Sashe 29
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
‘Zai dawo ya sameni don wallahi ba zan yarda ba.’
Haka ta wuni ranar tana shirin yanda zata bullo masa idan ya dawo.
Bata son ta ga Aisha a cikin walwala, tunda dai ta kasa rabasu da Yusuf to ta fi so ta ganta cikin damuwa da takura. Idan dai farin ciki take so to taje ta nemi mijinta ta bar mata Yusuf.
------
Kamar duk Babbar Sallah ranar hudu ga Sallah a gidan Umma suke wuni, don haka ma wannan sallar duka suka hadu da yaransu.
Zainab da matar Abubakar Fauziyya suna daki waken Hajiya yayinda Aisha, Zahida da Zuwaira sune a zaune a falo yaran kuma suna ta kaiwa da kawowarsu.
Aisha ta dubi Zainab tace
‘Ya Zainab nifa mota zan saya bayan sallar nan.’
Ta gyara zama tana murmushi
‘Haba! Ko ke fa? Tun tuni kike maganar nan amma sai wani jan kafa kike.’
‘Ba zaki gane ba Yaya Zainab. Kin san shi Yusuf da a tsarinsa yana da driver wanda ya kamata ya kaimu duk inda zamuje, amma matarsa ta hanani morar direban nan. In kika ga na hau motar nan to mai ita yana nan a gabansa ne amma yana juya baya haka zata barni da hawa motar haya.’
Zahida tace
‘Yauwa Yaya Aisha ai gara haka wallahi, ta karata da waccan motar.’
‘Hmmm! Kin san na fara yi masa maganar kwanaki yace na bari zai duba, a tunanina so yayi ya saya min to amma kinga idan ya saya min dole ya saya mata kuma inaga ko dai bashi da kudin sayen biyu ko kuma baya so ya bata motar. Su dai suka sani.’
Zainab tace
‘To ai ke da kudinki zaki saya ko?’
‘Eh, next month zan dauki adashi dubu dari uku idan na debi wasu a kudaden hayar gidana da nake tarawa na hada kamar miliyan daya da rabi na san zan sami mota mai kyau kuma kinga tunda Yaya Abubakar zan bawa ya siya min na san idan da ciko zai cika min.’
Zahida ta mika mata hannu suka tafa tana fadin
‘Baki da matsala Mrs Yusuf.’
Haka suka gama hirarrakinsu Aisha ta gama yanke shawara zata sayi mota saboda ta huta da wulakanci da Zahra take mata akan motar gidan.
………
Ya rigar ya sanar da su ranar Lahadi da sassafe zai dawo don haka duka suke ta shirin tarbarsa.
Wajen karfe bakwai na safe aka bugawa Aisha gate, Rukayya ce da kayanta niki-niki. Aishan ta dubeta bayan ta bude mata ta shigo tace
‘Rukayya ya na ganki da kaya?’
Ta sunkuyar da kai ta bata amsa
‘Mommy ce tace na taho dasu na dawo tayaki kwanan.’
‘To shiga muje ga Amira can tana bacci a dakin sai ta tayaki ki ajiye kayan ku fito muyi breakfast.’
Ta amsa ta wuce dakin, ita kuma Aisha ta koma kicin inda take aiyukanta.
Tana aiki tana dariyar Zahra; tabbas ta tabbata mai fuska biyu. Wato yana tafiya ta turo aka kirawo mata ‘yarta saboda kada ta tayata kwana, yanzu kuma da yake ya ce yau zai dawo shine har ta turota. Wato duk tsagerancinta ma akwai wanda take tsoro, sai dai tsoron Allah ne kawai bata yi. Haka tayi ta aiki tana dariya ita kadai.
Karfe shida da rabi na safe jirgin su Abba ya sauka a Nigeria. Suna sauka Malam Sule yana jiransu, a nan airport din ya sami taxi ya sa Yaya Bello don a kai shi gida kai tsaye.
Tun da suka fara shirin dawowa dama ya sanar da su a gidan Zahra zai sauka. Tayi shiri sosai na dawowarsa, an gyara gida sosai sannan ga abinci ta shirya masa funkaso da farfaesun naman Sallah ga zobo kuma sai kamshi kawai ke tashi.
Karfe takwas saura kwata motar Malam Sule ta tsaya a bakin gate din gidan Zahra, Malam Sule ya danna horn suna jiran mai gadi ya zo ya bude.
Dan ga ruwan da yake kawowa Aisha ruwa ne ya zo ya tsaya a bakin gate dinta, Abban yana hangoshi. Ya dauki dutse ya kwankwasa gate din ya dawo ya fara sauke jarkokin ruwan a wajen.
Abban ya dubi Malam Sule yace
‘Malam Sule me dan ga ruwa yake a kofar gidan can?’
‘Ah, yallabai Ina ga ai ruwa ya kawo amma ban sani ba, ko na karasa na tambayo Hajiyar?’
A dai-dai lokacin mai gadi ya zuge gate din, Abban ya bude kofar motar yana fadin
‘Shigar da motar, bari na je na ji.’
Ya fice Malam Sule ya tura motar ciki.
Yana isa gate din Aisha tana budewa, sanye da jilbab dinta. Ta dubi me ruwa tace
‘Sauke min a nan.’
Ta nuna masa wajen daga ciki.
Abba ya karasa shiga da fara’arta tace
‘Alhajin Allah, Sannu da zuwa.’
Da fara’a shima ya amsa sannan yace
‘Ya naga Dan ga ruwa?’
‘Uhm, ruwan ne Ina jin ya sami matsala shi yasa ba a kunnawa.’
Ta nunawa dan ga ruwa bokitin fentin da ta ajiye tana fadin
‘Juye a nan na dauka.’
Abba yace
‘Ke kike kaiwa ciki.’
‘Eh ai saboda nauyi, in na kai sai na dawo na kara kaiwa har na cika drum din.’
‘Gafara.’
Ya dauki jarkar ya nufi cikin gidan ta bi shi a baya yana tamabaya
‘A Ina kike juyewa?’
‘Akwai drum a kitchen.’
Yana shiga falon Rukayya da Amira suna zaune suna kallon TV. Duka suka mike suka yi masa sannu da zuwa ya amsa ya wuce kicin ya juye ruwan. Ya dawo ya sake dauko wata jarkar ya komo ciki.
Rukayya ta dubi Amira tace
‘Bari naje na gayawa Mommy Abba ya dawo.’
Ta fice da gudu suka hadu da Abban a tsakar gidan yana dauke da jarka tace
‘Abba bari naje na cewa Mommy ka dawo.’
Ta fice da gudu.
Haka ya gama juye mata ruwan ya cika mata drum biyu sannan ya fito ya sallami Dan ga ruwa ya koma ciki.
A daki ya sameta tana goge inda ruwa ya zuzzube, ya tsaya yana kallonta yana murmushi.
Ta dubeshi itama tana dariya tana fadin
‘Bari na sama maka ruwa ka dan sha.’
Ta zo wucewa ta gefensa ya sha gabanta ya janyota jikinsa ya rungumeta, suka sa dariya.
Bayan sun fito falon ta ajiye masa kunun aya mai sanyi da cake, ya ci ya koshi suna dan taba hira sannan yayi mata sallama ya wuce gidan Zahra.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
18
Tunda Rukayya ta kawo labarin ya dawo yana can yana diban ruwa Mommy take faman cika tana batsewa, dama Malam Sule ya shigo da karamar jakarsa.
Sai a lokacin sannan Mommy ta tuna Sadik ya yanke wayar injin janyo ruwan, ta dubeshi tace
‘Sadik baka mayar da abun nan ba ashe?’
‘Wallahi na manta Mommy, ba komai kafin dare zan mayar.’
Suka cigaba da harkarsu yayinda ita kuma ta wuce daki.
Duk nishadin da take ciki ya gushe saboda gaya mata da akayi yana can gidan Aisha yana kai mata ruwa. Ce mata yayi a nan wajenta zai sauka amma saboda munafinci yana can wajen amaryarsa yana hutawa, tabbas zai zo ya sameta.
Da sallama ya shigo gidan, tana sama ta jiyo yara suna oyoyo. A falon saman tayi zamanta tana jiransa tunda dama a nan ta saka masa abincinsa.
A zaune ya sameta a kan kujera tana ta cika tana batsewa, bai ma kula da yanayin fuskarta ba.
Yana rike da hannun Ummi ya shiga falon da sallama, bayan ta amsa sallamarsa ta bude baki kamar wadda aka yi wa dole tace
‘Sannu da zuwa.’
Ya karaso ya zauna a kusa da ita bayan ya amsa yace
‘Ya akayi babu ruwa a gidan Aisha ne, me ya sa ba a kunnawa ruwa yaje can na ga kuma nan da ruwa don fanfon waje ma a kunne yake?’
Ta dan gatsina fuska
‘Lalacewa yayi ina ga don kullum kuwa ana kunnawa, kuma bata fada baya zuwa ba ai da an duba.’
Ya gyara zama ya zaro waya, ya lalubo lambar wayar plumber ya danna masa kira, tana ji yana cewa lallai ya zo kafin la’asar don yau yake so a gyara ruwan nan.
Ranta ya kara matukar baci; tun da ya dawo unguwarnan yake hidimar Aisha kuma har yanzu ma ya shigo wajenta kallon kirki bata isheshi ba balle ma ya san yanayin da take ciki.
Ta daure ta tashi ta nufi dining table don ta kula sai ma tayi da gaske sannan zai dubeta. Ta dauko jug din zobon da kofi ta dora a kan tray ta kawo inda yake zaune shi da Ummi ta ajiye. Ta fara zubawa yace
‘Kai ba zan sha zobon nan ba ruwa dai zaki bani.’
Ta bishi da kallon mamaki, to me yake nufi?
Ta dauke zobon ta mayar kan table ta dauko masa ruwan roba ta kawo masa ta koma ta zauna.
Ya bude ya sha kamar rabin roba sannan ya dubeta yace
‘Ya na sameku? Ya gidan da yaran?’
Ta dan yi murmushi tace
‘Lafiya muke gaba daya, ya ibada? Ya gajiyar hanya?’
‘Lafiya kalau, mun gode Allah. Bari na watsa ruwa na fito na ci abinci kin san ban yi breakfast ba.’
‘Sai ka fito.’
Ya shige dakin tabi bayansa da kallo.
Sai da ya dauki lokaci ya shirya sannan ya fito, ya ce ta saka masa abincinsa a kan kafet ba zai ci a tebur ba don haka nan ya baje a kan kafet ya ci funkaso sosai ya shanye romonsa.
Naman sallan da ta sa masa a plate kuma ya ajiye a gefensa yana ci suna hira da yara. Sai a lokacin ne take jajanta masa barin da Aisha tayi, duk ba bata je ko kofar gidan ba haka kiri-kiri tace masa ta je.
Can zuwa azahar yana zaune a falo yana hutawa maigadi ya shigo ya sanar da shi isowar plumber, don haka ya tashi ya fice.
Kamar yanda al’adarsa take idan dai za ayi wani gyara a gidan nan to sai dai ayi a gabansa, don haka yau din ma tare suka zagaya bayan gidan.
Mai gyara yayi 'yan dube-dubensa ya juyo ya dubi Abban yace
‘Yallabai yara sun yi wasa a wajen nan dai ko?’
‘Ka san bana gari, ba zan iya sani ba. Me ka gani?’
Haka ta wuni ranar tana shirin yanda zata bullo masa idan ya dawo.
Bata son ta ga Aisha a cikin walwala, tunda dai ta kasa rabasu da Yusuf to ta fi so ta ganta cikin damuwa da takura. Idan dai farin ciki take so to taje ta nemi mijinta ta bar mata Yusuf.
------
Kamar duk Babbar Sallah ranar hudu ga Sallah a gidan Umma suke wuni, don haka ma wannan sallar duka suka hadu da yaransu.
Zainab da matar Abubakar Fauziyya suna daki waken Hajiya yayinda Aisha, Zahida da Zuwaira sune a zaune a falo yaran kuma suna ta kaiwa da kawowarsu.
Aisha ta dubi Zainab tace
‘Ya Zainab nifa mota zan saya bayan sallar nan.’
Ta gyara zama tana murmushi
‘Haba! Ko ke fa? Tun tuni kike maganar nan amma sai wani jan kafa kike.’
‘Ba zaki gane ba Yaya Zainab. Kin san shi Yusuf da a tsarinsa yana da driver wanda ya kamata ya kaimu duk inda zamuje, amma matarsa ta hanani morar direban nan. In kika ga na hau motar nan to mai ita yana nan a gabansa ne amma yana juya baya haka zata barni da hawa motar haya.’
Zahida tace
‘Yauwa Yaya Aisha ai gara haka wallahi, ta karata da waccan motar.’
‘Hmmm! Kin san na fara yi masa maganar kwanaki yace na bari zai duba, a tunanina so yayi ya saya min to amma kinga idan ya saya min dole ya saya mata kuma inaga ko dai bashi da kudin sayen biyu ko kuma baya so ya bata motar. Su dai suka sani.’
Zainab tace
‘To ai ke da kudinki zaki saya ko?’
‘Eh, next month zan dauki adashi dubu dari uku idan na debi wasu a kudaden hayar gidana da nake tarawa na hada kamar miliyan daya da rabi na san zan sami mota mai kyau kuma kinga tunda Yaya Abubakar zan bawa ya siya min na san idan da ciko zai cika min.’
Zahida ta mika mata hannu suka tafa tana fadin
‘Baki da matsala Mrs Yusuf.’
Haka suka gama hirarrakinsu Aisha ta gama yanke shawara zata sayi mota saboda ta huta da wulakanci da Zahra take mata akan motar gidan.
………
Ya rigar ya sanar da su ranar Lahadi da sassafe zai dawo don haka duka suke ta shirin tarbarsa.
Wajen karfe bakwai na safe aka bugawa Aisha gate, Rukayya ce da kayanta niki-niki. Aishan ta dubeta bayan ta bude mata ta shigo tace
‘Rukayya ya na ganki da kaya?’
Ta sunkuyar da kai ta bata amsa
‘Mommy ce tace na taho dasu na dawo tayaki kwanan.’
‘To shiga muje ga Amira can tana bacci a dakin sai ta tayaki ki ajiye kayan ku fito muyi breakfast.’
Ta amsa ta wuce dakin, ita kuma Aisha ta koma kicin inda take aiyukanta.
Tana aiki tana dariyar Zahra; tabbas ta tabbata mai fuska biyu. Wato yana tafiya ta turo aka kirawo mata ‘yarta saboda kada ta tayata kwana, yanzu kuma da yake ya ce yau zai dawo shine har ta turota. Wato duk tsagerancinta ma akwai wanda take tsoro, sai dai tsoron Allah ne kawai bata yi. Haka tayi ta aiki tana dariya ita kadai.
Karfe shida da rabi na safe jirgin su Abba ya sauka a Nigeria. Suna sauka Malam Sule yana jiransu, a nan airport din ya sami taxi ya sa Yaya Bello don a kai shi gida kai tsaye.
Tun da suka fara shirin dawowa dama ya sanar da su a gidan Zahra zai sauka. Tayi shiri sosai na dawowarsa, an gyara gida sosai sannan ga abinci ta shirya masa funkaso da farfaesun naman Sallah ga zobo kuma sai kamshi kawai ke tashi.
Karfe takwas saura kwata motar Malam Sule ta tsaya a bakin gate din gidan Zahra, Malam Sule ya danna horn suna jiran mai gadi ya zo ya bude.
Dan ga ruwan da yake kawowa Aisha ruwa ne ya zo ya tsaya a bakin gate dinta, Abban yana hangoshi. Ya dauki dutse ya kwankwasa gate din ya dawo ya fara sauke jarkokin ruwan a wajen.
Abban ya dubi Malam Sule yace
‘Malam Sule me dan ga ruwa yake a kofar gidan can?’
‘Ah, yallabai Ina ga ai ruwa ya kawo amma ban sani ba, ko na karasa na tambayo Hajiyar?’
A dai-dai lokacin mai gadi ya zuge gate din, Abban ya bude kofar motar yana fadin
‘Shigar da motar, bari na je na ji.’
Ya fice Malam Sule ya tura motar ciki.
Yana isa gate din Aisha tana budewa, sanye da jilbab dinta. Ta dubi me ruwa tace
‘Sauke min a nan.’
Ta nuna masa wajen daga ciki.
Abba ya karasa shiga da fara’arta tace
‘Alhajin Allah, Sannu da zuwa.’
Da fara’a shima ya amsa sannan yace
‘Ya naga Dan ga ruwa?’
‘Uhm, ruwan ne Ina jin ya sami matsala shi yasa ba a kunnawa.’
Ta nunawa dan ga ruwa bokitin fentin da ta ajiye tana fadin
‘Juye a nan na dauka.’
Abba yace
‘Ke kike kaiwa ciki.’
‘Eh ai saboda nauyi, in na kai sai na dawo na kara kaiwa har na cika drum din.’
‘Gafara.’
Ya dauki jarkar ya nufi cikin gidan ta bi shi a baya yana tamabaya
‘A Ina kike juyewa?’
‘Akwai drum a kitchen.’
Yana shiga falon Rukayya da Amira suna zaune suna kallon TV. Duka suka mike suka yi masa sannu da zuwa ya amsa ya wuce kicin ya juye ruwan. Ya dawo ya sake dauko wata jarkar ya komo ciki.
Rukayya ta dubi Amira tace
‘Bari naje na gayawa Mommy Abba ya dawo.’
Ta fice da gudu suka hadu da Abban a tsakar gidan yana dauke da jarka tace
‘Abba bari naje na cewa Mommy ka dawo.’
Ta fice da gudu.
Haka ya gama juye mata ruwan ya cika mata drum biyu sannan ya fito ya sallami Dan ga ruwa ya koma ciki.
A daki ya sameta tana goge inda ruwa ya zuzzube, ya tsaya yana kallonta yana murmushi.
Ta dubeshi itama tana dariya tana fadin
‘Bari na sama maka ruwa ka dan sha.’
Ta zo wucewa ta gefensa ya sha gabanta ya janyota jikinsa ya rungumeta, suka sa dariya.
Bayan sun fito falon ta ajiye masa kunun aya mai sanyi da cake, ya ci ya koshi suna dan taba hira sannan yayi mata sallama ya wuce gidan Zahra.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
18
Tunda Rukayya ta kawo labarin ya dawo yana can yana diban ruwa Mommy take faman cika tana batsewa, dama Malam Sule ya shigo da karamar jakarsa.
Sai a lokacin sannan Mommy ta tuna Sadik ya yanke wayar injin janyo ruwan, ta dubeshi tace
‘Sadik baka mayar da abun nan ba ashe?’
‘Wallahi na manta Mommy, ba komai kafin dare zan mayar.’
Suka cigaba da harkarsu yayinda ita kuma ta wuce daki.
Duk nishadin da take ciki ya gushe saboda gaya mata da akayi yana can gidan Aisha yana kai mata ruwa. Ce mata yayi a nan wajenta zai sauka amma saboda munafinci yana can wajen amaryarsa yana hutawa, tabbas zai zo ya sameta.
Da sallama ya shigo gidan, tana sama ta jiyo yara suna oyoyo. A falon saman tayi zamanta tana jiransa tunda dama a nan ta saka masa abincinsa.
A zaune ya sameta a kan kujera tana ta cika tana batsewa, bai ma kula da yanayin fuskarta ba.
Yana rike da hannun Ummi ya shiga falon da sallama, bayan ta amsa sallamarsa ta bude baki kamar wadda aka yi wa dole tace
‘Sannu da zuwa.’
Ya karaso ya zauna a kusa da ita bayan ya amsa yace
‘Ya akayi babu ruwa a gidan Aisha ne, me ya sa ba a kunnawa ruwa yaje can na ga kuma nan da ruwa don fanfon waje ma a kunne yake?’
Ta dan gatsina fuska
‘Lalacewa yayi ina ga don kullum kuwa ana kunnawa, kuma bata fada baya zuwa ba ai da an duba.’
Ya gyara zama ya zaro waya, ya lalubo lambar wayar plumber ya danna masa kira, tana ji yana cewa lallai ya zo kafin la’asar don yau yake so a gyara ruwan nan.
Ranta ya kara matukar baci; tun da ya dawo unguwarnan yake hidimar Aisha kuma har yanzu ma ya shigo wajenta kallon kirki bata isheshi ba balle ma ya san yanayin da take ciki.
Ta daure ta tashi ta nufi dining table don ta kula sai ma tayi da gaske sannan zai dubeta. Ta dauko jug din zobon da kofi ta dora a kan tray ta kawo inda yake zaune shi da Ummi ta ajiye. Ta fara zubawa yace
‘Kai ba zan sha zobon nan ba ruwa dai zaki bani.’
Ta bishi da kallon mamaki, to me yake nufi?
Ta dauke zobon ta mayar kan table ta dauko masa ruwan roba ta kawo masa ta koma ta zauna.
Ya bude ya sha kamar rabin roba sannan ya dubeta yace
‘Ya na sameku? Ya gidan da yaran?’
Ta dan yi murmushi tace
‘Lafiya muke gaba daya, ya ibada? Ya gajiyar hanya?’
‘Lafiya kalau, mun gode Allah. Bari na watsa ruwa na fito na ci abinci kin san ban yi breakfast ba.’
‘Sai ka fito.’
Ya shige dakin tabi bayansa da kallo.
Sai da ya dauki lokaci ya shirya sannan ya fito, ya ce ta saka masa abincinsa a kan kafet ba zai ci a tebur ba don haka nan ya baje a kan kafet ya ci funkaso sosai ya shanye romonsa.
Naman sallan da ta sa masa a plate kuma ya ajiye a gefensa yana ci suna hira da yara. Sai a lokacin ne take jajanta masa barin da Aisha tayi, duk ba bata je ko kofar gidan ba haka kiri-kiri tace masa ta je.
Can zuwa azahar yana zaune a falo yana hutawa maigadi ya shigo ya sanar da shi isowar plumber, don haka ya tashi ya fice.
Kamar yanda al’adarsa take idan dai za ayi wani gyara a gidan nan to sai dai ayi a gabansa, don haka yau din ma tare suka zagaya bayan gidan.
Mai gyara yayi 'yan dube-dubensa ya juyo ya dubi Abban yace
‘Yallabai yara sun yi wasa a wajen nan dai ko?’
‘Ka san bana gari, ba zan iya sani ba. Me ka gani?’