Sashe 76
Uwar Sadiku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A kusa da emergency din yayi parking suka fito suka shiga, sai dai suna shiga kuma ya rasa wanda zai kama. Don haka ya janyo Yaya Bello suka dawo waje ya kirawo Zahra ya tambayeta wanda zasu nema; bayan ta sanar da shi ya ajiye wayar ya kirawo lambar Saddikun sanna suka nufi komawa cikin emergency din.
Yana shiga ya hango wanda yake waya da shi; yaro ne matashi wanda ba zai wuce shekaru ashirin da biyar ba zuwa da shida. Da hanzari ya karaso wajen su Abban,bayan sun gaisa ya mikawa Abban wayar Saddiku yana fadin
‘Ga wayar Sadik din.’
Ya karba yana fadin
‘Wai me ya samesu ne?’
Cikin damuwa yace
‘To ni dai abokinsu ne ya kirawoni kuma a hotel na samesu wai party sukeyi shine suke competition aka wanda yafi shan kwaya da yawa zasu bashi kudi 250k. Su ukun da suke kwance a nan su suke shan kwayar shine da sauran suka ga sun sume duk suka gudu sai abokinsu daya ya kirawo ni ya gaya min don harda kanina a cikinsu. Shima yana gaya min ya gudu, don yanzu ma likitocin tambayar da suke shine a gaya musu sunan kwayar da suka sha don su san irin abun da ya dace suyi musu amma ni ban sani ba; abokan nasu kuma duk sun kashe waya. Gasu can dai su uku a kwance a sume an dai musu allura.’
Yaya Bello yace
‘Subhanallah!’
Matashin da yake yi musu bayani yace
‘Likitan da yake duba su yana wancan office din, ku zo mu karasa sai kuji daga bakinsa.’
Yaya Bello yaja hannun Abban Saddiku wanda ya kasa wani katabus suka bi bayan yaron.
Bayan ya gabatar da su a wajen likitan shima likitan irin bayanan da yayi musu ya sake basu, ya dora da
‘Matsalar itace bamu san irin kwayar da suka sha ba. Shi daya yaron da ya farfado yace sunan kwayar flash dayar kuma rod, a lussafinsa shi kwaya uku ya sha yayinda su kuma suka sha biyar ko shida. Muna bincike kuma muna jira su farfado mu sami ainahin sunan kwayar domin shine zamu san irin abinda ya dace muyi musu.’
Suka yiwa likitan sallama bayan ya sanar dasu idan sun farka za a mayar da su sashen kula da kwakwalwa.
Bayan sun fito daga ofishin suka karasa inda Saddikun yake; yana nan a kwance babu alamar wani motsi a tare da shi idan banda numfashi da yake futarwa a hankali. Suka kare masa kallo Yaya Bello yace
‘Allah ya kyauta.’
Ya janyo hannun Abban Sadik wanda yake binsa kamar mutum-mutumi suka fito bayan sun yiwa yaron godiya sun sanar dashi cewa suna nan a farfajiyar asibitin idan an bukaci wani abu.
Akwai dan waje daga gefen emergency din da kujerun siminti na zama, nan suka je suka zauna. Suna zama Abban ya zuba fuskarsa a tafukan hannunsa yayinda shi kuma Yaya Bellon ya zauna kusa da shi yana nashi nazarin ba tare da yace komai ba.
Sun dauki kusan minti goma haka kafin Abban Sadik ya sauke hannuwansa ya dubi Yaya nasa cike tsananin damuwa yace
‘Allah ya sauwake.’
‘Amin ya Allah.’
‘Wallahi Yaya ban san yanda aka yi Saddiku ya zama haka ba. Kusan mutum uku ne suka yi min magana a kan na binciki yaron nan, don malaminsu na secondary school ma kai tsaye ya gaya min cewa yana shaye-shaye. Amma duk yanda naso na dauki mataki a kai uwarsa ba zata bari ba domin wasu lokutan ko bari na ganshi ma bata yi. Gashi ko an kama shi da laifi ta iya kare shi, wasu lokutan ma kamar shashantar dani take ta mantar dani al’amarinsa. Yanzu ka ga abinda ya faru ko Yaya? Da anyi mata magana sai tace wai ana so a hadani da shi.’
Yaya Bello yace
‘Sha’anin mata ne sai hakuri. Yanzu jira zamuyi ya farfado muji daga bakin likitocin yanda za ayi a taimaka masa don ba zamu barshi haka ba.’
Cikin kunan rai ya cigaba
‘Ka ga tunda har ya kai ya shiga gasar shan kwaya kenan ya dade yana yi har ta bi jikinsa, kuma ma kudi har naira dubu dari biyu ina suka samo su? Ni dai ban taba bawa Saddiku naira dubu goma ba ma ba balle dubu dari biyu ko fiye. Ina ya sami wadannan abokanma?’
Suka cigaba da tattaunawa Yaya Bello yana kwantarwa da Abban hankali yana gaya masa za a samu ya bari in Sha Allahu.
Wajen karfe biyu suka jiyo kiran Sallah daga nesa, Yaya Bello ya dafa Abban yace
‘Ba muyi Sallah ba ai gara mu lekashi sai mu nemi masallaci muyi Sallah ko.’
Suka mike gaba daya.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
38
A nan asibitin suka zauna, sai waya Yaya Bello yayi gida ya sanar da su Asma’u taje ta bawa Hajiya abinci.
Tun shigowarsu abokin Sadik din ya bawa Abban mukullin motar Sadik din ya sanar da shi hotel din da sukayi party din inda a nan motar take. Don haka suna nan zaune ya kirawo wani yaronsa Shamsu yace ya zo ya sameshi a asibitin. Da yake lokacin da suke wayar Shamsun yana court road ba tare da bata lokaci ba ya hawo Babur ya karaso ya samesu. Mukullin motar Mommy din ya bashi ya sanar da shi inda motar take, yace yaje ya dauki motar ya ajiye masa ita a wajensa zai nemeshi. Sukayi sallama ya hau babur dinsa ya kama hanya.
Bayan an idar da sallar la’asar su Abba suka koma inda Saddiku yake kwance. Zuwa lokacin daya yaron wanda ya rigasu farfadowa har an canza masa daki yana tare da iyayensa. Shi kuma daya yaron kanin saurayin da su Abban suka tarar mahaifiyarsu ta riga ta zo inda ta yiwa likitan bayanin tana so su sallameshi zuwa gobe don ita da yaran zasu bi jirgi zuwa Lagos daga can zasu wuce Dubai hutu; tana so likitan ya rubuta mata medical report idan sun je can likitocin zasu sake duba yaronta.
Bayan ta gama bayanin suka gaisa da Abba suka jajantawa juna, likitan yayiwa su Abban bayanin cewa su Saddikun ma yanzu sun farka don haka ana bukatar a samo madara su sha sannan za a canza musu daki inda za a cigaba da kula da lafiyarsu.
Ba tare da bata lokaci ba Abba ya fita ya siyo madarar ya kawo, da taimakon ma’aikaciyar jinya Yaya Bello ya daga Saddikun wanda har zuwa lokacin idonsa yake a rufe ya dura masa madarar aka samu ya sha kadan.
Zuwa karfe biyar da rabi sun dan kara farfadowa domin shi Saddiku har yana kiran Mommy yana wasu zantuka da ba a gane me yake fada. Nan aka turashi a gadon jinya aka mayar dashi wani dakin a sashen kula da kwakwalwa. Aka saka mishi drip kuma aka sake yi masa allurai.
Bayan likitan ya fita Abba ya zauna a kujerar dake ajiye a dakin yayinda Yaya Bello ya tsaya a daidai kan Saddikun yana tofa masa addu’oi.
A hankali yayi shiru ya daina surutun, Yaya Bello ya dawo ya zauna a kujerar dake kusa da wadda Abban yake kai. Ya dubi Abban yace
‘Ko Zahran za a sanarwa saboda a sami wanda zai zo ya kwana da shi mu samu muje gida zuwa safiya ko?’
Cikin sanyin murya yace
‘Eh ba zan ma kirawota ba don bana jin zan iya saurarenta yanzu. Namiji dai ya kamata a samu ko kuma ni din in an jima sai na dawo zuwa safiyar mu gani.’
Yaya Bello yace
‘Ba za ayi haka ba, gamu da samari a dangi. Ko wajen su Jamilun Inna ai za a sami mai kwana da shi ko kwana nawa za ayi. Kuma ma yanzu ina ga Muhammadu zan kirawo ya taho musu da kayan bukata ya zo su kwana da shi tunda ba abu ne da ake so ya baza dangi ba ayi ta faman cewa yana shaye-shaye.’
Kafin Abban ya bashi amsa ya kirawo Karima ya sanar da ita halin da ake ciki, yace ta bawa Muhammadu kudin mota kuma ta zubo musu abincin dare ta bashi abun shimfida suna jiransa idan ya zo sai su tafi.
Muhammadu shine yaron Yaya Bello na farko wanda zai bawa Saddiku kamar shekaru hudu, don a halin yanzu shi yana ajin karshe a Jami’a inda yake karantar aikin jarida.
Nan suka zauna har zuwa lokacin da Muhammadu ya iso sannan sukayi masa sallama suka tafi.
-----------
Tunda Abban Saddiku ya fita ya sanar da ita gasu a asibiti kuma shima bai san me ya sami Saddikun ba don baya cikin hayyacinsa take cikin matsananciyar damuwa. Gashi Abban ya ce kada ta sake ta zo asibitin sannan kuma ya ce ta daina damunsa da waya idan ana bukatar wani abu a wajenta zai nemeta. Haka ta kasa sukuni kuma ta rasa me zata cewa yaran da suke ta faman tamabayarta ko bata da lafiya; don haka kawai sai ta biye musu a kan bata da lafiya sannan kuma Yaya Sadik ma bashi da lafiya yana asibiti Abba ya kai shi.
Har la’asar tana rike da waya tana jiran shigowar kiran Abba ko kuma ta ji shigowarsa gidan amma shiru. Hankalinta ya kara tashi don haka ta sake kiran Yaya Murja ta rushe da kuka. Cikin firgici Yaya Murja tace
‘Subhanallahi! Zahra Saddikun mutuwa yayi ne kike kuka haka? Ki gaya min me ya faru.’
Cikin shesshekar kuka tace
‘Yaya nima ban sani ba Abbanshi yana can tare da shi kuma yaki yayi min bayani har yanzu shiru, cewa ma yayi kada na sake yi masa waya sai ya dawo.’
‘Ikon Allah! To kiyi hakuri mana, na san tabbas da mutuwa Saddiku yayi da yanzu kin ji labari ai lafiya ce take buya akasinta baya buya. Kiyi hakuri zuwa lokacin da zai dawo gidan sai mu ji.’
Suka ajiye waya.
Jimawa kadan kuma Yaya Murja itama ta kasa nutsuwa saboda yanda Zahran take kuka, don haka nan da nan ta barwa abokiyar zamanta girkin da yake nata ta kama haryar gidan Zahra.
Yana shiga ya hango wanda yake waya da shi; yaro ne matashi wanda ba zai wuce shekaru ashirin da biyar ba zuwa da shida. Da hanzari ya karaso wajen su Abban,bayan sun gaisa ya mikawa Abban wayar Saddiku yana fadin
‘Ga wayar Sadik din.’
Ya karba yana fadin
‘Wai me ya samesu ne?’
Cikin damuwa yace
‘To ni dai abokinsu ne ya kirawoni kuma a hotel na samesu wai party sukeyi shine suke competition aka wanda yafi shan kwaya da yawa zasu bashi kudi 250k. Su ukun da suke kwance a nan su suke shan kwayar shine da sauran suka ga sun sume duk suka gudu sai abokinsu daya ya kirawo ni ya gaya min don harda kanina a cikinsu. Shima yana gaya min ya gudu, don yanzu ma likitocin tambayar da suke shine a gaya musu sunan kwayar da suka sha don su san irin abun da ya dace suyi musu amma ni ban sani ba; abokan nasu kuma duk sun kashe waya. Gasu can dai su uku a kwance a sume an dai musu allura.’
Yaya Bello yace
‘Subhanallah!’
Matashin da yake yi musu bayani yace
‘Likitan da yake duba su yana wancan office din, ku zo mu karasa sai kuji daga bakinsa.’
Yaya Bello yaja hannun Abban Saddiku wanda ya kasa wani katabus suka bi bayan yaron.
Bayan ya gabatar da su a wajen likitan shima likitan irin bayanan da yayi musu ya sake basu, ya dora da
‘Matsalar itace bamu san irin kwayar da suka sha ba. Shi daya yaron da ya farfado yace sunan kwayar flash dayar kuma rod, a lussafinsa shi kwaya uku ya sha yayinda su kuma suka sha biyar ko shida. Muna bincike kuma muna jira su farfado mu sami ainahin sunan kwayar domin shine zamu san irin abinda ya dace muyi musu.’
Suka yiwa likitan sallama bayan ya sanar dasu idan sun farka za a mayar da su sashen kula da kwakwalwa.
Bayan sun fito daga ofishin suka karasa inda Saddikun yake; yana nan a kwance babu alamar wani motsi a tare da shi idan banda numfashi da yake futarwa a hankali. Suka kare masa kallo Yaya Bello yace
‘Allah ya kyauta.’
Ya janyo hannun Abban Sadik wanda yake binsa kamar mutum-mutumi suka fito bayan sun yiwa yaron godiya sun sanar dashi cewa suna nan a farfajiyar asibitin idan an bukaci wani abu.
Akwai dan waje daga gefen emergency din da kujerun siminti na zama, nan suka je suka zauna. Suna zama Abban ya zuba fuskarsa a tafukan hannunsa yayinda shi kuma Yaya Bellon ya zauna kusa da shi yana nashi nazarin ba tare da yace komai ba.
Sun dauki kusan minti goma haka kafin Abban Sadik ya sauke hannuwansa ya dubi Yaya nasa cike tsananin damuwa yace
‘Allah ya sauwake.’
‘Amin ya Allah.’
‘Wallahi Yaya ban san yanda aka yi Saddiku ya zama haka ba. Kusan mutum uku ne suka yi min magana a kan na binciki yaron nan, don malaminsu na secondary school ma kai tsaye ya gaya min cewa yana shaye-shaye. Amma duk yanda naso na dauki mataki a kai uwarsa ba zata bari ba domin wasu lokutan ko bari na ganshi ma bata yi. Gashi ko an kama shi da laifi ta iya kare shi, wasu lokutan ma kamar shashantar dani take ta mantar dani al’amarinsa. Yanzu ka ga abinda ya faru ko Yaya? Da anyi mata magana sai tace wai ana so a hadani da shi.’
Yaya Bello yace
‘Sha’anin mata ne sai hakuri. Yanzu jira zamuyi ya farfado muji daga bakin likitocin yanda za ayi a taimaka masa don ba zamu barshi haka ba.’
Cikin kunan rai ya cigaba
‘Ka ga tunda har ya kai ya shiga gasar shan kwaya kenan ya dade yana yi har ta bi jikinsa, kuma ma kudi har naira dubu dari biyu ina suka samo su? Ni dai ban taba bawa Saddiku naira dubu goma ba ma ba balle dubu dari biyu ko fiye. Ina ya sami wadannan abokanma?’
Suka cigaba da tattaunawa Yaya Bello yana kwantarwa da Abban hankali yana gaya masa za a samu ya bari in Sha Allahu.
Wajen karfe biyu suka jiyo kiran Sallah daga nesa, Yaya Bello ya dafa Abban yace
‘Ba muyi Sallah ba ai gara mu lekashi sai mu nemi masallaci muyi Sallah ko.’
Suka mike gaba daya.
UWAR SADDIKU
Written by
Sakina Yazid
(Innar su Amal)
38
A nan asibitin suka zauna, sai waya Yaya Bello yayi gida ya sanar da su Asma’u taje ta bawa Hajiya abinci.
Tun shigowarsu abokin Sadik din ya bawa Abban mukullin motar Sadik din ya sanar da shi hotel din da sukayi party din inda a nan motar take. Don haka suna nan zaune ya kirawo wani yaronsa Shamsu yace ya zo ya sameshi a asibitin. Da yake lokacin da suke wayar Shamsun yana court road ba tare da bata lokaci ba ya hawo Babur ya karaso ya samesu. Mukullin motar Mommy din ya bashi ya sanar da shi inda motar take, yace yaje ya dauki motar ya ajiye masa ita a wajensa zai nemeshi. Sukayi sallama ya hau babur dinsa ya kama hanya.
Bayan an idar da sallar la’asar su Abba suka koma inda Saddiku yake kwance. Zuwa lokacin daya yaron wanda ya rigasu farfadowa har an canza masa daki yana tare da iyayensa. Shi kuma daya yaron kanin saurayin da su Abban suka tarar mahaifiyarsu ta riga ta zo inda ta yiwa likitan bayanin tana so su sallameshi zuwa gobe don ita da yaran zasu bi jirgi zuwa Lagos daga can zasu wuce Dubai hutu; tana so likitan ya rubuta mata medical report idan sun je can likitocin zasu sake duba yaronta.
Bayan ta gama bayanin suka gaisa da Abba suka jajantawa juna, likitan yayiwa su Abban bayanin cewa su Saddikun ma yanzu sun farka don haka ana bukatar a samo madara su sha sannan za a canza musu daki inda za a cigaba da kula da lafiyarsu.
Ba tare da bata lokaci ba Abba ya fita ya siyo madarar ya kawo, da taimakon ma’aikaciyar jinya Yaya Bello ya daga Saddikun wanda har zuwa lokacin idonsa yake a rufe ya dura masa madarar aka samu ya sha kadan.
Zuwa karfe biyar da rabi sun dan kara farfadowa domin shi Saddiku har yana kiran Mommy yana wasu zantuka da ba a gane me yake fada. Nan aka turashi a gadon jinya aka mayar dashi wani dakin a sashen kula da kwakwalwa. Aka saka mishi drip kuma aka sake yi masa allurai.
Bayan likitan ya fita Abba ya zauna a kujerar dake ajiye a dakin yayinda Yaya Bello ya tsaya a daidai kan Saddikun yana tofa masa addu’oi.
A hankali yayi shiru ya daina surutun, Yaya Bello ya dawo ya zauna a kujerar dake kusa da wadda Abban yake kai. Ya dubi Abban yace
‘Ko Zahran za a sanarwa saboda a sami wanda zai zo ya kwana da shi mu samu muje gida zuwa safiya ko?’
Cikin sanyin murya yace
‘Eh ba zan ma kirawota ba don bana jin zan iya saurarenta yanzu. Namiji dai ya kamata a samu ko kuma ni din in an jima sai na dawo zuwa safiyar mu gani.’
Yaya Bello yace
‘Ba za ayi haka ba, gamu da samari a dangi. Ko wajen su Jamilun Inna ai za a sami mai kwana da shi ko kwana nawa za ayi. Kuma ma yanzu ina ga Muhammadu zan kirawo ya taho musu da kayan bukata ya zo su kwana da shi tunda ba abu ne da ake so ya baza dangi ba ayi ta faman cewa yana shaye-shaye.’
Kafin Abban ya bashi amsa ya kirawo Karima ya sanar da ita halin da ake ciki, yace ta bawa Muhammadu kudin mota kuma ta zubo musu abincin dare ta bashi abun shimfida suna jiransa idan ya zo sai su tafi.
Muhammadu shine yaron Yaya Bello na farko wanda zai bawa Saddiku kamar shekaru hudu, don a halin yanzu shi yana ajin karshe a Jami’a inda yake karantar aikin jarida.
Nan suka zauna har zuwa lokacin da Muhammadu ya iso sannan sukayi masa sallama suka tafi.
-----------
Tunda Abban Saddiku ya fita ya sanar da ita gasu a asibiti kuma shima bai san me ya sami Saddikun ba don baya cikin hayyacinsa take cikin matsananciyar damuwa. Gashi Abban ya ce kada ta sake ta zo asibitin sannan kuma ya ce ta daina damunsa da waya idan ana bukatar wani abu a wajenta zai nemeta. Haka ta kasa sukuni kuma ta rasa me zata cewa yaran da suke ta faman tamabayarta ko bata da lafiya; don haka kawai sai ta biye musu a kan bata da lafiya sannan kuma Yaya Sadik ma bashi da lafiya yana asibiti Abba ya kai shi.
Har la’asar tana rike da waya tana jiran shigowar kiran Abba ko kuma ta ji shigowarsa gidan amma shiru. Hankalinta ya kara tashi don haka ta sake kiran Yaya Murja ta rushe da kuka. Cikin firgici Yaya Murja tace
‘Subhanallahi! Zahra Saddikun mutuwa yayi ne kike kuka haka? Ki gaya min me ya faru.’
Cikin shesshekar kuka tace
‘Yaya nima ban sani ba Abbanshi yana can tare da shi kuma yaki yayi min bayani har yanzu shiru, cewa ma yayi kada na sake yi masa waya sai ya dawo.’
‘Ikon Allah! To kiyi hakuri mana, na san tabbas da mutuwa Saddiku yayi da yanzu kin ji labari ai lafiya ce take buya akasinta baya buya. Kiyi hakuri zuwa lokacin da zai dawo gidan sai mu ji.’
Suka ajiye waya.
Jimawa kadan kuma Yaya Murja itama ta kasa nutsuwa saboda yanda Zahran take kuka, don haka nan da nan ta barwa abokiyar zamanta girkin da yake nata ta kama haryar gidan Zahra.