Sashe 58
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tunda aka shigo da keken take so a tayata ta hada amma kowa sai gwasaleta yake yi, Saddiku yana so ya hada mata amma kiri-kiri Mommy tace a dauke keken a ajiye ba za ayi amfani da shi ba sai an siyowa Yusra irinsa. Ita Yusra bata ma sha’awar dinki kwata-kwata, jaka da turaren da aka bawa Rukayyan ya fi tsaye mata a rai saboda tana jin itace babba ita ya kamata a fara bawa, amma da ta sami goyon bayan Mommy sai ta koma jin haushin keken ma. Don ta ciwa kanta alwashin idan dai ba a saya mata irinsa ba sai ta lalata shi.
Ko da suka fita da keken nan ba karamin dadi Rukayya taji ba; don dama tunda taga yanda Mommy take gwalewa ta yanke shawara gidan Antin zata mayar da shi idan ya so in tana can tayi dinki ko idan Amira ta zo.
Bayan ya kaita ya yiwa Aishan sallama kuwa yana fita suka saka keken a gaba ita da Aisha saida suka hada shi wajen dayan dare sannan suka kwanta.
--------
Duk yanda Mommy ta so morewa a wannan daren bata samu ba domin yana dawowa ya rufe gidan ya shige dakinsa ya kulle. Haka ta kwana tana takaicin yanda yake Raina mata hankali.
__
Duk wata tsaraba da Abban ya siyowa yara haka ya tattara ya kulle ya ajiye a gidan Aisha; tunda Zahra ta saka shi a gaba da maganganun nan yace ba zai bayar da tsarabar don haka har abinda ya siyo mata duk ajiyewa yayi. Wasu ma duk sai ya kwashe ya kaiwa mutan gidan Yaya Bello wadanda ba zai iya bayarwa ba kuma kamar computer da wayar da ya siyowa Yusra da niyyar in ta gama SS 3 ya bata duk ya tattara ya ajiye.
Saida sukayi sati da dawowa sanna Zahra ta samu ya dan fara sauraronta, don haka nan da nan ta samu ta sanar da shi ana biki a gidan su Amina zasu je. Ba tare da wata matsala ba ya bata dama.
…..
Kwanan su Abba goma sha uku da dawowa Zahra ta shirya ta fice ranar Alhamis da sunan ta tafi biki, karfe goma na safe suka kama hanyar Doguwa.
Sun ci sa’a wannan zuwan babu kowa a wajen don haka kai tsaye aka kaisu dakin da suka gurfane a gaban bokan.
Bayan sun gama yi masa bayani da sanar da shi Abban ya dawo yayi gyaran murya yace
‘Kudin aiki Naira dubu dari hudu.’
Ya tura musu bakar tasa Zahra ta juye kudin dake cikin jakarta wanda dubu dari biyar ne ta taho da su.
Dariya ta karade dakin. Daga baya bokan yace
‘Ranar Lahadi da daddare zamuyi aiki, ke kuma ki tabbatar ya kwana da janaba a wannan daren. Idan kikayi haka gari yana wayewa ba zai sake tuna wata mata ba.’
Dakin ya sake cika da dariya. Bayan dariyar ta lafa tace
‘Um ba a dakina zai kwana ba ranar Lahadi sai dai litinin.’
Ya saki wata kara wadda har ta firgita su, sannan yace
‘Ba ma aiki ranar litinin, Alhamis da Juma’a . Don haka ranar asabar da daddare ki tabbatar ya kwana da janaba mu kuma za muyi miki aiki.’
‘To hakan yayi.’
Ya ware tafi hannunsa sama, nan da an aka jefo masa wani mulmulallen farin gilas mai fasalin kwai. Ya turowa Zahran yana fadin
‘Ki saka wannan a wannan bakar robar ta gabanki ki rufe, ki nemi waje ko ina ne ki boyeta. Matukar ba a bude wannan robar ba to sai yanda kikayi da Yusuf, domin ko Sallah kika ce kada yayi to bazai yi ba balle wani aiki na duniya.’
Ta karba ta fara kici-kicin sakawa a robar da take gabanta yayinda dakin ya rude da dariya.
‘Ku tafi, ku tafi.’
Haka aka dinga nanata musu har suka fice daga dakin suka kamo hanya.
Abun ya dan so ya tsorata Zahra sai dai idan ta tuna zai manta da Aisha a rayuwarsa sai abun yayi mata dadi. Ta dai san ta kashe kudi da yawa, domin kusan miliyan guda kenan wancan zuwan da wannan. Gashi ragowar kudaden da take shirin karawa a business dinta duk tana ta facaka da su.
……….
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
31
A tsaye take a tsakar dakinta tana tunanin inda zata boye bakar robar nan da boka ya bata. Ta duba robar ba zata shiga bayan wardrobe din ba kuma bata so ta saka ta a cikin wardrobe din saboda waje ne da take yawan budewa. Kayan dakin nata irin Turkish Furniture din nan ne masu girma da nauyi don haka kusan ba a taba motsasu ba tunda aka kafa su. Nan take dabara ta fado mata.
Ta karasa ta ajiye robar a kan durowar gefen gadon sannan ta dage iya karfinta ta daga katifar daga daidai kan gadon, ta daga katakon ma sannan ta dauko robar a hankali ta ajiye a kasan katakon. Ta mayar da komai ta gyara gadonta; a nan kam tana da yakinin babu wanda zai motsa mata gado sai idan itace ta saka kuma babu mai duba mata.
Ta yiwa kanta murmushin jin dadi sannan ta fice daga dakin.
___
Ranar Juma’a ce don haka da yake Yaya Zainab bata zo wa Aisha sannu da zuwa ba sai yau ta zo. Gaba daya ita da su Amira suka zo da yake babu islamiyya.
Lokacin da direbansu ya saukesu a bakin gate din gidan Aisha yayi dai-dai da lokacin da Malam Ali ya kawo su Rukayya da makaranta.
Ummi ce ta tabo Rukayya tace
‘Yaya Rukayya ga kawarki can Amiro ta zo.’
Yusra ta balla musu harara duka su biyun, don haka sukayi shiru.
Har suka shiga gida Rukayya tana tunanin yanda zata samu ta je wajen Amira; tana son taje ta nuna mata keken dinkinta don ita Amiran tana da nata ta ma fi Rukayyan iya dinki, amma ta san ba za a barta taje ba.
Idan Abba ya rakata da daddare ta taya Aishan kwana, da safe idan ta fito suka tafi makaranta to Mommy ta haramta mata komawa gidan har sai wani daren idan Abban yayi magana. Idan bai yi magana ba to ita bata isa tace zata je gidan ba.
Yau din dai haka kawai take so taje gida su dan taba dinki kafin su Amira su tafi.
Ta riga ta fidda rai don in dai Yusra taga fitarta to ta san ko ba gidan Anti Aishan taje ba cewa Mommy zata yi can taje, kuma ta san tabbas sai Mommy ta ci mutuncinta.
Wajen karfe uku babu kowa a falon daga ita sai Ummi, ta mike ta dauki hijabinta. Ummi ma duk da bata san ina zata je ba ta mike tace
‘Yaya Rukayya zan raka ki.’
Don haka ta bita a baya suka wuce.
Suna shiga ta gaida su Anti Aishan a falo ta ja Amira suka kule a daki suna ta fama da keke, ita kuma Ummi ta zauna wajen su Hanan kannen Amira a falo suna wasa.
Nan sukayi la’asar sai wajen biyar na yamma sannan direban su Amira ya dawo ya kwashesu, suna tafiya Rukayya tayiwa Aisha sallama ta ja Ummi suka fice.
Ta san zata sha fadan Mommy don haka a hankali ta shiga gidan tana fatan Mommy bata nemeta ba.
Tana shiga falon taci karo da Mommy a zaune tare da Yusra da Nana, da sallama ta shiga amma babu wanda ya amsa sallamarta. Kallon da Mommy take mata ya tabbatar mata tana cikin matsala. Kafin ta gama tsara karyar da zata gayawa Mommy muryar Mommy din ta katse mata tunani
‘Zo nan Rukayya.’
Cikin sanyin jiki ta karasa ta tsuguna a gaban Mommy tace
‘Gani Mommy.’
‘Daga ina kike?’
‘Um Mommy gidan Anti Aisha daman naje wajen Amira, sun ma t…'
Kafin ta rufe baki ta dauketa da mari, ta dafe kumatun bakinta a bude ta sunkuyar da kai tana fitar da kwalla. Ummi da take tsaye ta raba ta wuce bayan kujera saboda kada a mareta itama. Cikin fushi Mommy ta cigaba
‘Ba na hanaki zuwa gidan matar nana ba? Itace ta haifar min ke ne ko me da zan ce kada ki fita ki saci jiki ki fice harda daukar ‘yar rakiya? Uban me take baki idan kin je da bazaki zauna cikin ‘yan uwanki ba? Wallahi ki shiga hankalinki Rukayya, idan ba haka ba zamu sa kafar wando daya dake a gidan nan. Tashi ki bace min da gani kafin na mangareki.’
Ta mike tana share hawaye ta nufi dakinsu na kasa.
‘Ummi.’
Mommy ta kirawota cikin tsawa, ta leko daga bayan kujera tana zare ido
‘Idan na sake ganin kin shiga wannan gidan sai na zaneki kuma na karya kafafunki.’
A sanyaye tace
‘Ba zan sake ba Mommy.’
Yusra tace
‘Mommy ba fa laifinta bane, waccan uwar shisshigin ce don ita kowa ma bata ki yaje gidan ba tunda bata gane mai sonta da mara sonta.’
‘To zanyi maganinta a cikin gidan nan.’
Ta tashi ta haye sama ta barsu a nan Yusra tana kara jawa Ummi kunne.
………….
Rukayya tana shiga dakin su ta wuce bandaki ta turo kofa, don ta san idan ta zauna a dakin ma yanzu Yusra zata biyota ta zo tana gaya mata maganganu.
A bushe bandakin yake don haka tana shiga ta zauna a kasa daga gefen bahon wanka ta hada kai da gwiwa ta kara rushewa da kuka.
Ko da suka fita da keken nan ba karamin dadi Rukayya taji ba; don dama tunda taga yanda Mommy take gwalewa ta yanke shawara gidan Antin zata mayar da shi idan ya so in tana can tayi dinki ko idan Amira ta zo.
Bayan ya kaita ya yiwa Aishan sallama kuwa yana fita suka saka keken a gaba ita da Aisha saida suka hada shi wajen dayan dare sannan suka kwanta.
--------
Duk yanda Mommy ta so morewa a wannan daren bata samu ba domin yana dawowa ya rufe gidan ya shige dakinsa ya kulle. Haka ta kwana tana takaicin yanda yake Raina mata hankali.
__
Duk wata tsaraba da Abban ya siyowa yara haka ya tattara ya kulle ya ajiye a gidan Aisha; tunda Zahra ta saka shi a gaba da maganganun nan yace ba zai bayar da tsarabar don haka har abinda ya siyo mata duk ajiyewa yayi. Wasu ma duk sai ya kwashe ya kaiwa mutan gidan Yaya Bello wadanda ba zai iya bayarwa ba kuma kamar computer da wayar da ya siyowa Yusra da niyyar in ta gama SS 3 ya bata duk ya tattara ya ajiye.
Saida sukayi sati da dawowa sanna Zahra ta samu ya dan fara sauraronta, don haka nan da nan ta samu ta sanar da shi ana biki a gidan su Amina zasu je. Ba tare da wata matsala ba ya bata dama.
…..
Kwanan su Abba goma sha uku da dawowa Zahra ta shirya ta fice ranar Alhamis da sunan ta tafi biki, karfe goma na safe suka kama hanyar Doguwa.
Sun ci sa’a wannan zuwan babu kowa a wajen don haka kai tsaye aka kaisu dakin da suka gurfane a gaban bokan.
Bayan sun gama yi masa bayani da sanar da shi Abban ya dawo yayi gyaran murya yace
‘Kudin aiki Naira dubu dari hudu.’
Ya tura musu bakar tasa Zahra ta juye kudin dake cikin jakarta wanda dubu dari biyar ne ta taho da su.
Dariya ta karade dakin. Daga baya bokan yace
‘Ranar Lahadi da daddare zamuyi aiki, ke kuma ki tabbatar ya kwana da janaba a wannan daren. Idan kikayi haka gari yana wayewa ba zai sake tuna wata mata ba.’
Dakin ya sake cika da dariya. Bayan dariyar ta lafa tace
‘Um ba a dakina zai kwana ba ranar Lahadi sai dai litinin.’
Ya saki wata kara wadda har ta firgita su, sannan yace
‘Ba ma aiki ranar litinin, Alhamis da Juma’a . Don haka ranar asabar da daddare ki tabbatar ya kwana da janaba mu kuma za muyi miki aiki.’
‘To hakan yayi.’
Ya ware tafi hannunsa sama, nan da an aka jefo masa wani mulmulallen farin gilas mai fasalin kwai. Ya turowa Zahran yana fadin
‘Ki saka wannan a wannan bakar robar ta gabanki ki rufe, ki nemi waje ko ina ne ki boyeta. Matukar ba a bude wannan robar ba to sai yanda kikayi da Yusuf, domin ko Sallah kika ce kada yayi to bazai yi ba balle wani aiki na duniya.’
Ta karba ta fara kici-kicin sakawa a robar da take gabanta yayinda dakin ya rude da dariya.
‘Ku tafi, ku tafi.’
Haka aka dinga nanata musu har suka fice daga dakin suka kamo hanya.
Abun ya dan so ya tsorata Zahra sai dai idan ta tuna zai manta da Aisha a rayuwarsa sai abun yayi mata dadi. Ta dai san ta kashe kudi da yawa, domin kusan miliyan guda kenan wancan zuwan da wannan. Gashi ragowar kudaden da take shirin karawa a business dinta duk tana ta facaka da su.
……….
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
31
A tsaye take a tsakar dakinta tana tunanin inda zata boye bakar robar nan da boka ya bata. Ta duba robar ba zata shiga bayan wardrobe din ba kuma bata so ta saka ta a cikin wardrobe din saboda waje ne da take yawan budewa. Kayan dakin nata irin Turkish Furniture din nan ne masu girma da nauyi don haka kusan ba a taba motsasu ba tunda aka kafa su. Nan take dabara ta fado mata.
Ta karasa ta ajiye robar a kan durowar gefen gadon sannan ta dage iya karfinta ta daga katifar daga daidai kan gadon, ta daga katakon ma sannan ta dauko robar a hankali ta ajiye a kasan katakon. Ta mayar da komai ta gyara gadonta; a nan kam tana da yakinin babu wanda zai motsa mata gado sai idan itace ta saka kuma babu mai duba mata.
Ta yiwa kanta murmushin jin dadi sannan ta fice daga dakin.
___
Ranar Juma’a ce don haka da yake Yaya Zainab bata zo wa Aisha sannu da zuwa ba sai yau ta zo. Gaba daya ita da su Amira suka zo da yake babu islamiyya.
Lokacin da direbansu ya saukesu a bakin gate din gidan Aisha yayi dai-dai da lokacin da Malam Ali ya kawo su Rukayya da makaranta.
Ummi ce ta tabo Rukayya tace
‘Yaya Rukayya ga kawarki can Amiro ta zo.’
Yusra ta balla musu harara duka su biyun, don haka sukayi shiru.
Har suka shiga gida Rukayya tana tunanin yanda zata samu ta je wajen Amira; tana son taje ta nuna mata keken dinkinta don ita Amiran tana da nata ta ma fi Rukayyan iya dinki, amma ta san ba za a barta taje ba.
Idan Abba ya rakata da daddare ta taya Aishan kwana, da safe idan ta fito suka tafi makaranta to Mommy ta haramta mata komawa gidan har sai wani daren idan Abban yayi magana. Idan bai yi magana ba to ita bata isa tace zata je gidan ba.
Yau din dai haka kawai take so taje gida su dan taba dinki kafin su Amira su tafi.
Ta riga ta fidda rai don in dai Yusra taga fitarta to ta san ko ba gidan Anti Aishan taje ba cewa Mommy zata yi can taje, kuma ta san tabbas sai Mommy ta ci mutuncinta.
Wajen karfe uku babu kowa a falon daga ita sai Ummi, ta mike ta dauki hijabinta. Ummi ma duk da bata san ina zata je ba ta mike tace
‘Yaya Rukayya zan raka ki.’
Don haka ta bita a baya suka wuce.
Suna shiga ta gaida su Anti Aishan a falo ta ja Amira suka kule a daki suna ta fama da keke, ita kuma Ummi ta zauna wajen su Hanan kannen Amira a falo suna wasa.
Nan sukayi la’asar sai wajen biyar na yamma sannan direban su Amira ya dawo ya kwashesu, suna tafiya Rukayya tayiwa Aisha sallama ta ja Ummi suka fice.
Ta san zata sha fadan Mommy don haka a hankali ta shiga gidan tana fatan Mommy bata nemeta ba.
Tana shiga falon taci karo da Mommy a zaune tare da Yusra da Nana, da sallama ta shiga amma babu wanda ya amsa sallamarta. Kallon da Mommy take mata ya tabbatar mata tana cikin matsala. Kafin ta gama tsara karyar da zata gayawa Mommy muryar Mommy din ta katse mata tunani
‘Zo nan Rukayya.’
Cikin sanyin jiki ta karasa ta tsuguna a gaban Mommy tace
‘Gani Mommy.’
‘Daga ina kike?’
‘Um Mommy gidan Anti Aisha daman naje wajen Amira, sun ma t…'
Kafin ta rufe baki ta dauketa da mari, ta dafe kumatun bakinta a bude ta sunkuyar da kai tana fitar da kwalla. Ummi da take tsaye ta raba ta wuce bayan kujera saboda kada a mareta itama. Cikin fushi Mommy ta cigaba
‘Ba na hanaki zuwa gidan matar nana ba? Itace ta haifar min ke ne ko me da zan ce kada ki fita ki saci jiki ki fice harda daukar ‘yar rakiya? Uban me take baki idan kin je da bazaki zauna cikin ‘yan uwanki ba? Wallahi ki shiga hankalinki Rukayya, idan ba haka ba zamu sa kafar wando daya dake a gidan nan. Tashi ki bace min da gani kafin na mangareki.’
Ta mike tana share hawaye ta nufi dakinsu na kasa.
‘Ummi.’
Mommy ta kirawota cikin tsawa, ta leko daga bayan kujera tana zare ido
‘Idan na sake ganin kin shiga wannan gidan sai na zaneki kuma na karya kafafunki.’
A sanyaye tace
‘Ba zan sake ba Mommy.’
Yusra tace
‘Mommy ba fa laifinta bane, waccan uwar shisshigin ce don ita kowa ma bata ki yaje gidan ba tunda bata gane mai sonta da mara sonta.’
‘To zanyi maganinta a cikin gidan nan.’
Ta tashi ta haye sama ta barsu a nan Yusra tana kara jawa Ummi kunne.
………….
Rukayya tana shiga dakin su ta wuce bandaki ta turo kofa, don ta san idan ta zauna a dakin ma yanzu Yusra zata biyota ta zo tana gaya mata maganganu.
A bushe bandakin yake don haka tana shiga ta zauna a kasa daga gefen bahon wanka ta hada kai da gwiwa ta kara rushewa da kuka.