Sashe 84
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daga nan falon inda su Jummai suke zaune da yaran suka jiyo sallamar namiji daga falon kasa. Jummai ta mike ta ajiye Sumayya tana share hawaye ta fice daga falon. Jimawa kadan ta dawo saman, ta karewa yaran kallo; yanda suke a gigice gaba daya bata ga alamar akwai wanda zai iya kirawo mata Abban ba don haka ta wuce ta kwankwasa kofar dakin nasa.
Ya bude yana share ruwan alwalar da yake fuskarsa, yana budewa tace
'Malam Liman ne a falon kasa da mutane suna magana.’
Ya daga mata kai ya koma ciki.
Yana shiga ya dauki wayarsa ya kirawo Aisha ya sanar da ita halin da ake ciki, Bai saurari tambayoyin da take yi masa ba ya ajiye wayar ya fito ya nufi falon kasa. A nan falon Abban ya zauna shi da su Malam Liman suna jajantawa suna jiran isowar Yaya Muhammadu da Yaya Bello.
Basu dade da zama ba Rukayya ta shigo, wadda Malam Ali ne ya koma makaranta ya daukota da ya fahimci abinda yake faruwa. Bai gaya mata abinda ya faru ba don haka da ta hango Abba a falo sai ta dafe kirji tayi dan gajeran murmushi, ta kasa magana domin ta kula zaman nasu ba na lafiya bane don haka da gudu ta haye sama.
Yanda ta ga Yusra a kashingide kanta babu dankwalu da Mama zaune a kusa da ita ya sa ta karasa falon da gudu. Ta zube a gaban Yusra ta dafa ta tana haki tace
'Yaya Yusra me ya sameki? Ina Mommy?’
Yusran ta kara rushewa da kuka ta matso ta rungume Rukayyan tana fadin
'Mommy ta mutu Rukayya, ta mutu ta barmu.’
Da karfi Rukayyan ta banbare Yusra daga jikinta ta tureta, ta fara bin fuskokin ‘yan uwanta da kallo. Ta kama hannun Mama wanda yake dafe da cinyar Yusra yayinda ta sa hannunta na hagu ta dafe kirjinta tana fitar da hawaye tana fadin
'Mama ai Mommy tana nan ko?’
Kafin a bata amsa numfashinta ya fara yin sama don haka Mama ta saki Yusra ta dafe Rukayya tana umartar Jummai ta debo ruwa.
A daidai nan Saddiku ya shigo falon; wanda tare da Yaya Bello suka zo gidan. Ya kare musu kallo na dan lokaci da jajayen idanunsa. Kai tsaye ya shige dakin Mommy. Kallo daya yayi mata ya tabbatar ta mutu, nan ya tsuguna a gaban gadon yana kallon gawar yana fitar da hawaye.
Daidai lokacin da aka fara samo kan Rukayya a lokacin Aisha ta shigo falon saman. Kusa da Jummai ta karasa tana fadin
'Jummai me yake faruwa ne ban gane bayanin Abban ba.’
Cikin hawaye Jummai tace
'Wallahi Anti ni yau ko haduwa bamuyi da Mommy ba, Yusra tace min bata jin dadi ta kwanta. Muna kasa ni da Yusra muna hidimar mu Yusran ta shigo ta koma tana ihu Mommy babu.’
'Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun.’
Ta tashi ta karasa kusa da Rukayya wadda Mama take kokarin samo kanta, tana tsugunawa a wajen Rukayyan ta fado jikinta ta rushe da kuka tana fadin
'Anti Mommy! Mammy ta tafi ta barmu!’
Rungumeta tayi itama ta fashe da kuka tana bin yaran da kallo na tausayi yayinda rasuwar mahaifinta ta dawo mata sabuwa, don a lokacin bata fi shekarun Rukayyan ba.
Jimawa kadan ‘yan uwan Zahran suka shigo, su Yaya Murja suka zauna nan wajen yaran yayinda su Yaya Muhammad suka shigo suka duba gawar.
Nan da nan aka sauka da ita falon kasa inda a nan ne su Yaya Murja zasu yi mata wanka da sutura da taimakon malamai mata guda biyu da Malam Liman ya kirawo domin wankan.
………
Kafin wani lokaci gida ya dinke da mutane. Nan da nan aka yi mata sutura maza suka dauka aka nufi masallaci domin yin Sallah saboda can ya dan fi sarari domin babu laifi ta sami mutane.
Ana idar da sallah aka kwasa aka tafi makabarta.
Abba da Saddiku suna kan gaba an kama gawa za a saka a rami Saddiku ya saki ya dafe kai, wani daga gefe yace
'Subhanallah! Ku rikeshi zai fadi.’
Nan da nan aka dafeshi, aka karasa sakata. Shima Abban da kyar ya jure tsayuwar saboda yanda kansa yake sarawa. Aka sakata aka rufe mutane suka tattaro suka dawo gida.
Haka aka cigaba da karbar gaisuwa. Itama Aisha hutun aiki ta dauka don a gidan makokin take wuni sai dare take komawa gidanta.
A hankali har aka kwana uku. Ranar kwana uku bayan sallar isha'i ana zaune a falon kasa Suwaiba kanwar Zahran ta dubi Yaya Murja tace
'Yaya ba zaki tafi da Sumayya ba kuwa? Ni nayi nayi da ita tace ba zata bini ba kuma wallahi tunda akayi rasuwarnan fa bana jin ta ci abincin kirki.’
Kafin ayi magana Sumayya ta noke a bayan Rukayya tace
'Ni ba zani ba.’
Aisha ta mika mata hannu ta janyota tana fadin
'Wajena zaki kwana ko?’
Ta daga kai alamar eh. Aishan ta dubi Yaya Murja tace, bari a jima kadan idan muka je can sai taci abincin.
Wajen karfe tara Aisha ta mike ta ja hannun Sumayya da Ummi ta yiwa su Yaya Murja sallama ta fice.
Cikin hanzari Yusra tabi bayansu. Motsin da Aishan taji ya sa ta juya, ganin Yusra ya sa ta tsaya don ta zata wani abun zata fada ko ta bawa ‘yan uwanta.
Ta matso dab da Aishan ta sha gabanta a lokacin da Ummi da Sumayya har sun kusa isa gate don haka suka tsaya daga nan.
Murya kasa-kasa cikin gadara Yusran ta kalli Aisha tar tace
'Ina ruwanki da su da zaki tafi dasu?’
Da mamaki Aishan ta bude baki zatayi magana Yusran ta daga mata hannu ta cigaba
'Ki bar ganin Mommy ta rasu ki zata zaki maye gurbinta, baki isa ba kuma ba zaki taba isa ba. Nan ba gidanki bane kada ma ki taba tunanin zan barki ki shiga dakin uwata wallahi kin yi kadan, kuma idan wani abu ya sami su Ummi wallahi sai kin gwammace zama da Mommy da zama da ni. Eye service kawai.’
Kafin Aishan tace wani abu Yusran ta wuce ta koma ciki ta barta da baki a bude tana mamaki. Sai da Ummi ta gaji ta dawo ta taba Aishan sannan ta tuna ya kamata su tafi ne.
Ta ja yaran suka fice tunani kala-kala yana yawo a kwakwalwarta.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
41
Ranar da Zahra ta kwana hudu da rasuwa bayan azahar Abba ya sallami mutane, ya sanar da su Yaya Muhammad an tashi daga makoki. A cikin gida ma an sanar da mata don haka nan take aka fara watsewa, itama Amina wadda da ita aka yi zaman kwanaki ukun tayi musu sallama ta tafi. Zuwa la'asar ya zama gidan babu kowa sai Yaya Jummai da Rahma wadanda suka ce sai washegari zasu tafi inda zasu bar yaran da Goggo Binta wadda goggon su Zahran ce; idan an yi kwana bakwai ita kuma zata tafi.
—----
Ranar kwana biyar gidan ya dan sami natsuwa domin mutane sun yi saukin zama, sai dai da an zo babu dadewa ayi musu gaisuwa a tafi. Yaran gaba dayansu suna cikin tsananin damuwa, musamman masu wayon daga kan Saddiku zuwa Nana. Ummi da Sumayya dai suna dan sakewa sai dai tun ranar da aka kwana hudu Yusra ta hansu bin Aisha idan ta shigo don haka suka rage samun wanda zai saka su a gaba su ci abinci.
Abba yana kokarin kulawa da su don bai koma aiki ba, sai dai shima a cikin damuwar yake wuni. Ya kasa gane abinda yafi yi masa zafi a ransa; mutuwar Zahra ko kuma halin maraicin da yaransa suka shiga. Yana iya kokarinsa wajen basu hakuri sannan kuma ga Goggo Binta ma tana kokari amma duk da haka da damuwa yake ganinsu.
Bayan an idar da sallar isha'i sai da ya siyowa Ummi yoghurt sannan ya shiga gidan. Rukayya ya samu a falo tana kwance kamar mai bacci, sai dai yana shiga falon ta tashi zaune. Bayan ta amsa sallamarsa tayi masa sannu da zuwa. Ya mika mata ledar yoghurt din yace ta kaiwa Goggo nata sannan ta raba sauran ita da ‘yanuwanta.
Ta karba ta nufi daki domin kaiwa Goggo nata.
Tana karba ya wuce sama, kai tsaye dakinsa ya shige ya turo kofa ya zauna a gefen gado yana tunani. Bai dade da zama ba ya dauki mukullinsa ya fito ya rufe dakin; sai da ya leka dakin Sadik ya sanar da shi kada ya rufe gidan don yanzu zai dawo sannan ya fita.
Gidan Aisha ya nufa; tun ranar da akayi rasuwar rabon da ya shiga gidan nata; sai dai kawai yana ganinta a gidan Zahra. Yau ne kawai zai ce bai ganta a gidan ba.
Da sallama ya shiga falon, tana zauna a kan kujerar zaman mutum uku da waya a hannunta yayinda TV take kunne. Bayan tayi masa sannu da zuwa ya zauna, ta wuce kicin ta dauko masa ruwan sanyi. Ta zuba masa ruwan a kofi sannan ta zauna a gefensa.
Suka gaisa ta sake yi masa gaisuwa; bayan ya amsa tace
'Ya yaran?’
Cike da damuwa yace
‘Alhamdulillah. Yau ban ji ki a cikin gidan ba.’
Ta kawar da kai tana dan gatsina fuska tace
‘Kaina ne yake ta ciwo tun asuba, shi yasa tun safe da na shiga na ga basa bukatar komai na dawo na dan kwanta.’
Suka yi shiru gaba dayansu kowa da abinda yake ransa.
Ba wai ciwon kai ne ya hanata zama a gidan ba; ta dai gaji ne da yanda Yusra take yar mata da maganganu tana kokarin sai ta tsokaneta sun yi fada. Tunda Yaya Murja ta tafi Yusran ta daina raga mata sai dai idan bata shiga gidan ba, dama kuma ko da ana zaman makokin ma tana kula da yanda Yusra da Nana basa gaisheta sai dai idan ita ta yi musu gaisuwa. Don haka ma ita a yanda ta shiga yau da safen ta yanke ba zata sake shiga ba sai an kwana biyu.
Abban ne ya mika hannunsa ya shafi kumatunta yana murmushi yace
'To tunanin ya isa haka.’
Ya bude yana share ruwan alwalar da yake fuskarsa, yana budewa tace
'Malam Liman ne a falon kasa da mutane suna magana.’
Ya daga mata kai ya koma ciki.
Yana shiga ya dauki wayarsa ya kirawo Aisha ya sanar da ita halin da ake ciki, Bai saurari tambayoyin da take yi masa ba ya ajiye wayar ya fito ya nufi falon kasa. A nan falon Abban ya zauna shi da su Malam Liman suna jajantawa suna jiran isowar Yaya Muhammadu da Yaya Bello.
Basu dade da zama ba Rukayya ta shigo, wadda Malam Ali ne ya koma makaranta ya daukota da ya fahimci abinda yake faruwa. Bai gaya mata abinda ya faru ba don haka da ta hango Abba a falo sai ta dafe kirji tayi dan gajeran murmushi, ta kasa magana domin ta kula zaman nasu ba na lafiya bane don haka da gudu ta haye sama.
Yanda ta ga Yusra a kashingide kanta babu dankwalu da Mama zaune a kusa da ita ya sa ta karasa falon da gudu. Ta zube a gaban Yusra ta dafa ta tana haki tace
'Yaya Yusra me ya sameki? Ina Mommy?’
Yusran ta kara rushewa da kuka ta matso ta rungume Rukayyan tana fadin
'Mommy ta mutu Rukayya, ta mutu ta barmu.’
Da karfi Rukayyan ta banbare Yusra daga jikinta ta tureta, ta fara bin fuskokin ‘yan uwanta da kallo. Ta kama hannun Mama wanda yake dafe da cinyar Yusra yayinda ta sa hannunta na hagu ta dafe kirjinta tana fitar da hawaye tana fadin
'Mama ai Mommy tana nan ko?’
Kafin a bata amsa numfashinta ya fara yin sama don haka Mama ta saki Yusra ta dafe Rukayya tana umartar Jummai ta debo ruwa.
A daidai nan Saddiku ya shigo falon; wanda tare da Yaya Bello suka zo gidan. Ya kare musu kallo na dan lokaci da jajayen idanunsa. Kai tsaye ya shige dakin Mommy. Kallo daya yayi mata ya tabbatar ta mutu, nan ya tsuguna a gaban gadon yana kallon gawar yana fitar da hawaye.
Daidai lokacin da aka fara samo kan Rukayya a lokacin Aisha ta shigo falon saman. Kusa da Jummai ta karasa tana fadin
'Jummai me yake faruwa ne ban gane bayanin Abban ba.’
Cikin hawaye Jummai tace
'Wallahi Anti ni yau ko haduwa bamuyi da Mommy ba, Yusra tace min bata jin dadi ta kwanta. Muna kasa ni da Yusra muna hidimar mu Yusran ta shigo ta koma tana ihu Mommy babu.’
'Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun.’
Ta tashi ta karasa kusa da Rukayya wadda Mama take kokarin samo kanta, tana tsugunawa a wajen Rukayyan ta fado jikinta ta rushe da kuka tana fadin
'Anti Mommy! Mammy ta tafi ta barmu!’
Rungumeta tayi itama ta fashe da kuka tana bin yaran da kallo na tausayi yayinda rasuwar mahaifinta ta dawo mata sabuwa, don a lokacin bata fi shekarun Rukayyan ba.
Jimawa kadan ‘yan uwan Zahran suka shigo, su Yaya Murja suka zauna nan wajen yaran yayinda su Yaya Muhammad suka shigo suka duba gawar.
Nan da nan aka sauka da ita falon kasa inda a nan ne su Yaya Murja zasu yi mata wanka da sutura da taimakon malamai mata guda biyu da Malam Liman ya kirawo domin wankan.
………
Kafin wani lokaci gida ya dinke da mutane. Nan da nan aka yi mata sutura maza suka dauka aka nufi masallaci domin yin Sallah saboda can ya dan fi sarari domin babu laifi ta sami mutane.
Ana idar da sallah aka kwasa aka tafi makabarta.
Abba da Saddiku suna kan gaba an kama gawa za a saka a rami Saddiku ya saki ya dafe kai, wani daga gefe yace
'Subhanallah! Ku rikeshi zai fadi.’
Nan da nan aka dafeshi, aka karasa sakata. Shima Abban da kyar ya jure tsayuwar saboda yanda kansa yake sarawa. Aka sakata aka rufe mutane suka tattaro suka dawo gida.
Haka aka cigaba da karbar gaisuwa. Itama Aisha hutun aiki ta dauka don a gidan makokin take wuni sai dare take komawa gidanta.
A hankali har aka kwana uku. Ranar kwana uku bayan sallar isha'i ana zaune a falon kasa Suwaiba kanwar Zahran ta dubi Yaya Murja tace
'Yaya ba zaki tafi da Sumayya ba kuwa? Ni nayi nayi da ita tace ba zata bini ba kuma wallahi tunda akayi rasuwarnan fa bana jin ta ci abincin kirki.’
Kafin ayi magana Sumayya ta noke a bayan Rukayya tace
'Ni ba zani ba.’
Aisha ta mika mata hannu ta janyota tana fadin
'Wajena zaki kwana ko?’
Ta daga kai alamar eh. Aishan ta dubi Yaya Murja tace, bari a jima kadan idan muka je can sai taci abincin.
Wajen karfe tara Aisha ta mike ta ja hannun Sumayya da Ummi ta yiwa su Yaya Murja sallama ta fice.
Cikin hanzari Yusra tabi bayansu. Motsin da Aishan taji ya sa ta juya, ganin Yusra ya sa ta tsaya don ta zata wani abun zata fada ko ta bawa ‘yan uwanta.
Ta matso dab da Aishan ta sha gabanta a lokacin da Ummi da Sumayya har sun kusa isa gate don haka suka tsaya daga nan.
Murya kasa-kasa cikin gadara Yusran ta kalli Aisha tar tace
'Ina ruwanki da su da zaki tafi dasu?’
Da mamaki Aishan ta bude baki zatayi magana Yusran ta daga mata hannu ta cigaba
'Ki bar ganin Mommy ta rasu ki zata zaki maye gurbinta, baki isa ba kuma ba zaki taba isa ba. Nan ba gidanki bane kada ma ki taba tunanin zan barki ki shiga dakin uwata wallahi kin yi kadan, kuma idan wani abu ya sami su Ummi wallahi sai kin gwammace zama da Mommy da zama da ni. Eye service kawai.’
Kafin Aishan tace wani abu Yusran ta wuce ta koma ciki ta barta da baki a bude tana mamaki. Sai da Ummi ta gaji ta dawo ta taba Aishan sannan ta tuna ya kamata su tafi ne.
Ta ja yaran suka fice tunani kala-kala yana yawo a kwakwalwarta.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
41
Ranar da Zahra ta kwana hudu da rasuwa bayan azahar Abba ya sallami mutane, ya sanar da su Yaya Muhammad an tashi daga makoki. A cikin gida ma an sanar da mata don haka nan take aka fara watsewa, itama Amina wadda da ita aka yi zaman kwanaki ukun tayi musu sallama ta tafi. Zuwa la'asar ya zama gidan babu kowa sai Yaya Jummai da Rahma wadanda suka ce sai washegari zasu tafi inda zasu bar yaran da Goggo Binta wadda goggon su Zahran ce; idan an yi kwana bakwai ita kuma zata tafi.
—----
Ranar kwana biyar gidan ya dan sami natsuwa domin mutane sun yi saukin zama, sai dai da an zo babu dadewa ayi musu gaisuwa a tafi. Yaran gaba dayansu suna cikin tsananin damuwa, musamman masu wayon daga kan Saddiku zuwa Nana. Ummi da Sumayya dai suna dan sakewa sai dai tun ranar da aka kwana hudu Yusra ta hansu bin Aisha idan ta shigo don haka suka rage samun wanda zai saka su a gaba su ci abinci.
Abba yana kokarin kulawa da su don bai koma aiki ba, sai dai shima a cikin damuwar yake wuni. Ya kasa gane abinda yafi yi masa zafi a ransa; mutuwar Zahra ko kuma halin maraicin da yaransa suka shiga. Yana iya kokarinsa wajen basu hakuri sannan kuma ga Goggo Binta ma tana kokari amma duk da haka da damuwa yake ganinsu.
Bayan an idar da sallar isha'i sai da ya siyowa Ummi yoghurt sannan ya shiga gidan. Rukayya ya samu a falo tana kwance kamar mai bacci, sai dai yana shiga falon ta tashi zaune. Bayan ta amsa sallamarsa tayi masa sannu da zuwa. Ya mika mata ledar yoghurt din yace ta kaiwa Goggo nata sannan ta raba sauran ita da ‘yanuwanta.
Ta karba ta nufi daki domin kaiwa Goggo nata.
Tana karba ya wuce sama, kai tsaye dakinsa ya shige ya turo kofa ya zauna a gefen gado yana tunani. Bai dade da zama ba ya dauki mukullinsa ya fito ya rufe dakin; sai da ya leka dakin Sadik ya sanar da shi kada ya rufe gidan don yanzu zai dawo sannan ya fita.
Gidan Aisha ya nufa; tun ranar da akayi rasuwar rabon da ya shiga gidan nata; sai dai kawai yana ganinta a gidan Zahra. Yau ne kawai zai ce bai ganta a gidan ba.
Da sallama ya shiga falon, tana zauna a kan kujerar zaman mutum uku da waya a hannunta yayinda TV take kunne. Bayan tayi masa sannu da zuwa ya zauna, ta wuce kicin ta dauko masa ruwan sanyi. Ta zuba masa ruwan a kofi sannan ta zauna a gefensa.
Suka gaisa ta sake yi masa gaisuwa; bayan ya amsa tace
'Ya yaran?’
Cike da damuwa yace
‘Alhamdulillah. Yau ban ji ki a cikin gidan ba.’
Ta kawar da kai tana dan gatsina fuska tace
‘Kaina ne yake ta ciwo tun asuba, shi yasa tun safe da na shiga na ga basa bukatar komai na dawo na dan kwanta.’
Suka yi shiru gaba dayansu kowa da abinda yake ransa.
Ba wai ciwon kai ne ya hanata zama a gidan ba; ta dai gaji ne da yanda Yusra take yar mata da maganganu tana kokarin sai ta tsokaneta sun yi fada. Tunda Yaya Murja ta tafi Yusran ta daina raga mata sai dai idan bata shiga gidan ba, dama kuma ko da ana zaman makokin ma tana kula da yanda Yusra da Nana basa gaisheta sai dai idan ita ta yi musu gaisuwa. Don haka ma ita a yanda ta shiga yau da safen ta yanke ba zata sake shiga ba sai an kwana biyu.
Abban ne ya mika hannunsa ya shafi kumatunta yana murmushi yace
'To tunanin ya isa haka.’