jikinta, idan akwai wata matsala yace sai a dawo.’
Duk da tace masa zata iya tashi amma sai da ya riketa ya kamata sannan ta tashi, yana rike da ita har suka zo wajen motarsa. Sai da ya kwantar da kujerar gaban motarsa sannan ya sa Aisha ta dan kashingida. Ya rufe kofar motar ya matso kusa da Zuwaira wadda take tsaye jikin motar da direbanta ya kawota. Yace
‘Ina ga mu tafi a motata, in ya so sai direban ya sameki a can ko.’
Saboda haka gaba daya suka shiga motar Abban suka nufi gidan Aisha.
Sai da ya tsaya a super market ya siyowa Aisha kaji da yoghurt mai sanyi kuma ya hada da apple ya zuba a mota sannan suka wuce gidan.
A bakin gate yayi parking, kafin ya zagayo ya budewa Aisha kofa ta bude ta fito. Ya fito da ledojin da yayi sayayya ya mikawa Zuwaira yana fadin
‘Bari na rakaku ciki sai na fito na wuce office don ko isa ban yi ba na sami kiranki.’
Yana rike da Aishan suka nufo gidan, tunda ya bude gate din ya sako kafarsa cikin gidan ya fara jin wannan warin da yake firgita shi. Daga hannunsa da take rike da shi ta fuskanci abinda yake faruwa da shi, tana kokarin duba fuskarsa ya zare hannun nasa daga cikin nata.
Suna daf da taka barandar falon ya ja baya, yana juyowa ya fuskanci Zuwaira wadda take biye da su a baya wadda itama sauyawar da fuskarshi tayi yayi matukar bata mamaki. Kafin tace wani abu yace
‘Yauwa ku shiga, bari nayi sauri naje sai na dawo.’
Bata yi tsammanin ya ji a dawo lafiyar da takeyi masa ba don kamar a guje ya fice har yana yin tuntube.
Suka kalli juna ita da Aisha, ta matsa kusa da Aishan tana mamaki. Aisha tayi murmushi tace
‘Kin gani ko? Wallahi da ya shigo yake rudewa haka.’
Suka karasa cikin gidan.
Kafin wani lokaci Zuwaira ta gyarata ta hada mata abinci, bayan taci abinci ta sha magani ta kwanta a dakin baki sai bacci.
Kafin azahar dangi duk sun hadu a gidan don wannan karon Hajiya ma cewa tayi sai ta zo, don haka gaba daya suka taho da yaran da Anti Uwani. Sai da yamma suka tafi suka barta da Amira bayan da suka tabbatar ta wattsake.
-------
Kafin ya fita daga gidan har kansa ya fara sarawa, yana fita daga gate din ya kama hanyar ya nufi gidan Zahra.
Sai da ya kusa zuwa gate sannan ya kalli hannunsa ya ga mukullin motarsa, a take ya tuna da motarsa kuma ya tuna office ya kamata ya tafi.
A hankali ya janyo kafarsa ya dawo ya shiga motarsa ya kama hanyar office. Zuciyarsa tana begen Aisha amma ya kasa shiga inda take. Ya tuno kamar dai lokacin da suna asibiti bai ji wani wari ba, shi ya manta ma da wannan matsalar gaba daya.
Abun yana ransa kullum yana cewa zai nemi taimako ko addu’a a yi masa amma sai ya dinga mantawa, wasu lokutan ma yana rasa abinda ya sa baya magana a kan matsalar nan. Sau biyu yana zuwa gidan Yaya Bello don ya sanar da shi matsalar amma idan yaje sai suyita wasu hirarrakin gaba daya ma ya manta da abinda ya kaishi.
Yana tukin ma abinda yake ransa shine ya wuce wajen wani malami da ya sani mai Islamic chemist yaji ko zai sami wani taimako. Kafin ya gama tsara abinda zai gayawa Malam din kawai ya tsinci kansa a farfajiyar office anata faman yi masa sannu da zuwa.
Haka ya hakura ya shiga office din da niyyar idan ya tashi daga aiki ya biya ta wajen Malam din.
__
Tun ranar da Balele ya fara zuwa aiki suka fara fita da Zahra, da yake ta maida hankali kuma hawa motar tana ranta kafin sati hannunta ya fada. Tunda kuwa taga ta fara iya fita ita kadai ta bawa Balele tata motar ta karbi Fijo din da Malam Sule ya bar masa, don tana ganin ko Yaya dai wannan din tafi wadda Abban ya bata tsada.
Tunda motar tazo hannu kuma sai ta fara yi masa tunin yayi mata alkawarin kujerar Umra, wadda ta ce masa ta azumi take so kuma shi ma goman karshe. Ya tabbatar mata kujerarta tana nan in Sha Allahu da lokacin yayi za a bata.
………
Tunda Balele ya fara aiki Sadik ya makale masa saida ya koyi mota, dama tun a wajen Malam Sule ya so koya Abbanshi ya hana.
Jarrabawarsa ta WAEC ta kusan fitowa, shi da Mommy sun hadu sun saka Abban a gaba a kan lallai sai an kai shi Dubai zai yi degree. Da fari Abban ya ki amincewa amma daga baya ya amsa don haka sakamakon WAEC din kawai ake jira.
‘La ilaha illallah, wayyo!’
Gumi ya cigaba da karyo mata saboda yanda mararta take kara kartawa da ciwo. Ta dan muskuta ta gyara zama ta cigaba da ambaton
‘hasbunallahu wa ni’imal wakil’.
A hankali ta dan fara samun natsuwa, dakin ya dawo dai-dai sai dai mararta da bata daina murdawa ba.
Ta tuna sallar dare ma ta tashi yi don haka a hankali ta zuro kafafunta daga kan gadon don taje bandaki tayiwo alwala.
Yanda taji danshi a jikinta ta tabbatar fitsari tayi ko kuma jini ne yake binta, cikin hanzari ta karasa bandaki. Tana kwabe kayanta taga jini ne yake binta gashi mararta tana kara kartawa. Da kyar ta daure ta wanke jikinta sannan ta lallabo ta dawo dakin ta kwanta. Ta duba wayar tata taga karfe uku da minti biyar na dare, ta gyara kwanciyarta ta kashe fitilar wayar don yanzu babu wanda zata iya tashi daga barci.
Haka ta kwanta tanata juyi tana ambaton Allah ga mararta tana ciwo har akayi kiran asuba. Ta lallaba ta hada ruwan zafi tayi wanka sannan ta hada shayi. Ta dawo ta zauna a kan dining table ta saka kofin shayin a gaba tana kallonsa; karo na biyu kenan tana barar da ciki a gidan nan, to me yake faruwa? Ta san dai bawa baya wuce kaddararsa amma abun ya fara bata tsoro musamman na jiya da daddare da yayi kama da zuwa akayi musamman aka cire cikin aka tafi.
Kusan shekaru hudu kenan da aurensu amma bazata iya cewa sunyi wata shida cikin nutsuwa ba, fitna daga wannan sai wannan.
Yanzu gashi sati wajen uku kenan an shiga na hudu rabon da Yusuf yazo inda take, sai dai kawai waya. Wayar ma yanzu ba kullum yake kira ba.
Saida shayin nan ya fara hucewa sannan ta dauka ta sha. Ta sami Panadol ta sha saboda yanda mararta take ciwo sannan ta koma ta kwanta a kan doguwar kujera.
Sai wajen bakwai da rabi na safe sannan ta kirawo Yaya Zuwaira ta sanar da ita halin da take ciki, wajen takwas da rabi ta iso gidan suka kama hanyar asibiti.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
24
Suna zuwa asibiti suka wuce emergency, nan take likita yace suyi scanning. Bayan sun kawo sakamakon likita yayi musu bayani cewa cikin ya fita amma za a yi mata wankin ciki. A nan suka sami waje Zuwaira tace Aishan ta zauna zata je ta biya kudin ta dawo.
Bayan ta dawo kafin su koma waje likita ta dubeta tace
‘Wai kin gaya masa kuwa?’
Ta kau da kai
‘To me zan ce masa baya iya zuwa kusa dani, ni ban gaya masa ba.’
‘To bari na dawo sai na gaya masa, ai gara ya sani ko don ya san cikin jikinki ya bare.’
Ta wuce ta barta a nan.
Bayan ta biya ta dawo aka shiga da Aisha dakin wankin cikin, ita kuma Zuwaira ta zauna tana jiransu.
---------
Yana hanyar tafiya office wayarsa tayi kara, yana dubawa yaga Zuwaira. Da rawar jiki ya dauki wayar wanda shi kansa bai san dalilin hakan ba. Bayan sun gaisa ta sanar da shi Aisha tayi bari suna Asibitin Nassarawa.
Nan take ya juya kan motar ya kama hanyar asibitin.
Yana shiga asibitin yayi tambaya aka nuna masa inda suke, kai tsaye ya wuce.
Kafin ya karasa wajen ya hango Zuwaira a zaune a kan kujera tana jira a fito da Aisha daga wankin cikin.
Yana dab da karasawa nurse ta bude kofar dakin wankin cikin Aisha ta fito, nurse din tana mata sannu tana kokarin dafa ta. Zuwaira ta mike da hanzari ta nufota daidai lokacin da Abban ya karaso kusa da ita.
‘Aisha.’
Ya kirawo sunanta, ta kalleshi suka hada ido.
Ta dauke kanta tana kokarin mikewa sosai saboda yanda take jin jikinta babu kwari.
Kafin ta karasa mikewa ya tareta, gaba daya ya rungumeta yana mayar da numfashi. Suka dauki kamar minti daya bashi da niyyar sakinta. Yaya Zuwaira tana tsaye tana kallon ikon Allah ita kuwa nurse tuni ta wuce ta basu waje.
Bashi da niyyar sakinta don haka ta dan fara mutsu-mutsu tana son ta zare jikinta.
‘Akwai mutane fa.’
Ta rada masa.
Ya saketa, sai dai yana rike da hannunta yana kallon fuskarta. Cikin damuwa da tausayawa yace
‘Sannu.’
Ta daga masa kai.
Suka karasa suka zauna a kan kujera suna jiran a rubuta mata sallama.
Tana ta faman gyara zama don haka ya matsa ya janyota jikinsa ta kwanta.
Suna nan zaune likita ya fito daga dakin wankin cikin ya shige ofishinsa. Zuwaira ce ta mike ta bishi don shi baya jin zai iya barin Aisha a nan ita kadai ba.
Jimawa kadan Zuwaira ta fito rike da takardu, ta mikawa Abban takardun tace
‘Ga wanna magunguna aka rubuta, likitan yace zamu iya tafiya. Idan taci abinci ta huta zata ji kwari a jikinta, idan akwai wata matsala yace sai a dawo.’
Duk da tace masa zata iya tashi amma sai da ya riketa ya kamata sannan ta tashi, yana rike da ita har suka zo wajen motarsa. Sai da ya kwantar da kujerar gaban motarsa sannan ya sa Aisha ta dan kashingida. Ya rufe kofar motar ya matso kusa da Zuwaira wadda take tsaye jikin motar da direbanta ya kawota. Yace
‘Ina ga mu tafi a motata, in ya so sai direban ya sameki a can ko.’
Saboda haka gaba daya suka shiga motar Abban suka nufi gidan Aisha.
Sai da ya tsaya a super market ya siyowa Aisha kaji da yoghurt mai sanyi kuma ya hada da apple ya zuba a mota sannan suka wuce gidan.
A bakin gate yayi parking, kafin ya zagayo ya budewa Aisha kofa ta bude ta fito. Ya fito da ledojin da yayi sayayya ya mikawa Zuwaira yana fadin
‘Bari na rakaku ciki sai na fito na wuce office don ko isa ban yi ba na sami kiranki.’
Yana rike da Aishan suka nufo gidan, tunda ya bude gate din ya sako kafarsa cikin gidan ya fara jin wannan warin da yake firgita shi. Daga hannunsa da take rike da shi ta fuskanci abinda yake faruwa da shi, tana kokarin duba fuskarsa ya zare hannun nasa daga cikin nata.
Suna daf da taka barandar falon ya ja baya, yana juyowa ya fuskanci Zuwaira wadda take biye da su a baya wadda itama sauyawar da fuskarshi tayi yayi matukar bata mamaki. Kafin tace wani abu yace
‘Yauwa ku shiga, bari nayi sauri naje sai na dawo.’
Bata yi tsammanin ya ji a dawo lafiyar da takeyi masa ba don kamar a guje ya fice har yana yin tuntube.
Suka kalli juna ita da Aisha, ta matsa kusa da Aishan tana mamaki. Aisha tayi murmushi tace
‘Kin gani ko? Wallahi da ya shigo yake rudewa haka.’
Suka karasa cikin gidan.
Kafin wani lokaci Zuwaira ta gyarata ta hada mata abinci, bayan taci abinci ta sha magani ta kwanta a dakin baki sai bacci.
Kafin azahar dangi duk sun hadu a gidan don wannan karon Hajiya ma cewa tayi sai ta zo, don haka gaba daya suka taho da yaran da Anti Uwani. Sai da yamma suka tafi suka barta da Amira bayan da suka tabbatar ta wattsake.
-------
Kafin ya fita daga gidan har kansa ya fara sarawa, yana fita daga gate din ya kama hanyar ya nufi gidan Zahra.
Sai da ya kusa zuwa gate sannan ya kalli hannunsa ya ga mukullin motarsa, a take ya tuna da motarsa kuma ya tuna office ya kamata ya tafi.
A hankali ya janyo kafarsa ya dawo ya shiga motarsa ya kama hanyar office. Zuciyarsa tana begen Aisha amma ya kasa shiga inda take. Ya tuno kamar dai lokacin da suna asibiti bai ji wani wari ba, shi ya manta ma da wannan matsalar gaba daya.
Abun yana ransa kullum yana cewa zai nemi taimako ko addu’a a yi masa amma sai ya dinga mantawa, wasu lokutan ma yana rasa abinda ya sa baya magana a kan matsalar nan. Sau biyu yana zuwa gidan Yaya Bello don ya sanar da shi matsalar amma idan yaje sai suyita wasu hirarrakin gaba daya ma ya manta da abinda ya kaishi.
Yana tukin ma abinda yake ransa shine ya wuce wajen wani malami da ya sani mai Islamic chemist yaji ko zai sami wani taimako. Kafin ya gama tsara abinda zai gayawa Malam din kawai ya tsinci kansa a farfajiyar office anata faman yi masa sannu da zuwa.
Haka ya hakura ya shiga office din da niyyar idan ya tashi daga aiki ya biya ta wajen Malam din.
__
Tun ranar da Balele ya fara zuwa aiki suka fara fita da Zahra, da yake ta maida hankali kuma hawa motar tana ranta kafin sati hannunta ya fada. Tunda kuwa taga ta fara iya fita ita kadai ta bawa Balele tata motar ta karbi Fijo din da Malam Sule ya bar masa, don tana ganin ko Yaya dai wannan din tafi wadda Abban ya bata tsada.
Tunda motar tazo hannu kuma sai ta fara yi masa tunin yayi mata alkawarin kujerar Umra, wadda ta ce masa ta azumi take so kuma shi ma goman karshe. Ya tabbatar mata kujerarta tana nan in Sha Allahu da lokacin yayi za a bata.
………
Tunda Balele ya fara aiki Sadik ya makale masa saida ya koyi mota, dama tun a wajen Malam Sule ya so koya Abbanshi ya hana.
Jarrabawarsa ta WAEC ta kusan fitowa, shi da Mommy sun hadu sun saka Abban a gaba a kan lallai sai an kai shi Dubai zai yi degree. Da fari Abban ya ki amincewa amma daga baya ya amsa don haka sakamakon WAEC din kawai ake jira.