Sashe 94
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Shi din ma za a saka miki shi a kwalba!”
Kalmar da kwakwalwarsa ta dinga maimaita masa kenan.
Tabbas da ba don Allah ya karbi rayuwar Zahra a daidai wannan lokacin ba da yanzu bai san halin da suke ciki ba shi da Aishan. Don yaji inda aka ambaci yaron Malam a hirarsu da Amina kuma yana zargin ko ba wajen yaron Malam din zasu je ba to tabbas kudin da ta turawa Amina na zuwa wajen wani matsafin ne. Ya lalubo sunan ‘yan uwanta Murja da Suwaiba ya duba hirarrakinsu, sai dai a nan bai sami wani abu da yake da alaka da zantukan da tayi da Amina ba. Ya cigaba da kaiwa da kawowa a dakin yana tunanin da mamakin yanda Zahra ta dade tana cutar dashi.
Kwankwasa masa kofar da akayi ne ya dawo da shi hayyacinsa, yace
'Shigo.'
Saddiku ne ya bude ya shigo ya dubi Abban da alamar tambaya a fuskarsa sai kuma yace
'Abba Anti Murja ce suka zo ita da Anti Suwaiba.'
Ya dafe kai yace
'Subhanallah! Ka ga na manta tun last week suka sanar min zasu zo yau din. Gani nan zuwa.’
Saddiku ya fice ya rufe masa kofa.
Ya koma ya zauna a gefen gadon ya dafe kai; gaba daya ya manta tun wancan satin Murja ta kirawoshi ta sanara da shi zasu zo ranar Lahadi su bude dakin Zahra su kwashe kayanta na sawa. Ya amsa musu don shima yana so su kwashe kayan, don shi ya ce har gadon Yaya Murja ta kwashe su sa a kasuwa sai su kawo kudin a rabawa yara shi ya yafe; fenti yake son yiwa gidan gaba daya kafin Aisha ta shiga dakin.
Ya kashe wayar cike da damuwa ya ajiyeta a kan durowar gefen gado ya matsa gaban wardrobe ya goge fuskarsa da tawul ya fice daga dakin. A falon kasa ya samesu inda ya zauna suka gaisa, Yusra da Saddiku wadanda basu je makaranta ba suna zaune suma. Bayan sun gaisa ya dubi Saddiku yace
'Ka bude mana dakin Mommynka Saddiku, za a duba kayan ne a kwashe masu amfani a sayar a raba gado kamar yanda Allah ya ce.’
Ba tare da ya amsa ba ya mike ya haye sama tunda mukullin dakin nata yana dakin Abban inda Saddikun ya ajiye. Abban ya mike tsaye yana yiwa su Yaya Murja iso zuwa saman. Suna mikewa wayarsa da take aljihunsa ta fara kara, ya ja baya yayi musu iso su wuce saman inda suka wuce Yusra tana biye da su. Ya lalubo wayar ya amsa da saurin tana daf da tsinkewa ganin cewa Yaya Bello ne.
Suna gama gaisawa Yaya Bello yace
'Ina ka tsaya ne? Kace zamu je wajen iyayen Aisha sha daya da rabi gashi sha daya da rabin har ta yi baka zo ba balle mu tafi.’
Ya dora daya hannun nasa a ka yana fadin
'Subhanallahi! Wallahi Yaya na manta shaf. Kai Jama'ah! Kuma ka ga ma baki ne da mu a gidan ‘yan uwan Zahra ne zasu duba kayanta a fitar don a rabawa magada. Kai! Ni kaina wallahi yanzun ba a nutse nake ba Yaya, ina ga bari kawai na kirawo Abubakar din su yi mana uzuri ma je da magriba don wallahi yanzu bani ma da nutsuwa.’
Yaya Bellon yace
'Akwai wata matsala ne a gidan? Na ji ka kam lallai ba ka da nutsuwa.’
'Wallahi Yaya, idan na zo dai zaka ji. Bari na kirawo Abubakar din.’
Yana ajiye wayar ya kirawo Abubakar ya sanar dashi suyi masa uzuri zasu zo da Magriba, nan ya sanar dashi dama an yi rasuwa Baffa yana son yaje jana'iza don haka suka bari sa hadu da magriba.
Yana ajiye wayar ya mayar da ita aljihunsa ya haye saman, yana isa falon saman kuma ya tsaya ya jona wayar tasa a chaji sanna ya shige dakin Zahran.
Yana shiga ya tarar da su sun fito da kayanta na sawa suna ta lodawa a akwati, ga wasu kuma a gefe wadanda sababbi ne sai kuma manyan leshinanta wadanda Yaya Murja take ganin a bawa yara su dinka. Nan da nan Yusra da Saddiku suka taya su suka lode kayan a akwatuna, wadanda akwatunan basu dauka ba aka waresu gefe zuwa lokacin da za a sami mazubi a san yanda za ayi da su.
Dan akwatin sarkokinta an dauko shi inda Yaya Murja ta ware na good ta mikawa Abban tace
'Wannan gwal ne sai a ajiyewa yaran.’
Ba tare da ya duba ba ya karbi dan akwatin ya bawa Saddiku ya kai masa daki.
Wani akwatin ya hango a saman wardrobe na agogo, ya mika hannu ya dauko. Yana daukowa yaji wani abu ya fada bayan wardrobe din. Ya zauna a gefen gadon ya bude akwatin; agogunata ne a ciki da sarkokinta na fashion. Ya mayar ya rufe ya mikawa Suwaiba yana fadin
‘Wannan ma ai sai ku zabawa yaran na ga masu kyau ne.’
Ta karba ta ajiye a gefe suka cigaba da zazzage durowoyin mudubin ta, wadanda duk tarkacen kayan mata ne a ciki. Su ma su Suwaiban karewa sukeyi suna fatan Abban ya fita ya basu guri amma ya ki.
A nan Yaya Murja ta sanar da shi ta sami mai sayen gadon amma nan zai zo ya gani ayi ciniki idan ya biya sai ya dauka. Ya dubi Saddiku wanda yake kwashe tarkacen kayan shafawa da kwalliyarta a kwali yace
'Bar wannan in suka duba sa kwashe zo ka kama min wardrobe din nan mu matsar a dauko abinda ya fada tunda an kwashe kayan ciki gaba daya. Idan muka dauko sai mu kwance gadon don mai sayen ko bana nan idan suka zo sai kawai ya duba suyi magana da Antinka.
Suka kama wardrobe din da kyar suka dan matsar da shi gaba, Abban yace Saddiku ya shiga bayan ya dauko duk abubuwan da suka fada. Nan ya shige ya dinga kwaso tarkacen; wasu warin dankunnaye, agogo guda daya wanda shine ya fada lokacin da Abban ya dauko akwatin da irin lallen nan rani wanda ya ma riga ya bushe. Ya zo fitowa daga bayan ya taka kwalbar fiya-fiya, ya tsuguna ya dauka yana gogewa. Abban ya mika hannu ya karba yana cewa
'Meye wannan kuma?’
Saddikun ya amsa
'Ban sani ba, kamar wani magani ne ko me a ciki oh.’
Ya karasa goge kwalbar yana dubawa; wani dan abu ne a ciki kamar busasshiyar fata da allurai guda biyu a jiki sai kuma wani guntun farin tsumma ko takarda bai gane ba. Abun yayi masa kama da tsafi sannan kuma ya tuna masa abun da aka cire a gidan Aisha lokacin da ana shuka bishiya, don shima allurai ne a jikin abun. Ya tuna wancan warin don haka yaji tsoron bude kwalbar fiya-fiyan ya jefe a aljihunsa da niyyar sai ya kaiwa liman ko Malam Sama'ila sai a bude.
Yaya Murja tana kallonshi ta dauke kai, duk da bata fahimci menene abun ba amma dai ta ga kamar abun ya karawa Abban damuwa. Suka cigaba da tattara kayan suna duddubawa.
Abba da Saddiku suka kama katifar suka jingine bayan Yusra ta cire zanin gadon. Nan da nan suka kama kwance gadon. Katako ne mai nauyin gaske don haka da kyar suke kamawa suna jinginewa. Kan gadon yafi komai nauyi don haka sai da Suwaiba ta sa hannu ta bangaren Saddiku sannan suka cicciba suka jingine. Ta juyo ta dauki wata bakar robar da ta gani a bayan gadon, kafin ace wani abu ta bude tana mamaki don babu ko rubutuba jiki balle tace mai ne.
Tana budewa wani farin hayaki ya fito daga cikin robar ya kanannade yayi sama; Saddiku, Abba da Murja da Yusra duk suna tsaye suna kallo. Suka zaro ido kowa ya ja baya yayinda Suwaiban itama ta saki robara kasa ta ja baya tana fadin
'Wayyo Allah!’
Haka hayakin da ya fita daga robar ya nannade yayi sama suna kallo ya bace, suka yi cirko-cirko. Abban ya karasa ya daga robar a kasan ba tare da ya dauka ba. Wani abu ne a ciki kamar kwan agwagwa sai dai shi akwai rubutu a jiki. Suka dan matso suka zubawa abun ido. Abban ya fara karanto ayatul kursiyyu a fili ya tofawa wannan robar sannan ya ci gaba da jan ‘la haula wa la kuwwata illa billah’; yasa hannu ya zaro kwan a hankali. Babu nauyi kwata kwata, yana dubawa ya ga kwan ya tsage kuma babu komai a ciki; kamar bawon kwan ne kawai. Ya juya yana karanta rubutun da yake jikin bawon kwan; sunansa ne da sunan mahaifinsa da na mahaifiyarsu aka rubuta da jan rubutu. Sai kuma aka rubuta sunan Aisha da na iyayenta da bakin rubutu kuma aka sokeshi da jan rubutu.
Cikin sanyin murya Saddiku yayi tambayar da kowa yake son yi ya kasa
'Abba menene wannan din kamar abun aljannu?’
Ba tare da ya dauke idonsa daga kallon abun ba yace
'Ban sani ba Saddiku, amma dauko min wayata a falo tana chaji na kirawo Malam Liman Muji. Tunda ma abun ya fita a gidan kada muje ya cutar da wani.’
Nan da nan Saddiku ya fice.
Su Murja da Zahra duk sun kasa magana sai kallon-kallo kawai sukeyi suna zare idanu. Ba jimawa Saddiku ya dawo ya mikawa Abban wayar yana cewa
'Baba ma ya kirawoka ga missed calls nan har biyar.’
Yana karbar wayar ya kawar da missed calls din Yaya Bello ya lalubo lambar Malam Liman ya kirawo. Aka yi sa'a yana kusa don haka ba tare da bata lokaci ba ya ce gashi nan zuwa.
Daga su Murja har su Zahra duk jikinsu yayi sanyi don haka gaba daya suka hakura da aikin suka fara diban kayan da zasu fito da su suna fitowa dasu falon.
Kafin su gama Malam Liman ya bugo wayar Abba ya sanar dashi yana kasa, ya umarci Saddiku da ya shigo da shi. Ya sauko daga saman da sauri.
Yana zuwa bakin kofar falon kasan ya ci karo da Yaya Bello yana sallama a bakin kofar. Bayan ya amsa gaisuwarta yace
'Saddiku Ina Abban naka ne? Lafiya dai kuke gaba daya? Ina kannenka? Ina ta kiran wayar Abban baya dagawa.’
Kalmar da kwakwalwarsa ta dinga maimaita masa kenan.
Tabbas da ba don Allah ya karbi rayuwar Zahra a daidai wannan lokacin ba da yanzu bai san halin da suke ciki ba shi da Aishan. Don yaji inda aka ambaci yaron Malam a hirarsu da Amina kuma yana zargin ko ba wajen yaron Malam din zasu je ba to tabbas kudin da ta turawa Amina na zuwa wajen wani matsafin ne. Ya lalubo sunan ‘yan uwanta Murja da Suwaiba ya duba hirarrakinsu, sai dai a nan bai sami wani abu da yake da alaka da zantukan da tayi da Amina ba. Ya cigaba da kaiwa da kawowa a dakin yana tunanin da mamakin yanda Zahra ta dade tana cutar dashi.
Kwankwasa masa kofar da akayi ne ya dawo da shi hayyacinsa, yace
'Shigo.'
Saddiku ne ya bude ya shigo ya dubi Abban da alamar tambaya a fuskarsa sai kuma yace
'Abba Anti Murja ce suka zo ita da Anti Suwaiba.'
Ya dafe kai yace
'Subhanallah! Ka ga na manta tun last week suka sanar min zasu zo yau din. Gani nan zuwa.’
Saddiku ya fice ya rufe masa kofa.
Ya koma ya zauna a gefen gadon ya dafe kai; gaba daya ya manta tun wancan satin Murja ta kirawoshi ta sanara da shi zasu zo ranar Lahadi su bude dakin Zahra su kwashe kayanta na sawa. Ya amsa musu don shima yana so su kwashe kayan, don shi ya ce har gadon Yaya Murja ta kwashe su sa a kasuwa sai su kawo kudin a rabawa yara shi ya yafe; fenti yake son yiwa gidan gaba daya kafin Aisha ta shiga dakin.
Ya kashe wayar cike da damuwa ya ajiyeta a kan durowar gefen gado ya matsa gaban wardrobe ya goge fuskarsa da tawul ya fice daga dakin. A falon kasa ya samesu inda ya zauna suka gaisa, Yusra da Saddiku wadanda basu je makaranta ba suna zaune suma. Bayan sun gaisa ya dubi Saddiku yace
'Ka bude mana dakin Mommynka Saddiku, za a duba kayan ne a kwashe masu amfani a sayar a raba gado kamar yanda Allah ya ce.’
Ba tare da ya amsa ba ya mike ya haye sama tunda mukullin dakin nata yana dakin Abban inda Saddikun ya ajiye. Abban ya mike tsaye yana yiwa su Yaya Murja iso zuwa saman. Suna mikewa wayarsa da take aljihunsa ta fara kara, ya ja baya yayi musu iso su wuce saman inda suka wuce Yusra tana biye da su. Ya lalubo wayar ya amsa da saurin tana daf da tsinkewa ganin cewa Yaya Bello ne.
Suna gama gaisawa Yaya Bello yace
'Ina ka tsaya ne? Kace zamu je wajen iyayen Aisha sha daya da rabi gashi sha daya da rabin har ta yi baka zo ba balle mu tafi.’
Ya dora daya hannun nasa a ka yana fadin
'Subhanallahi! Wallahi Yaya na manta shaf. Kai Jama'ah! Kuma ka ga ma baki ne da mu a gidan ‘yan uwan Zahra ne zasu duba kayanta a fitar don a rabawa magada. Kai! Ni kaina wallahi yanzun ba a nutse nake ba Yaya, ina ga bari kawai na kirawo Abubakar din su yi mana uzuri ma je da magriba don wallahi yanzu bani ma da nutsuwa.’
Yaya Bellon yace
'Akwai wata matsala ne a gidan? Na ji ka kam lallai ba ka da nutsuwa.’
'Wallahi Yaya, idan na zo dai zaka ji. Bari na kirawo Abubakar din.’
Yana ajiye wayar ya kirawo Abubakar ya sanar dashi suyi masa uzuri zasu zo da Magriba, nan ya sanar dashi dama an yi rasuwa Baffa yana son yaje jana'iza don haka suka bari sa hadu da magriba.
Yana ajiye wayar ya mayar da ita aljihunsa ya haye saman, yana isa falon saman kuma ya tsaya ya jona wayar tasa a chaji sanna ya shige dakin Zahran.
Yana shiga ya tarar da su sun fito da kayanta na sawa suna ta lodawa a akwati, ga wasu kuma a gefe wadanda sababbi ne sai kuma manyan leshinanta wadanda Yaya Murja take ganin a bawa yara su dinka. Nan da nan Yusra da Saddiku suka taya su suka lode kayan a akwatuna, wadanda akwatunan basu dauka ba aka waresu gefe zuwa lokacin da za a sami mazubi a san yanda za ayi da su.
Dan akwatin sarkokinta an dauko shi inda Yaya Murja ta ware na good ta mikawa Abban tace
'Wannan gwal ne sai a ajiyewa yaran.’
Ba tare da ya duba ba ya karbi dan akwatin ya bawa Saddiku ya kai masa daki.
Wani akwatin ya hango a saman wardrobe na agogo, ya mika hannu ya dauko. Yana daukowa yaji wani abu ya fada bayan wardrobe din. Ya zauna a gefen gadon ya bude akwatin; agogunata ne a ciki da sarkokinta na fashion. Ya mayar ya rufe ya mikawa Suwaiba yana fadin
‘Wannan ma ai sai ku zabawa yaran na ga masu kyau ne.’
Ta karba ta ajiye a gefe suka cigaba da zazzage durowoyin mudubin ta, wadanda duk tarkacen kayan mata ne a ciki. Su ma su Suwaiban karewa sukeyi suna fatan Abban ya fita ya basu guri amma ya ki.
A nan Yaya Murja ta sanar da shi ta sami mai sayen gadon amma nan zai zo ya gani ayi ciniki idan ya biya sai ya dauka. Ya dubi Saddiku wanda yake kwashe tarkacen kayan shafawa da kwalliyarta a kwali yace
'Bar wannan in suka duba sa kwashe zo ka kama min wardrobe din nan mu matsar a dauko abinda ya fada tunda an kwashe kayan ciki gaba daya. Idan muka dauko sai mu kwance gadon don mai sayen ko bana nan idan suka zo sai kawai ya duba suyi magana da Antinka.
Suka kama wardrobe din da kyar suka dan matsar da shi gaba, Abban yace Saddiku ya shiga bayan ya dauko duk abubuwan da suka fada. Nan ya shige ya dinga kwaso tarkacen; wasu warin dankunnaye, agogo guda daya wanda shine ya fada lokacin da Abban ya dauko akwatin da irin lallen nan rani wanda ya ma riga ya bushe. Ya zo fitowa daga bayan ya taka kwalbar fiya-fiya, ya tsuguna ya dauka yana gogewa. Abban ya mika hannu ya karba yana cewa
'Meye wannan kuma?’
Saddikun ya amsa
'Ban sani ba, kamar wani magani ne ko me a ciki oh.’
Ya karasa goge kwalbar yana dubawa; wani dan abu ne a ciki kamar busasshiyar fata da allurai guda biyu a jiki sai kuma wani guntun farin tsumma ko takarda bai gane ba. Abun yayi masa kama da tsafi sannan kuma ya tuna masa abun da aka cire a gidan Aisha lokacin da ana shuka bishiya, don shima allurai ne a jikin abun. Ya tuna wancan warin don haka yaji tsoron bude kwalbar fiya-fiyan ya jefe a aljihunsa da niyyar sai ya kaiwa liman ko Malam Sama'ila sai a bude.
Yaya Murja tana kallonshi ta dauke kai, duk da bata fahimci menene abun ba amma dai ta ga kamar abun ya karawa Abban damuwa. Suka cigaba da tattara kayan suna duddubawa.
Abba da Saddiku suka kama katifar suka jingine bayan Yusra ta cire zanin gadon. Nan da nan suka kama kwance gadon. Katako ne mai nauyin gaske don haka da kyar suke kamawa suna jinginewa. Kan gadon yafi komai nauyi don haka sai da Suwaiba ta sa hannu ta bangaren Saddiku sannan suka cicciba suka jingine. Ta juyo ta dauki wata bakar robar da ta gani a bayan gadon, kafin ace wani abu ta bude tana mamaki don babu ko rubutuba jiki balle tace mai ne.
Tana budewa wani farin hayaki ya fito daga cikin robar ya kanannade yayi sama; Saddiku, Abba da Murja da Yusra duk suna tsaye suna kallo. Suka zaro ido kowa ya ja baya yayinda Suwaiban itama ta saki robara kasa ta ja baya tana fadin
'Wayyo Allah!’
Haka hayakin da ya fita daga robar ya nannade yayi sama suna kallo ya bace, suka yi cirko-cirko. Abban ya karasa ya daga robar a kasan ba tare da ya dauka ba. Wani abu ne a ciki kamar kwan agwagwa sai dai shi akwai rubutu a jiki. Suka dan matso suka zubawa abun ido. Abban ya fara karanto ayatul kursiyyu a fili ya tofawa wannan robar sannan ya ci gaba da jan ‘la haula wa la kuwwata illa billah’; yasa hannu ya zaro kwan a hankali. Babu nauyi kwata kwata, yana dubawa ya ga kwan ya tsage kuma babu komai a ciki; kamar bawon kwan ne kawai. Ya juya yana karanta rubutun da yake jikin bawon kwan; sunansa ne da sunan mahaifinsa da na mahaifiyarsu aka rubuta da jan rubutu. Sai kuma aka rubuta sunan Aisha da na iyayenta da bakin rubutu kuma aka sokeshi da jan rubutu.
Cikin sanyin murya Saddiku yayi tambayar da kowa yake son yi ya kasa
'Abba menene wannan din kamar abun aljannu?’
Ba tare da ya dauke idonsa daga kallon abun ba yace
'Ban sani ba Saddiku, amma dauko min wayata a falo tana chaji na kirawo Malam Liman Muji. Tunda ma abun ya fita a gidan kada muje ya cutar da wani.’
Nan da nan Saddiku ya fice.
Su Murja da Zahra duk sun kasa magana sai kallon-kallo kawai sukeyi suna zare idanu. Ba jimawa Saddiku ya dawo ya mikawa Abban wayar yana cewa
'Baba ma ya kirawoka ga missed calls nan har biyar.’
Yana karbar wayar ya kawar da missed calls din Yaya Bello ya lalubo lambar Malam Liman ya kirawo. Aka yi sa'a yana kusa don haka ba tare da bata lokaci ba ya ce gashi nan zuwa.
Daga su Murja har su Zahra duk jikinsu yayi sanyi don haka gaba daya suka hakura da aikin suka fara diban kayan da zasu fito da su suna fitowa dasu falon.
Kafin su gama Malam Liman ya bugo wayar Abba ya sanar dashi yana kasa, ya umarci Saddiku da ya shigo da shi. Ya sauko daga saman da sauri.
Yana zuwa bakin kofar falon kasan ya ci karo da Yaya Bello yana sallama a bakin kofar. Bayan ya amsa gaisuwarta yace
'Saddiku Ina Abban naka ne? Lafiya dai kuke gaba daya? Ina kannenka? Ina ta kiran wayar Abban baya dagawa.’