Sashe 36
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
‘Ai shikenan.’
…………
Har karfe goma na dare yana zaune shi kadai a dakinsa, babu abinda yakeyi kawai tunani kala-kala suke yawo a kwakwalwarsa. Tunda ya zauna yake kallon wayarsa yana jiran Aisha ta kirawoshi tace masa ta dawo amma har yanzu shiru. Ya sake kallon lokaci nan take ya lalubo lambarta ya danna mata kira. Wayar tana dab da tsinkewa ta amsa, yace
‘A’eesh, kin dawo kuwa?’
‘Eh, tun dazu har ma na kwanta.’
‘Ok bari na rako miki Rukayyan.’
‘Ka barta kawai dare yayi, ma hadu da safe.’
Sukayi shiru na dan lokaci kadan, ya ma rasa me zai ce don ya san tabbas bai kyautawa Aisha ba. Ya gaji da sauraron numfashinsu yace
‘Zaki iya kwana ke kadai to?’
‘Eh.’
Ya fahimci gajiyawa a cikin muryarta kuma shima bashi da sauran abinda zai ce mata don haka yayi mata sai da safe, suka ajiye waya.
Yanda Aisha ta kwana tana fushi da shi haka ya kwana yana fushi da Zahra, duk yanda ta kai ga shisshige masa ya ki ya saurareta har ta gaji ta kyaleshi.
Ko da gari ya waye tun wajen tara saura ya gama shiryawa don yana da daurin aure, yana fatan kafin lokacin Aisha ta tashi; don bata tashi da wuri ranakun Asabar da Lahadi; in ya so sai ya shiga wajenta kafin ya wuce.
Yana tsaye a gaban mudubi yana gyara karin hularsa Mommy ta shigo dakin, ta wuce ta zauna a kan gado don ta kula har yanzu fushi yakeyi.
Ya gama gyara hular ya daura agogonsa ya dauki mukullan motarsa tare da wayarsa da suke ajiye a kan mudubin ya dubeta yace
‘Kada ki ajiye min abincin rana a gidan Hajiya zan ci, sai da yamma zan dawo.’
Da murmushi a fuskarta tace
‘To, ka gaida Hajiya da mutanen gidan.’
Ba zata iya hakura ba don tana ganin wannan itace damarta ta karshe idan bata yi masa magana yanzu ba abun yana kara wucewa haka za ayi ta cutarsu ita da yaranta. Don haka har ya juya ya nufi kofa ta tashi ta murmushi ta biyo shi, sai da ta zo dab dashi ta kirawo sunansa
‘Abban Sadik.’
Ya juyo ya bita da kallo alamar yana sauraronta, ta dan bata rai sannan tace
‘Mu sai yaushe za a kawo mana namu kajin ni da yarana?’
Da mamaki a fuskarsa yake kallonta yace
‘Kaji kuma? Wannan watan da akayi cefane ba a kawo harda kaji bane? Ko da yake idan ma sun kare ai sai kuci nama ko kifi tunda duk an kawo ko?’
Ta kara shan kunu
‘Kajin da aka kaiwa Aisha ta soyawa yara su nake magana, wadannan ma ai sun gani ko ladan ganin ido ai sai a bamu.’
Binta kawai yake da kallo yana mamaki, ya gyara tsaiwa ya kare mata kallo. Ya ma rasa me zai ce mata, yace
‘Allah ya sauwake. In dai kajin da Aisha ta soyawa yara ne ba ni na saya mata ba, kudinta ta sa ta siyo don ta soyawa yaranta kuma da ta soya duk yaron da yake cikin gidan saida ta bashi. Idan kina da kudi kema ki bayar a sayo miki kaji ki soya ku cinye ko kuma ragowar na miyar ki soya muku idan kun cinye sai kiyi miyar lami.’
Kafin tace wani abu ya juya ya fice; idonsa har rufewa yake saboda takaici da mamakin Zahra; Yaushe ta zama haka ne? Dama tura yaran take su gano mata abinda akeyi a gidan Aishan kenan?
A can gidan Aisha ma bai sami yanda yake so ba don haka ranar dai haka ya fita zuciyarsa a jagule.
_
Duk wanda Zahra take bi bashi wannan watan saida ta kirawo su, don haka sosai aka biyata bashi. Sai dai duk yanda ta so kudaden da ta hada su kai dubu dari uku basu kai ba, gashi bazata iya tambayar Abban ba don har yanzu bai koma kamar da da ita ba.
Ta riga ta tsarawa Abba cewa akwai kawarsu ita da Amina wadda mijinta ya rasu, don haka zasu je mata gaisuwa can Gaya. Ko da yace mata Malam Sule ya kaita sai ta ce masa da motar Amina zasu je don su uku zasu je. Don haka ya bata izinin zuwa.
__
Ranar Lahadi suka yi shirin tafiya Gaya, tun karfe takwas da rabi na safe tasa Malam Sule yazo ya kaita gidan Amina. Daga can suka kama hanya a motar Aminan.
Idan aka shiga Gayan ma sai an nufi can bayan gari kamar za a fita daga garin sannan a hau wani kwararo. Dan karamin kauye ne, duk da gidan ba wani babba bane amma dai yafi duk gidajen da suke kewaye da shi girma.
A share farfajiyar gidan take tsaf ga rumfuna kamar guda hudu wanda kowacce cike take da almajirai ana ta karatu.
Malam ya san da zuwansu don haka motarsu tana tsayawa wani matashi a cikin almajiran ya taso da hanzari ya taresu. Ya jagorancesu cikin gida.
Suna shiga soron farko ya nuna musu kofar wani daki yace
‘Hajiya ku shiga nan Malam yana jiranku.’
Suka daga labule suka shige da sallama yayinda shi kuma almajirin Malam ya juya ya koma waje.
Da fara'a Malam ya taresu; su biyu ne a dakin shi da wani babban almajirinsa wanda shi yayi yawo da yawa don haka ya tara ilimi sosai musamman irin wannan na kauce hanya.
A kan dadduma suke zaune, yaron Malam ya nuna musu daya daddumar wadda take dama da Malam yace su zauna. Akwai ruwan roba daga gefe guda a dakin ya balle ledar ya dauko guda biyu ya ajiye musu a gabansu.
Suka gaisa da Malam, yayi gyaran murya ya dubi Zahra
‘Hajiya Allah ya nufa kin zo kenan?’
‘Wallahi Malam.’
‘To yanzu wanne za ayi?’
Nan ta koro masa bayani daga karshe tace
‘Gaskiya Malam ni dai so nake a rabasu kawai, auren ya rabu muyi zamanmu ni da shi.’
Malam Hatimu ya dubi yaron Malam yace
‘Ka ji bayani.’
Ya gyada kai ya mike ya dauko wata tsummar fata a nannade. Ya dawo ya zauna a gaban Malam ya kwance fatar ya shimfida, yashi ne mai laushin gaske a kan fatar, ya gyara mata zama ya sake baza yashin. Ya rufe ido ya fuskanci sama yayi wani karatu wanda duka basa ji saidai suna ganin motsin bakinsa. Jimawa kadan ya sauke fuskarsa yayi busa a kan yashin a hankali. Ya sa yatsansa manuniya yayi digo guda uku a kan yashin ya dauke hannunsa ya zubawa yashin ido.
A take aka fara jan layi daga kan digon nan guda uku; ba shi yake jan layi ba kuma basu ga alamar akwai wani wanda yake jan layi ba.
Tun kafin layikan suyi nisa aka daina jan daya, sai guda biyun aka cigaba da ja har aka kai karshen fatar aka dire kasa har zuwa inda birbishin yashin ya kare.
Yaron Malam ya dubi Malam Hatimu yace
‘Ka gani Malam, Yusufa da Aisha tafiyarsu mai nisan gaske ce. Ko da zamu iya raba auren nan to sai an yi aiki da gaske wanda yake butara lokaci don sai dai na kaiwa Malam na gabas, kuma abun zai dauki akalla watanni takwas; amma komai fitnarsu za a rabasu.’
Malam Hatimu ya dubi Zahra yace
‘Kin ji ko Hajiya.’
Ta kara zare ido ta dubi Amina suka yi shiru na dan lokaci. Jim kadan tace
‘Malam to yanzu babu wani abun da za a iya yi a kai? Ni dai ko basu rabu ba ina so ya daina kulata, ta zauna a matarsa amma ya kasa nutsuwa da ita sai ya zo wajena.’
Malam Hatimu ya dubi yaron Malam yace
‘Kaji Yaron Malam.’
‘Wannan mai sauki me Malam, in dai da kayan aiki wannan ba zai dauki sati biyu ba ma an gama in dai sunyi abinda muka ce da kanshi zai gujeta.’
Zahra tace
‘Hakan ma yayi Malam, in ya so wancan babban aikin shima sai a fara tanadinsa don gaskiya zan fi so a rabasu.’
Yaron Malam ya matsa kusa da Malam sukayi kus-kus, Malam ya dubeta yace
‘Naira dubu dari biyu shine kudin aikinki Hajiya, da zarar kin kawo za a fara aiki.’
Ta dubi Amina wadda kudin suke jakarta, nan take ta zaro kudi suka kirga dubu dari biyu suka ajiye a gaban Malam.
Yaron Malam ya dauka ya kirga, bayan ya gama kirgawa ya mayar ya ajiye sannan ya dubi Malam yace
‘Hakane Malam, a daren yau za a fara aiki idan an gama sai ayi musu waya su zo su karba.’
Suka amsa tare da yiwa Malam sallama suka kamo hanya.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
22
Duk da Aisha tace ta hakura ba fushi takeyi da shi ba amma shi dai bai gamsu ba, yana ganin kamar har yanzu bata huce ba don taki sakewa da shi.
Ya santa da son ice cream don haka ranar da zai koma kwananta yana idar da sallar isha’i ya tafi neman ice cream. Saida ya fara tsayawa a Green Park ya siyo gasasshen kifi da chips irin wanda take so sannan ya siyo ice cream din ya dawo.
A bakin gate din gidan Zahra yayi parking ya fitar da nasu ita da Yara ya kai musu, bayan ya fito ya ja motar ya wuce gidan Aishan.
Tana kwance a falo a kan doguwar kujera ya shiga, bayan ya amsa sannu da zuwa ta ya wuce ya ajiye ledodin a kan dining table, ya dawo ya zauna a kusa da ita yana duban fuskarta. Yace
‘Yaya dai? Jikin ko garin?’
Tayi murmushi
‘Babu daya, kwanciya dai nayi kawai ashe bacci ya daukeni don ban ma san sun kawo wuta ba.’
‘Kinyi abincin dare?’
‘Eh, nayi tuwo miyar kuka.’
‘Yauwa sai a rufe mana shi mayi dumame don ga kifi da chips na siyo, harda ice cream.’
Tayi murmushi tace
‘Ai kuwa ka taimaka min don wallahi kwadayi nake ji kamar naci babu.’
Yayi dariya ya mike yana fadin
‘To sai ki tashi ki fara gashi nan, ni bari na canzo kaya.’
Ya shige daki, ita kuma ta karasa gaba dining table din ta duba kayan da ya siyo.
…………
Har karfe goma na dare yana zaune shi kadai a dakinsa, babu abinda yakeyi kawai tunani kala-kala suke yawo a kwakwalwarsa. Tunda ya zauna yake kallon wayarsa yana jiran Aisha ta kirawoshi tace masa ta dawo amma har yanzu shiru. Ya sake kallon lokaci nan take ya lalubo lambarta ya danna mata kira. Wayar tana dab da tsinkewa ta amsa, yace
‘A’eesh, kin dawo kuwa?’
‘Eh, tun dazu har ma na kwanta.’
‘Ok bari na rako miki Rukayyan.’
‘Ka barta kawai dare yayi, ma hadu da safe.’
Sukayi shiru na dan lokaci kadan, ya ma rasa me zai ce don ya san tabbas bai kyautawa Aisha ba. Ya gaji da sauraron numfashinsu yace
‘Zaki iya kwana ke kadai to?’
‘Eh.’
Ya fahimci gajiyawa a cikin muryarta kuma shima bashi da sauran abinda zai ce mata don haka yayi mata sai da safe, suka ajiye waya.
Yanda Aisha ta kwana tana fushi da shi haka ya kwana yana fushi da Zahra, duk yanda ta kai ga shisshige masa ya ki ya saurareta har ta gaji ta kyaleshi.
Ko da gari ya waye tun wajen tara saura ya gama shiryawa don yana da daurin aure, yana fatan kafin lokacin Aisha ta tashi; don bata tashi da wuri ranakun Asabar da Lahadi; in ya so sai ya shiga wajenta kafin ya wuce.
Yana tsaye a gaban mudubi yana gyara karin hularsa Mommy ta shigo dakin, ta wuce ta zauna a kan gado don ta kula har yanzu fushi yakeyi.
Ya gama gyara hular ya daura agogonsa ya dauki mukullan motarsa tare da wayarsa da suke ajiye a kan mudubin ya dubeta yace
‘Kada ki ajiye min abincin rana a gidan Hajiya zan ci, sai da yamma zan dawo.’
Da murmushi a fuskarta tace
‘To, ka gaida Hajiya da mutanen gidan.’
Ba zata iya hakura ba don tana ganin wannan itace damarta ta karshe idan bata yi masa magana yanzu ba abun yana kara wucewa haka za ayi ta cutarsu ita da yaranta. Don haka har ya juya ya nufi kofa ta tashi ta murmushi ta biyo shi, sai da ta zo dab dashi ta kirawo sunansa
‘Abban Sadik.’
Ya juyo ya bita da kallo alamar yana sauraronta, ta dan bata rai sannan tace
‘Mu sai yaushe za a kawo mana namu kajin ni da yarana?’
Da mamaki a fuskarsa yake kallonta yace
‘Kaji kuma? Wannan watan da akayi cefane ba a kawo harda kaji bane? Ko da yake idan ma sun kare ai sai kuci nama ko kifi tunda duk an kawo ko?’
Ta kara shan kunu
‘Kajin da aka kaiwa Aisha ta soyawa yara su nake magana, wadannan ma ai sun gani ko ladan ganin ido ai sai a bamu.’
Binta kawai yake da kallo yana mamaki, ya gyara tsaiwa ya kare mata kallo. Ya ma rasa me zai ce mata, yace
‘Allah ya sauwake. In dai kajin da Aisha ta soyawa yara ne ba ni na saya mata ba, kudinta ta sa ta siyo don ta soyawa yaranta kuma da ta soya duk yaron da yake cikin gidan saida ta bashi. Idan kina da kudi kema ki bayar a sayo miki kaji ki soya ku cinye ko kuma ragowar na miyar ki soya muku idan kun cinye sai kiyi miyar lami.’
Kafin tace wani abu ya juya ya fice; idonsa har rufewa yake saboda takaici da mamakin Zahra; Yaushe ta zama haka ne? Dama tura yaran take su gano mata abinda akeyi a gidan Aishan kenan?
A can gidan Aisha ma bai sami yanda yake so ba don haka ranar dai haka ya fita zuciyarsa a jagule.
_
Duk wanda Zahra take bi bashi wannan watan saida ta kirawo su, don haka sosai aka biyata bashi. Sai dai duk yanda ta so kudaden da ta hada su kai dubu dari uku basu kai ba, gashi bazata iya tambayar Abban ba don har yanzu bai koma kamar da da ita ba.
Ta riga ta tsarawa Abba cewa akwai kawarsu ita da Amina wadda mijinta ya rasu, don haka zasu je mata gaisuwa can Gaya. Ko da yace mata Malam Sule ya kaita sai ta ce masa da motar Amina zasu je don su uku zasu je. Don haka ya bata izinin zuwa.
__
Ranar Lahadi suka yi shirin tafiya Gaya, tun karfe takwas da rabi na safe tasa Malam Sule yazo ya kaita gidan Amina. Daga can suka kama hanya a motar Aminan.
Idan aka shiga Gayan ma sai an nufi can bayan gari kamar za a fita daga garin sannan a hau wani kwararo. Dan karamin kauye ne, duk da gidan ba wani babba bane amma dai yafi duk gidajen da suke kewaye da shi girma.
A share farfajiyar gidan take tsaf ga rumfuna kamar guda hudu wanda kowacce cike take da almajirai ana ta karatu.
Malam ya san da zuwansu don haka motarsu tana tsayawa wani matashi a cikin almajiran ya taso da hanzari ya taresu. Ya jagorancesu cikin gida.
Suna shiga soron farko ya nuna musu kofar wani daki yace
‘Hajiya ku shiga nan Malam yana jiranku.’
Suka daga labule suka shige da sallama yayinda shi kuma almajirin Malam ya juya ya koma waje.
Da fara'a Malam ya taresu; su biyu ne a dakin shi da wani babban almajirinsa wanda shi yayi yawo da yawa don haka ya tara ilimi sosai musamman irin wannan na kauce hanya.
A kan dadduma suke zaune, yaron Malam ya nuna musu daya daddumar wadda take dama da Malam yace su zauna. Akwai ruwan roba daga gefe guda a dakin ya balle ledar ya dauko guda biyu ya ajiye musu a gabansu.
Suka gaisa da Malam, yayi gyaran murya ya dubi Zahra
‘Hajiya Allah ya nufa kin zo kenan?’
‘Wallahi Malam.’
‘To yanzu wanne za ayi?’
Nan ta koro masa bayani daga karshe tace
‘Gaskiya Malam ni dai so nake a rabasu kawai, auren ya rabu muyi zamanmu ni da shi.’
Malam Hatimu ya dubi yaron Malam yace
‘Ka ji bayani.’
Ya gyada kai ya mike ya dauko wata tsummar fata a nannade. Ya dawo ya zauna a gaban Malam ya kwance fatar ya shimfida, yashi ne mai laushin gaske a kan fatar, ya gyara mata zama ya sake baza yashin. Ya rufe ido ya fuskanci sama yayi wani karatu wanda duka basa ji saidai suna ganin motsin bakinsa. Jimawa kadan ya sauke fuskarsa yayi busa a kan yashin a hankali. Ya sa yatsansa manuniya yayi digo guda uku a kan yashin ya dauke hannunsa ya zubawa yashin ido.
A take aka fara jan layi daga kan digon nan guda uku; ba shi yake jan layi ba kuma basu ga alamar akwai wani wanda yake jan layi ba.
Tun kafin layikan suyi nisa aka daina jan daya, sai guda biyun aka cigaba da ja har aka kai karshen fatar aka dire kasa har zuwa inda birbishin yashin ya kare.
Yaron Malam ya dubi Malam Hatimu yace
‘Ka gani Malam, Yusufa da Aisha tafiyarsu mai nisan gaske ce. Ko da zamu iya raba auren nan to sai an yi aiki da gaske wanda yake butara lokaci don sai dai na kaiwa Malam na gabas, kuma abun zai dauki akalla watanni takwas; amma komai fitnarsu za a rabasu.’
Malam Hatimu ya dubi Zahra yace
‘Kin ji ko Hajiya.’
Ta kara zare ido ta dubi Amina suka yi shiru na dan lokaci. Jim kadan tace
‘Malam to yanzu babu wani abun da za a iya yi a kai? Ni dai ko basu rabu ba ina so ya daina kulata, ta zauna a matarsa amma ya kasa nutsuwa da ita sai ya zo wajena.’
Malam Hatimu ya dubi yaron Malam yace
‘Kaji Yaron Malam.’
‘Wannan mai sauki me Malam, in dai da kayan aiki wannan ba zai dauki sati biyu ba ma an gama in dai sunyi abinda muka ce da kanshi zai gujeta.’
Zahra tace
‘Hakan ma yayi Malam, in ya so wancan babban aikin shima sai a fara tanadinsa don gaskiya zan fi so a rabasu.’
Yaron Malam ya matsa kusa da Malam sukayi kus-kus, Malam ya dubeta yace
‘Naira dubu dari biyu shine kudin aikinki Hajiya, da zarar kin kawo za a fara aiki.’
Ta dubi Amina wadda kudin suke jakarta, nan take ta zaro kudi suka kirga dubu dari biyu suka ajiye a gaban Malam.
Yaron Malam ya dauka ya kirga, bayan ya gama kirgawa ya mayar ya ajiye sannan ya dubi Malam yace
‘Hakane Malam, a daren yau za a fara aiki idan an gama sai ayi musu waya su zo su karba.’
Suka amsa tare da yiwa Malam sallama suka kamo hanya.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
22
Duk da Aisha tace ta hakura ba fushi takeyi da shi ba amma shi dai bai gamsu ba, yana ganin kamar har yanzu bata huce ba don taki sakewa da shi.
Ya santa da son ice cream don haka ranar da zai koma kwananta yana idar da sallar isha’i ya tafi neman ice cream. Saida ya fara tsayawa a Green Park ya siyo gasasshen kifi da chips irin wanda take so sannan ya siyo ice cream din ya dawo.
A bakin gate din gidan Zahra yayi parking ya fitar da nasu ita da Yara ya kai musu, bayan ya fito ya ja motar ya wuce gidan Aishan.
Tana kwance a falo a kan doguwar kujera ya shiga, bayan ya amsa sannu da zuwa ta ya wuce ya ajiye ledodin a kan dining table, ya dawo ya zauna a kusa da ita yana duban fuskarta. Yace
‘Yaya dai? Jikin ko garin?’
Tayi murmushi
‘Babu daya, kwanciya dai nayi kawai ashe bacci ya daukeni don ban ma san sun kawo wuta ba.’
‘Kinyi abincin dare?’
‘Eh, nayi tuwo miyar kuka.’
‘Yauwa sai a rufe mana shi mayi dumame don ga kifi da chips na siyo, harda ice cream.’
Tayi murmushi tace
‘Ai kuwa ka taimaka min don wallahi kwadayi nake ji kamar naci babu.’
Yayi dariya ya mike yana fadin
‘To sai ki tashi ki fara gashi nan, ni bari na canzo kaya.’
Ya shige daki, ita kuma ta karasa gaba dining table din ta duba kayan da ya siyo.