Sashe 19
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
‘Ah bari ma kawai na kirawota ta turo min hotunansu sai ki zaba ko?’
Kafin ta amsa ya daga waya ya kirawo Zahra, wadda a take ta turo masa hotunan leshin ta Whatsapp.
Irin leshin nan ne mai hade da mayafinsa, ta san kudinsu basu wuce dubu ashirin da biyar ba. Bata raina ba, sai dai kuma leshin baya burgeta kwata kwata. Tabbas da anyi shawara da ita ba za a saya mata wannan leshin ba domin ita da a bata wannan gara a bata leshi marar mayafi ko ma atamfa. Ta duba su gaba daya ma kalolin ba wani kyau sukayi ba amma dai ta zabi wani kalar ruwan toka mai fulawoyi ruwan goro.
Ana kawo leshin ta kaiwa Hajiya tace a bawa Zahida ta kai mata dinki zasuyi waya.
Sai ana i gobe Sallah ya sanar da ita sa zai yanka da rago, kuma zuwa zatayi su soya tare a gidan Mommy in an gama soyawa sai a raba a dibarwa kowa nasa. Tsarin bai yi mata ba domin tun bayan zuwansu gidan Hajiya bata son shiga harkar Zahra, sai dai bata son tayi masa musu kada yaga kamar kullum itace take fara bashi matsala. Don haka tace babu komai hakan yayi.
Ta san Zahran ce ta shirya masa hakan kuma ta san don a cuceta ne, amma zata tsaya taga gudun ruwansu tukunna.
Amma dole a sake wannan tsarin don ba zata dauka ba.
------
Kudin kayan sallar da ya turo mata a ciki ta samu ta fidda dubu ashirin kudin aikin da Hajja tace zata yi mata; domin ko leshin da ta bawa Aisha ma dubu ashirin da biyar take sayar da shi amma a kan dubu hamsin ta bawa Abban.
Nan da nan ta kirawo Hajjan ta sanar da ita kudi sun samu, tayi mata alkawarin zata kawo mata aikin ana saura kwana uku Sallah.
Ranar asabar kuwa sai ga Hajja, bayan sun gaisa ta zaro farar kwalba irin ta fiya-fiya. Tarkace ne kawai a cikin kwalbar sai wani guntun tsoka da aka sokawa allura ga kuma takarda wadda ke dauke da rubutun larabci a jiki wadda aka nannade aka sakata a tsaye. Ta mikawa Zahra kwalabar tare da wata mitsitsiyar kwalbar baka tace
‘Kin gansu nan; wannan babbar ki sami singiletinsa wadda ya saka yayi gumi a jikinta ki gutsiri dan mitsitsi ki saka a ciki. Idan kika saka sai ki juye man da yake cikin wannan kwalbar ki mayar ki rufe. Ki samu waje mai duhu ki boye kwalbarki; idan kikayi haka to zaki sha mamaki don ya daina musa maganarki kuma duk abinda zai bata ranki ba zai yi shi ba.'
‘Allah Hajja.’
‘Ai sai dai idan bakiyi yanda nace ba, amma tabbas idan kinyi yanda nace to baki da matsala.’
Sukayi sallama tana ta jin dadi.
Ranar a wajenta ya kwana don haka singiletin da ya cire ita ta samu ta yanka ta hada kamar yanda aka umarceta. Ta samu waje a dakinta bayan wardrobe ta boye kwalbar. Ta kwana tana walwala da farin ciki.
Ranar Sallah ba a wajen Aisha yake ba, amma dai ya sanar da ita da safe zasu tafi da tuwon Sallah don su kaiwa Hajiya idan an sauko idi don haka itama ta zuba nata.
Tun dare Rukayya ta tayata ta gama miyar taushenta sannan ta hada zobonta mai dadi. Asuba nayi ta dora tuwo, da yake ba yawa ne da shi ba nan da nan ta gama. Suka gyara gidan tare da Rukayya suka yi wanka. Atamfa ta saka sabuwa kar dinkin doguwar rigar mai matukar kyau, tayi kwalliyarta sannan suka budade gidan da turaren wuta.
Zuwa karfe bakwai da rabi sun gama komai don haka Rukayya tayi mata sallama a kan zata je gida don kayanta suna can.
Bata dade da fita ba ya shigo tare da Sadik; tunda aka kawota yaune rana ta farko da Sadik ya shigo gidan kuma yaune rana ta biyu data taba ganinsa, don ko a unguwar bata hangoshi. Bata son yanda yake mata wani kallo mai cike da raini, amma dai haka ya gaisheta ta amsa.
Abbansa ya wuce daki tabi bayansa.
Basu dade da shiga ba suka fito, ta basu abincin gidan Hajiya a flask da kuma zobo a kula suka kama hanya.
………
Ya riga ya sanar da ita tsarin yanda suyar naman Sallah zata kasance, ya gaya mata ranar Sallah ake farawa a karasa washegari don haka idan an yanka za a zo ayi mata magana.
Sai wajen sha daya aka turo Rukayya ta kirawota, nan take ta canza kaya suka tafi tare da Rukayyan.
Masu aiki ne su biyu Uwar biyu da kuma Hansatu, sai Jummai, sannan kuma ga Asiya wadda itace ‘yar autar su Zahran wadda ta koma hannu Yayansu Muhammad tun bayan rasuwar mahaifiyarsu. Ana ta aikace-aikace, su Hansatu suna kokarin hura wuta, ta karasa suka gaisa da Mommy babu yabo babu fallasa. Su Jummai ma duk suka gaggaisheta, amma tana kallon Yusra bata gaisheta ba kuma babu wanda yace wani abu. Ta zauna ta kamawa Jummai nama suka cigaba da yankawa.
Murahu biyar aka dora don haka aikin nasu ya fara da sauri. Gaba daya naman san gida aka shigo musu da shi, sai raguna guda uku. Ya raba rago daya da rabi aka bayar sadaka a waje, aka sake shigo musu da rago daya da cinyoyin na biyun.
A take Mommy ta ware naman da za ayiwo musu dambun nama ta bayar aka tafi kaiwa.
Ragowar kuma ana soyawa ana kulle wani ana kai mata freezer.
Duk kaskon da aka sauke za a watso naman a faranti ace kowa ya taba, haka har magriba suna aiki. Babu laifi an soya da yawa don haka ana yin Sallah Mommy tace a barshi haka gobe a karasa.
A gajiye Aisha ta dauki ‘yar jakarta da ta shigo da ita tayi musu sallama ta koma gida.
Ta gaji, bata taba yin aikin sa ba don ita kullum raguna ake yanka musu. Ta so ace an bata nata naman tayi yanda take so da shi amma da yake wannan ne karon fari ta hakura; amma tabbas bazata sake wannan aikin hadakar ba. Danyen naman da taga ana sakawa a freezer tayi zaton za ace ga nata amma bataji an ce ba, tana jira taga goben tukunna.
Ranar ma ba a wajenta zai kwana ba don haka ita da Rukayya suka kwana. Tun bakwai na safe yayiwo mata waya yace su taho an fara aiki; da kyar ta tashi suka shirya suka fice. Tana sane taki cin abinci suka fice. Suna zuwa suka dan taba aikin ta fuskanci tayi kamar awa daya tana aiki ta cewa Mommy zatazo gidan tayi breakfast yanzu zata dawo. Ta fice ta barsu a ranta ta san ba zata koma ba don ta gaji.
Tana shiga gida taci abincinta ta koma bacci.
Sai can wajen azahar Zahra ta sami Abban Sadik din ta ce masa ya je ya turo musu Aisha saboda aiki yayi yawa. Take ya tashi ya nufi gidan.
Tsit gidan kamar babu kowa, don haka ya wuce daki. Tayi dai-dai a kan gado tana baccinta don ko motsinsa bata ji ba, saida yayi gyaran murya ya zauna a gefen gadon sannan ta farka.
Ta mutssike idonta tace
‘A’a sannu da zuwa.’
Bayan ya amsa yace
‘Lafiya dai ko, anata aiki ashe kina nan kina bacci.’
Ta yatsina fuska tana daga kwance
‘Jiri naji yana kwasata ga kaina yana ciwo shi yasa na zo na kwanta, ka san zazzabin nan ba wai ya gama sakina bane.’
‘Eh hakane.’
Ya kai hannu ya taba wuyanta
‘To kin sha Panadol?’
‘Eh, na sha kafin na kwanta da yake ban dade da kwantawa ba ka shigo.’
‘Ok, to sannu. Kwanta, bari naje sai nayi musu bayani.’
Yayi mata sallama ya fice.
Yana shiga ya wuce falo, don haka mommy ta bishi. Yana kokarin kunna TV tace
‘Abban Sadik lafiya dai Aishan bata dawo ba?’
‘Uh, bata jin dadi ne. Jiri take da ciwon kai kin san bata gama warwarewa ba tayi zazzabi kwanan na.’
Ta hadiye malolon da ya taso mata ta yage baki tace
‘Mhmm! Ko dai kanwata ciki ne da ita ne ake mana laulayi a fakaice.’
Yayi dariya yana shafa kai
‘A’a Babu wannan zancen tukunna, zazzabi ne dai kawai.’
Suka dan taba hira sannan ta tashi ta wuce dakinta, tana shiga ta zauna a gefen gado cike da damuwa; tabbas cikine da Aisha don jiyan ma tana kula da yanda take abubuwa jikinta babu kwari. Tab, ya za ayi ta bari a haihu da mijinta, gashi ta cika gida da yara mata yanzu idan Aishan ta haifi maza uku ko mutuwa yayi sai ta fita gadon arzikin da aka tara da ita. Gaskiya ba zata yarda ba.
Ta shafa hannunta inda aka saka mata inplant na family planning; tabbas da an koma aiki zata je a cire mata wannan abun don ya zama ko da bata sami hanyar lalata cikin Aisha ba to sai dai suyi haihuwar tare. Ba zata sha wahalar talaucin Yusuf ba kuma ya tara dukiya a fi ta gado. Haka ta zauna tayi ta tunani har saida Nana ta shigo kiranta ta sanar da ita an sauke wani ta zo ta nuna wanda za dora sannan ta taso ta fito.
Zuwa la’asar sun gama soya duk naman da za a soya, sai su Jummai da suke ta faman gyara wajen. Danyen naman kuma duk an lode a babbar freezer.
A falon kasa ta zauna ta dibarwa Hajiya nata naman cikin wata babbar roba mai murfi! Duk da Hajiyan ma ya yanka mata rago a gidanta amma haka suka saba sai an kai mata. Ta sami ‘yan bakaken ledodi ta zubawa su Jummai nasu tunda dukansu ta basu danye da yawa sun kai gida sannan kuma biyansu zata yi kudin aikinsu.
Ta dauko kwanon samira mai kamar girman langa tuwo da miya ta zuba naman har ta cika sannan ta rufe sannan ta dauko roba irin ta take away din nan ta zuba kayan ciki ta rufe.
Ta dubi Rukayya wadda take zaune tana ta cin naman tace
‘Rukayya dauki ki kaiwa matar ubanku.’
Tace
‘Anti Aisha?’
A fusace mommyn tace
‘Ba ita ba ni, kuma idan kin je ki zauna tunda uwarkice.’
Kafin ta amsa ya daga waya ya kirawo Zahra, wadda a take ta turo masa hotunan leshin ta Whatsapp.
Irin leshin nan ne mai hade da mayafinsa, ta san kudinsu basu wuce dubu ashirin da biyar ba. Bata raina ba, sai dai kuma leshin baya burgeta kwata kwata. Tabbas da anyi shawara da ita ba za a saya mata wannan leshin ba domin ita da a bata wannan gara a bata leshi marar mayafi ko ma atamfa. Ta duba su gaba daya ma kalolin ba wani kyau sukayi ba amma dai ta zabi wani kalar ruwan toka mai fulawoyi ruwan goro.
Ana kawo leshin ta kaiwa Hajiya tace a bawa Zahida ta kai mata dinki zasuyi waya.
Sai ana i gobe Sallah ya sanar da ita sa zai yanka da rago, kuma zuwa zatayi su soya tare a gidan Mommy in an gama soyawa sai a raba a dibarwa kowa nasa. Tsarin bai yi mata ba domin tun bayan zuwansu gidan Hajiya bata son shiga harkar Zahra, sai dai bata son tayi masa musu kada yaga kamar kullum itace take fara bashi matsala. Don haka tace babu komai hakan yayi.
Ta san Zahran ce ta shirya masa hakan kuma ta san don a cuceta ne, amma zata tsaya taga gudun ruwansu tukunna.
Amma dole a sake wannan tsarin don ba zata dauka ba.
------
Kudin kayan sallar da ya turo mata a ciki ta samu ta fidda dubu ashirin kudin aikin da Hajja tace zata yi mata; domin ko leshin da ta bawa Aisha ma dubu ashirin da biyar take sayar da shi amma a kan dubu hamsin ta bawa Abban.
Nan da nan ta kirawo Hajjan ta sanar da ita kudi sun samu, tayi mata alkawarin zata kawo mata aikin ana saura kwana uku Sallah.
Ranar asabar kuwa sai ga Hajja, bayan sun gaisa ta zaro farar kwalba irin ta fiya-fiya. Tarkace ne kawai a cikin kwalbar sai wani guntun tsoka da aka sokawa allura ga kuma takarda wadda ke dauke da rubutun larabci a jiki wadda aka nannade aka sakata a tsaye. Ta mikawa Zahra kwalabar tare da wata mitsitsiyar kwalbar baka tace
‘Kin gansu nan; wannan babbar ki sami singiletinsa wadda ya saka yayi gumi a jikinta ki gutsiri dan mitsitsi ki saka a ciki. Idan kika saka sai ki juye man da yake cikin wannan kwalbar ki mayar ki rufe. Ki samu waje mai duhu ki boye kwalbarki; idan kikayi haka to zaki sha mamaki don ya daina musa maganarki kuma duk abinda zai bata ranki ba zai yi shi ba.'
‘Allah Hajja.’
‘Ai sai dai idan bakiyi yanda nace ba, amma tabbas idan kinyi yanda nace to baki da matsala.’
Sukayi sallama tana ta jin dadi.
Ranar a wajenta ya kwana don haka singiletin da ya cire ita ta samu ta yanka ta hada kamar yanda aka umarceta. Ta samu waje a dakinta bayan wardrobe ta boye kwalbar. Ta kwana tana walwala da farin ciki.
Ranar Sallah ba a wajen Aisha yake ba, amma dai ya sanar da ita da safe zasu tafi da tuwon Sallah don su kaiwa Hajiya idan an sauko idi don haka itama ta zuba nata.
Tun dare Rukayya ta tayata ta gama miyar taushenta sannan ta hada zobonta mai dadi. Asuba nayi ta dora tuwo, da yake ba yawa ne da shi ba nan da nan ta gama. Suka gyara gidan tare da Rukayya suka yi wanka. Atamfa ta saka sabuwa kar dinkin doguwar rigar mai matukar kyau, tayi kwalliyarta sannan suka budade gidan da turaren wuta.
Zuwa karfe bakwai da rabi sun gama komai don haka Rukayya tayi mata sallama a kan zata je gida don kayanta suna can.
Bata dade da fita ba ya shigo tare da Sadik; tunda aka kawota yaune rana ta farko da Sadik ya shigo gidan kuma yaune rana ta biyu data taba ganinsa, don ko a unguwar bata hangoshi. Bata son yanda yake mata wani kallo mai cike da raini, amma dai haka ya gaisheta ta amsa.
Abbansa ya wuce daki tabi bayansa.
Basu dade da shiga ba suka fito, ta basu abincin gidan Hajiya a flask da kuma zobo a kula suka kama hanya.
………
Ya riga ya sanar da ita tsarin yanda suyar naman Sallah zata kasance, ya gaya mata ranar Sallah ake farawa a karasa washegari don haka idan an yanka za a zo ayi mata magana.
Sai wajen sha daya aka turo Rukayya ta kirawota, nan take ta canza kaya suka tafi tare da Rukayyan.
Masu aiki ne su biyu Uwar biyu da kuma Hansatu, sai Jummai, sannan kuma ga Asiya wadda itace ‘yar autar su Zahran wadda ta koma hannu Yayansu Muhammad tun bayan rasuwar mahaifiyarsu. Ana ta aikace-aikace, su Hansatu suna kokarin hura wuta, ta karasa suka gaisa da Mommy babu yabo babu fallasa. Su Jummai ma duk suka gaggaisheta, amma tana kallon Yusra bata gaisheta ba kuma babu wanda yace wani abu. Ta zauna ta kamawa Jummai nama suka cigaba da yankawa.
Murahu biyar aka dora don haka aikin nasu ya fara da sauri. Gaba daya naman san gida aka shigo musu da shi, sai raguna guda uku. Ya raba rago daya da rabi aka bayar sadaka a waje, aka sake shigo musu da rago daya da cinyoyin na biyun.
A take Mommy ta ware naman da za ayiwo musu dambun nama ta bayar aka tafi kaiwa.
Ragowar kuma ana soyawa ana kulle wani ana kai mata freezer.
Duk kaskon da aka sauke za a watso naman a faranti ace kowa ya taba, haka har magriba suna aiki. Babu laifi an soya da yawa don haka ana yin Sallah Mommy tace a barshi haka gobe a karasa.
A gajiye Aisha ta dauki ‘yar jakarta da ta shigo da ita tayi musu sallama ta koma gida.
Ta gaji, bata taba yin aikin sa ba don ita kullum raguna ake yanka musu. Ta so ace an bata nata naman tayi yanda take so da shi amma da yake wannan ne karon fari ta hakura; amma tabbas bazata sake wannan aikin hadakar ba. Danyen naman da taga ana sakawa a freezer tayi zaton za ace ga nata amma bataji an ce ba, tana jira taga goben tukunna.
Ranar ma ba a wajenta zai kwana ba don haka ita da Rukayya suka kwana. Tun bakwai na safe yayiwo mata waya yace su taho an fara aiki; da kyar ta tashi suka shirya suka fice. Tana sane taki cin abinci suka fice. Suna zuwa suka dan taba aikin ta fuskanci tayi kamar awa daya tana aiki ta cewa Mommy zatazo gidan tayi breakfast yanzu zata dawo. Ta fice ta barsu a ranta ta san ba zata koma ba don ta gaji.
Tana shiga gida taci abincinta ta koma bacci.
Sai can wajen azahar Zahra ta sami Abban Sadik din ta ce masa ya je ya turo musu Aisha saboda aiki yayi yawa. Take ya tashi ya nufi gidan.
Tsit gidan kamar babu kowa, don haka ya wuce daki. Tayi dai-dai a kan gado tana baccinta don ko motsinsa bata ji ba, saida yayi gyaran murya ya zauna a gefen gadon sannan ta farka.
Ta mutssike idonta tace
‘A’a sannu da zuwa.’
Bayan ya amsa yace
‘Lafiya dai ko, anata aiki ashe kina nan kina bacci.’
Ta yatsina fuska tana daga kwance
‘Jiri naji yana kwasata ga kaina yana ciwo shi yasa na zo na kwanta, ka san zazzabin nan ba wai ya gama sakina bane.’
‘Eh hakane.’
Ya kai hannu ya taba wuyanta
‘To kin sha Panadol?’
‘Eh, na sha kafin na kwanta da yake ban dade da kwantawa ba ka shigo.’
‘Ok, to sannu. Kwanta, bari naje sai nayi musu bayani.’
Yayi mata sallama ya fice.
Yana shiga ya wuce falo, don haka mommy ta bishi. Yana kokarin kunna TV tace
‘Abban Sadik lafiya dai Aishan bata dawo ba?’
‘Uh, bata jin dadi ne. Jiri take da ciwon kai kin san bata gama warwarewa ba tayi zazzabi kwanan na.’
Ta hadiye malolon da ya taso mata ta yage baki tace
‘Mhmm! Ko dai kanwata ciki ne da ita ne ake mana laulayi a fakaice.’
Yayi dariya yana shafa kai
‘A’a Babu wannan zancen tukunna, zazzabi ne dai kawai.’
Suka dan taba hira sannan ta tashi ta wuce dakinta, tana shiga ta zauna a gefen gado cike da damuwa; tabbas cikine da Aisha don jiyan ma tana kula da yanda take abubuwa jikinta babu kwari. Tab, ya za ayi ta bari a haihu da mijinta, gashi ta cika gida da yara mata yanzu idan Aishan ta haifi maza uku ko mutuwa yayi sai ta fita gadon arzikin da aka tara da ita. Gaskiya ba zata yarda ba.
Ta shafa hannunta inda aka saka mata inplant na family planning; tabbas da an koma aiki zata je a cire mata wannan abun don ya zama ko da bata sami hanyar lalata cikin Aisha ba to sai dai suyi haihuwar tare. Ba zata sha wahalar talaucin Yusuf ba kuma ya tara dukiya a fi ta gado. Haka ta zauna tayi ta tunani har saida Nana ta shigo kiranta ta sanar da ita an sauke wani ta zo ta nuna wanda za dora sannan ta taso ta fito.
Zuwa la’asar sun gama soya duk naman da za a soya, sai su Jummai da suke ta faman gyara wajen. Danyen naman kuma duk an lode a babbar freezer.
A falon kasa ta zauna ta dibarwa Hajiya nata naman cikin wata babbar roba mai murfi! Duk da Hajiyan ma ya yanka mata rago a gidanta amma haka suka saba sai an kai mata. Ta sami ‘yan bakaken ledodi ta zubawa su Jummai nasu tunda dukansu ta basu danye da yawa sun kai gida sannan kuma biyansu zata yi kudin aikinsu.
Ta dauko kwanon samira mai kamar girman langa tuwo da miya ta zuba naman har ta cika sannan ta rufe sannan ta dauko roba irin ta take away din nan ta zuba kayan ciki ta rufe.
Ta dubi Rukayya wadda take zaune tana ta cin naman tace
‘Rukayya dauki ki kaiwa matar ubanku.’
Tace
‘Anti Aisha?’
A fusace mommyn tace
‘Ba ita ba ni, kuma idan kin je ki zauna tunda uwarkice.’