Sashe 46
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da ya sauko falon kasa sannan ya kirawo Rahama a waya, ta bude dakin baki wanda yake kasan ta fito.
‘Anti Rahma zan fita ne, a gidan Aisha zan kwana dauki mukulli ki kulle muku wannan kofar sai da safe zan dawo. Yaran suna bacci ban tashe su ba.’
‘To.’
Ta koma ta dauko mukullin ta fito, yana fita ta mayar da kofar ta rufe.
Karar bude kofarsa ya janyo hankalin Yusra wadda dama bata yi bacci ba.
Yana ficewa ta sauko falon lokacin Rahma ta gama kulle kofa ta juyo zata koma daki. Tace
‘Anti Rahma Abban fita yayi?’
‘Eh, haka yace gidan Antinku zai kwana.’
‘Um.’
Ta juya ta koma saman.
Itama Rahma ta shige dakin.
Tana sane da yanda tun zuwanta yake kwana a nan, amma a tunaninta kwana yake saboda yara; don haka ma yau din da yace mata can zai kwana bata yi mamaki ba don a hakan ma tana ganin yayi kokari.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
26
Tunda Rukayya ta zo suka hadu da Amira sai ta bar musu dakin baki, ita kuma ta koma tana kwana a dakinta ita kadai.
Tana kwance a kan gadonta Amma ba bacci takeyi ba, ta kashe fitilar dakin sai irin fitilar nan mara haske ta kan durowar ta bari a kunne. Karatun kur’ani ne yake tashi kasa-kasa a dakin wanda ta kunna a mp3 dinta take bi tana daga kwance. Kamar a mafarki ta jiyo motsin bude gate, da sauri ta tashi ta leka ta taga wadda take kallon gate din. Zuciyarta na dakan uku-uku saboda a tunaninta ko wani ne ya shigo musu gidan daga ita sai yara.
Sai da ya gama shigowa gaba daya sannan ta gane shi, ta dafe kirji ta mayar da numfashi. Ta san iyakarsa kofar falo ba iya shigowa zai yi ba, ta tabe baki ta koma ta kwanta ta cigaba da bin karatunta.
Ta baza kunnuwanta tana sauraro taji fitarsa sai kuma taji motsin bude kofar falo, yana kunna fitilar falon ta hango haske ta kasan kofar. Mamaki ya cikata, a fili tace
‘Toh!’
Duk da haka dai sa rai takeyi taji fitarsa, sai kuma taji ya shiga dakinsa wanda a jikin nata dakin yake. A ranta tace yanzu haka wani abune mai mahimmanci da ake bukata yanzu ya bari a dakin shine ya daure ya shigo ya dauka.
Ta gyara kwanciyarta ta cigaba da karatunta tana mamaki.
………..
Tun daga bakin gate yake mamaki yana godewa Allah saboda kwata-kwata babu wani wari, duk wani nauyi da yake ji a kirjinsa idan ya shigo gidan yau babu. Ya karewa farfajiyar gidan kallo duk da cewa akwai duhu sai fitila guda daya dake haska wajen. Ya wuce ya nufi cikin gida.
Yana shiga falon kamshin turarenta ya doki hancinsa, tabbas yayi kewar kamshin nan da kuma mai kamshin.
Kai tsaye dakinsa ya wuce domin a tunaninsa a nan zai sameta sai dai ga mamakinsa bata ciki. Ba tare da bata lokaci ba ya fito ya nufi dakinta, tun daga bakin kofa ya jiyo sauti don haka ya tabbatar tana ciki. Yayi zaton waya takeyi don haka ya murda hannun kofar ya shiga a hankali, sai da ya bude kofar sannan ya fahimci sautin karatun kur’ani yake jiyowa.
Ya hangota a kwance a kan gado; ji yayi kamar zuciyarsa zata fito daga kirjinsa ta riga jikinsa isa inda take kwance.
Kafin ya karasa ta tashi zaune, ta kunna fitilar wayarta don ta tabbatar shine.
Yayi zaton bacci takeyi, amma da yaga ta kunna fitilar wayar sai ya dan ja baya ya kunna fitilar dakin.
Ta bishi da kallo mai cike da tambayoyi, shima kallonta yake yana murmushi a lokacin da yake karasawa inda take. Ta dan muskuta kadan ya zauna a gefen kafafunta da suke mike a kan gadon.
Ya cigaba da binta da kallo har ta dauke idonta tana kokarin tare kwallar da ta taso mata, ya dan matsa kadan ya kama hannunta. Ya kirawo sunanta kamar daga can kasan makogoronsa
‘Aisha.’
A gajarce ta bashi amsa
‘Um.’
Ya dan kara matsawa kusa da ita, so yake ya rungumeta amma ta ki motsawa. Ya kamo daya hannun nata ya rike, yayi shiru na dan lokaci yana tunanin ta inda zai fara.
Kusan wata shida kenan rabonshi da ita, fuskarta kawai da yake kallo yanzu ya tabbatar masa da cewa ya saka ta a cikin damuwa ga kuma wata rama da yaga tayi; domin rigar bacci ce a jikinta mai hannun shimi don haka yana kallon wuyanta.
Yace
‘Aisha kiyi hakuri, na san mun sha wahala amma Alhamdulillah yanzu komai ya wuce. Na sami maganin abinda yake hanani shigowa gidan nan, in sha Allah Allah ba zai bari a wani abu ya sake shiga tsakaninmu ba.’
Ta zare hannunta daga nasa ta share kwallar da ta taru a idonta, tace
‘Bari na dubo su Rukayya a dakinsu.’
Ta zare daya hannun nata ta sauko daga kan gadon, kafin yace wani abu ta fice daga dakin.
Ya juyo ya bi bayanta da kallo; sai yanzu ya kara tausayinta, tabbas ya san ya barta cikin damuwa kamar yanda shima yake cikin damuwa. Duk wanda yayi masa wannan abun tabbasa ba zai taba yafe masa ba. Ya gyara zama ya koma inda ta tashi ya zauna kamar yanda take zaune kafin ta tashi. Ya dauki wayarta ya kashe fitilar da ta bari a kunne.
…….
Tana fita daga dakin hawayen da take rikewa ya kwace, fita hawaye yake daga idonta tana sharewa har ta karasa dakin baki inda Rukayya da Amira suke bacci.
Ba so take ta tashesu daga bacci ba don haka cikin sanda ta karasa kan kafet din dake tsakar dakin, ta mika hannu ta dauko filo wanda ga dukkan alamu na Amira ne ta jefo shi kasa garin bacci. Ta gyara filon ta ajiye a kan kafet din ta kwanta.
Hawayen da yake bin idonta ya cigaba da zarya babu kakkautawa; sai yanzu ya tuna da ita? Wata kusan shida? Ko jiya da za ayi shuka ta san warin da yace yana ji ne baya so ya ji shi yasa bai shigo ba ya kirawota. Me zai ce mata yanzun? Nan da ya shigo mata daki so yake ta rungumeshi shikenan ko me? To idan fa ma yanzu ta saki jiki da shi matarshi ta dawo ya koma wajenta ya kyaleta fa?
Zuciyarta ta fara harbawa da sauri yayinda hawayenta ya kara yawa; tabbas tana iya yiwuwa don matarsa bata nan ne don ta san tabbas ko ma menene ya shiga tsakaninsa itace. Idan kuwa hakane akwai yiwuwar ya zo ya hilaceta ta saki jiki da shi ana sallacewa matarsa ta dawo ya koma wajenta yace idan ya shigo nan din yana jin wari. Gaskiya a yanzu ba zata iya sakar masa kanta ba, gara ma kawai ita kada ya takura mata, ko kuma a kalla ya jira matarsa ta dawo sai a cigaba da rabon kwana. A lokacin sai ta san ba rashin matarsa ne ya kawo shi inda take ba.
Ta muskuta ta cigaba da share hawaye.
………..
Yana nan zaune yana jiran Aisha har wajen minti talatin suka shude, mamaki ya cikashi. To me take yi a dakin su Rukayyan? Ya taso ya fito daga dakin ya shiga nashi dakin bata nan, ya duba kofar falon yaga babu alamar an budeta. Wannan ya tabbatar masa da cewa dakin yaran ta shiga kenan. To me takeyi har yanzu bata fito ba?
Ya dawo falo ya kunna fitila ya zauna yana tunani; to ko dai Aisha fushi tayi dashi? Baya jin zatayi fushi tunda ai ta san ba yin kansa bane.
Ya tashi ya zo kofar dakin su Rukayyan ya tsaya ya kasa kunne ko zai ji motsinsu Bai ji komai ba, to ko dai Aisha fushi tayi da shi?
Ya Kuma kan kujera ya zauna; baya son shiga dakin yaran da wannan daren tunda su din mata ne kuma gashi harda Amira a ciki.
Haka ya gaji da zama a falon ya tashi ya koma dakin Aishan ya kwanta; sai dai da yake zuciyarsa bata da nutsuwa haka ya kasa bacci yana ta juyi.
……..
Karfe uku na dare da minti arba’in da biyar agogon dakin mai alarm ya fara kararrawa, a gefen Rukayya yake don haka cikin magagin bacci ta mika hannu ta katseshi.
A take Aisha ta tashi tunda dama ba bacci takeyi ba, ta fada bandaki ta wanko fuska ta dauro alwala sannan ta fito ta tashi yaran. Da akwai kayanta a dakin don haka ta dauki zaninta ta daura a kan kayan baccin. Saida tayi musu bayanin cewa Abban Rukayya yana nan don su san irin shigar da zasuyi kada su fito yanda suka saba da kayan bacci.
Tayi tsammanin yana falon don bata jin ya fita daga gidan, amma sai taga babu kowa, don haka kai tsaye ta fada kichin. Ta dora indomie da kuma ruwan shayi sannan ta tsaya yanka albasa.
A nan su Amira suka fito suka sameta, suka tayata har indomie din ta dahu sannan ta zuba nata ita da yaran a tray Amira ta dauka ta kai musu kan kafet din falo. Shi kuma Abba ta zuba masa nashi a plate ta hada masa shayi ta dora a kan dining table.
Rukayyace ta hado musu shayi gaba daya ta ajiye sannan ta dauko musu ruwan sha ta ajiye.
Aisha ta duba agogo taga karfe hudu da kwata don haka tace da su Rukayya su fara cin abincin kafin ta taso Abban.
Tana taba kofar ya bude ido, bayan ya amsa sallamarta tace
‘Nayi serving abincin sahur, gara ka fito kaci don an kusa assalatu.’
Yana daga zaune a kan gadon yace
‘Aisha.’
Ta kalleshi suka hada ido alamar tana sauraronsa, ya cigaba yana mika mata hannunsa
‘Zo nan.’
Ta kawar da kai tace
‘Zamu makara fa, saura bai fi minti ashirin ba ayi assalatu gara ka fito kawai muci abinci.’
Kafin yace wani abu ta juya ta fice.
‘Anti Rahma zan fita ne, a gidan Aisha zan kwana dauki mukulli ki kulle muku wannan kofar sai da safe zan dawo. Yaran suna bacci ban tashe su ba.’
‘To.’
Ta koma ta dauko mukullin ta fito, yana fita ta mayar da kofar ta rufe.
Karar bude kofarsa ya janyo hankalin Yusra wadda dama bata yi bacci ba.
Yana ficewa ta sauko falon lokacin Rahma ta gama kulle kofa ta juyo zata koma daki. Tace
‘Anti Rahma Abban fita yayi?’
‘Eh, haka yace gidan Antinku zai kwana.’
‘Um.’
Ta juya ta koma saman.
Itama Rahma ta shige dakin.
Tana sane da yanda tun zuwanta yake kwana a nan, amma a tunaninta kwana yake saboda yara; don haka ma yau din da yace mata can zai kwana bata yi mamaki ba don a hakan ma tana ganin yayi kokari.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
26
Tunda Rukayya ta zo suka hadu da Amira sai ta bar musu dakin baki, ita kuma ta koma tana kwana a dakinta ita kadai.
Tana kwance a kan gadonta Amma ba bacci takeyi ba, ta kashe fitilar dakin sai irin fitilar nan mara haske ta kan durowar ta bari a kunne. Karatun kur’ani ne yake tashi kasa-kasa a dakin wanda ta kunna a mp3 dinta take bi tana daga kwance. Kamar a mafarki ta jiyo motsin bude gate, da sauri ta tashi ta leka ta taga wadda take kallon gate din. Zuciyarta na dakan uku-uku saboda a tunaninta ko wani ne ya shigo musu gidan daga ita sai yara.
Sai da ya gama shigowa gaba daya sannan ta gane shi, ta dafe kirji ta mayar da numfashi. Ta san iyakarsa kofar falo ba iya shigowa zai yi ba, ta tabe baki ta koma ta kwanta ta cigaba da bin karatunta.
Ta baza kunnuwanta tana sauraro taji fitarsa sai kuma taji motsin bude kofar falo, yana kunna fitilar falon ta hango haske ta kasan kofar. Mamaki ya cikata, a fili tace
‘Toh!’
Duk da haka dai sa rai takeyi taji fitarsa, sai kuma taji ya shiga dakinsa wanda a jikin nata dakin yake. A ranta tace yanzu haka wani abune mai mahimmanci da ake bukata yanzu ya bari a dakin shine ya daure ya shigo ya dauka.
Ta gyara kwanciyarta ta cigaba da karatunta tana mamaki.
………..
Tun daga bakin gate yake mamaki yana godewa Allah saboda kwata-kwata babu wani wari, duk wani nauyi da yake ji a kirjinsa idan ya shigo gidan yau babu. Ya karewa farfajiyar gidan kallo duk da cewa akwai duhu sai fitila guda daya dake haska wajen. Ya wuce ya nufi cikin gida.
Yana shiga falon kamshin turarenta ya doki hancinsa, tabbas yayi kewar kamshin nan da kuma mai kamshin.
Kai tsaye dakinsa ya wuce domin a tunaninsa a nan zai sameta sai dai ga mamakinsa bata ciki. Ba tare da bata lokaci ba ya fito ya nufi dakinta, tun daga bakin kofa ya jiyo sauti don haka ya tabbatar tana ciki. Yayi zaton waya takeyi don haka ya murda hannun kofar ya shiga a hankali, sai da ya bude kofar sannan ya fahimci sautin karatun kur’ani yake jiyowa.
Ya hangota a kwance a kan gado; ji yayi kamar zuciyarsa zata fito daga kirjinsa ta riga jikinsa isa inda take kwance.
Kafin ya karasa ta tashi zaune, ta kunna fitilar wayarta don ta tabbatar shine.
Yayi zaton bacci takeyi, amma da yaga ta kunna fitilar wayar sai ya dan ja baya ya kunna fitilar dakin.
Ta bishi da kallo mai cike da tambayoyi, shima kallonta yake yana murmushi a lokacin da yake karasawa inda take. Ta dan muskuta kadan ya zauna a gefen kafafunta da suke mike a kan gadon.
Ya cigaba da binta da kallo har ta dauke idonta tana kokarin tare kwallar da ta taso mata, ya dan matsa kadan ya kama hannunta. Ya kirawo sunanta kamar daga can kasan makogoronsa
‘Aisha.’
A gajarce ta bashi amsa
‘Um.’
Ya dan kara matsawa kusa da ita, so yake ya rungumeta amma ta ki motsawa. Ya kamo daya hannun nata ya rike, yayi shiru na dan lokaci yana tunanin ta inda zai fara.
Kusan wata shida kenan rabonshi da ita, fuskarta kawai da yake kallo yanzu ya tabbatar masa da cewa ya saka ta a cikin damuwa ga kuma wata rama da yaga tayi; domin rigar bacci ce a jikinta mai hannun shimi don haka yana kallon wuyanta.
Yace
‘Aisha kiyi hakuri, na san mun sha wahala amma Alhamdulillah yanzu komai ya wuce. Na sami maganin abinda yake hanani shigowa gidan nan, in sha Allah Allah ba zai bari a wani abu ya sake shiga tsakaninmu ba.’
Ta zare hannunta daga nasa ta share kwallar da ta taru a idonta, tace
‘Bari na dubo su Rukayya a dakinsu.’
Ta zare daya hannun nata ta sauko daga kan gadon, kafin yace wani abu ta fice daga dakin.
Ya juyo ya bi bayanta da kallo; sai yanzu ya kara tausayinta, tabbas ya san ya barta cikin damuwa kamar yanda shima yake cikin damuwa. Duk wanda yayi masa wannan abun tabbasa ba zai taba yafe masa ba. Ya gyara zama ya koma inda ta tashi ya zauna kamar yanda take zaune kafin ta tashi. Ya dauki wayarta ya kashe fitilar da ta bari a kunne.
…….
Tana fita daga dakin hawayen da take rikewa ya kwace, fita hawaye yake daga idonta tana sharewa har ta karasa dakin baki inda Rukayya da Amira suke bacci.
Ba so take ta tashesu daga bacci ba don haka cikin sanda ta karasa kan kafet din dake tsakar dakin, ta mika hannu ta dauko filo wanda ga dukkan alamu na Amira ne ta jefo shi kasa garin bacci. Ta gyara filon ta ajiye a kan kafet din ta kwanta.
Hawayen da yake bin idonta ya cigaba da zarya babu kakkautawa; sai yanzu ya tuna da ita? Wata kusan shida? Ko jiya da za ayi shuka ta san warin da yace yana ji ne baya so ya ji shi yasa bai shigo ba ya kirawota. Me zai ce mata yanzun? Nan da ya shigo mata daki so yake ta rungumeshi shikenan ko me? To idan fa ma yanzu ta saki jiki da shi matarshi ta dawo ya koma wajenta ya kyaleta fa?
Zuciyarta ta fara harbawa da sauri yayinda hawayenta ya kara yawa; tabbas tana iya yiwuwa don matarsa bata nan ne don ta san tabbas ko ma menene ya shiga tsakaninsa itace. Idan kuwa hakane akwai yiwuwar ya zo ya hilaceta ta saki jiki da shi ana sallacewa matarsa ta dawo ya koma wajenta yace idan ya shigo nan din yana jin wari. Gaskiya a yanzu ba zata iya sakar masa kanta ba, gara ma kawai ita kada ya takura mata, ko kuma a kalla ya jira matarsa ta dawo sai a cigaba da rabon kwana. A lokacin sai ta san ba rashin matarsa ne ya kawo shi inda take ba.
Ta muskuta ta cigaba da share hawaye.
………..
Yana nan zaune yana jiran Aisha har wajen minti talatin suka shude, mamaki ya cikashi. To me take yi a dakin su Rukayyan? Ya taso ya fito daga dakin ya shiga nashi dakin bata nan, ya duba kofar falon yaga babu alamar an budeta. Wannan ya tabbatar masa da cewa dakin yaran ta shiga kenan. To me takeyi har yanzu bata fito ba?
Ya dawo falo ya kunna fitila ya zauna yana tunani; to ko dai Aisha fushi tayi dashi? Baya jin zatayi fushi tunda ai ta san ba yin kansa bane.
Ya tashi ya zo kofar dakin su Rukayyan ya tsaya ya kasa kunne ko zai ji motsinsu Bai ji komai ba, to ko dai Aisha fushi tayi da shi?
Ya Kuma kan kujera ya zauna; baya son shiga dakin yaran da wannan daren tunda su din mata ne kuma gashi harda Amira a ciki.
Haka ya gaji da zama a falon ya tashi ya koma dakin Aishan ya kwanta; sai dai da yake zuciyarsa bata da nutsuwa haka ya kasa bacci yana ta juyi.
……..
Karfe uku na dare da minti arba’in da biyar agogon dakin mai alarm ya fara kararrawa, a gefen Rukayya yake don haka cikin magagin bacci ta mika hannu ta katseshi.
A take Aisha ta tashi tunda dama ba bacci takeyi ba, ta fada bandaki ta wanko fuska ta dauro alwala sannan ta fito ta tashi yaran. Da akwai kayanta a dakin don haka ta dauki zaninta ta daura a kan kayan baccin. Saida tayi musu bayanin cewa Abban Rukayya yana nan don su san irin shigar da zasuyi kada su fito yanda suka saba da kayan bacci.
Tayi tsammanin yana falon don bata jin ya fita daga gidan, amma sai taga babu kowa, don haka kai tsaye ta fada kichin. Ta dora indomie da kuma ruwan shayi sannan ta tsaya yanka albasa.
A nan su Amira suka fito suka sameta, suka tayata har indomie din ta dahu sannan ta zuba nata ita da yaran a tray Amira ta dauka ta kai musu kan kafet din falo. Shi kuma Abba ta zuba masa nashi a plate ta hada masa shayi ta dora a kan dining table.
Rukayyace ta hado musu shayi gaba daya ta ajiye sannan ta dauko musu ruwan sha ta ajiye.
Aisha ta duba agogo taga karfe hudu da kwata don haka tace da su Rukayya su fara cin abincin kafin ta taso Abban.
Tana taba kofar ya bude ido, bayan ya amsa sallamarta tace
‘Nayi serving abincin sahur, gara ka fito kaci don an kusa assalatu.’
Yana daga zaune a kan gadon yace
‘Aisha.’
Ta kalleshi suka hada ido alamar tana sauraronsa, ya cigaba yana mika mata hannunsa
‘Zo nan.’
Ta kawar da kai tace
‘Zamu makara fa, saura bai fi minti ashirin ba ayi assalatu gara ka fito kawai muci abinci.’
Kafin yace wani abu ta juya ta fice.