Sashe 72
Karshen Wahala Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Satin su d'aya a Kano sun xagaya gidajen en uwa har kaduna nauwara taje k'wanan ta d'aya ta dawo kano, ranar sunday suka shige abuja saboda makarantar su na'eem da ameer, yanxu saleem ya had'a degree di'n shi akan harkar kasuwanci bai nemi aiki ba Abba ya wulla shi company nin su nauwara dake abuja don ya dunga kula shi ya had'a shi da kwararrun ma'aikata masu tsoron Allah da amana a xuciyoyin su nan da nan company nin ya fara samun cigaba yanxu saleem ganin shi sai week end a Kano sauran k'wanaki biyar di'n a kaduna tun an fara xama babban mutum yanxu aure ya rage mishi don duk wani jin dad'i ya same shi, ammi kullum cikin addu'a take ma yaranta dasu umma da abba da suka rik'e su tsakani da Allah....
Aishat A muh'd
[4/30, 20:18] Umar Dalha: 🍀🍀☘☘🍀🍀
*K'ARSHEN WAHALA*
🍀🍀☘☘🍀🍀
*written by*
Aishat A muh'd
*K'ARSHE* (last page)
Cikin nauwara ya shiga wata na shida yayi girma sosae kamar nasu twins abduljabbar ba k'aramin tausaya mata yake ba kullum ya dawo daga aiki baya fita xai xauna kusa da ita yana lalla6a ta tare da bata labarai masu dad'i da ban dariya ita kuma tana nannad'e a jikin shi tana dariya haka na'eem da ameer xasu xo su kewaye su ana yi dasu kulawa sosai yake bata .
Kamar yau tana xaune a falon down stairs tana sanye da simple gown don tafi mata dad'in sawa gaban ta fruit salad ne abduljabbar yana gefen ta yana bata a baki aka kirawo shi a waya da sauri nauwara ta mik'a mishi wayar da yake tana hannun ta ganin sunan abba ne d'aga wa yayi da sallama bayan ya gaida abba ne yake sanar dashi ammi ta haihu an sami baby boy tuni fuskar abduljabbar ta fad'ad'a da fara'a sosai Alhmdullilah ya furta bayan ya ajiye wayar nauwara wadda ta xuba mishi ido tace
"waya haihu ne?"
"ammi ce ta haihu yanxu an samu baby boy "
Cikin wani irin sauri ta mik'e tsaye tana cewa wanda har sai da marar ta ta d'an murd'a kan a hankali ta dafe wajen tare da furta washh amman bata bi ta kanta ba tare da cewa
"da gaske kake don Allah "
Kamo ta yayi ya xaunar da ita kan kafafun shi ya d'an d'aure fuska yace "ban hana Ki tashi da sauri haka ba sai kin jiwa kanki ciwo? "
Langa6e kai tayi tare da fad'in "sorry " d'an murmishi yayi Kafin yace "da gaske nake miki ammi ta haihu na samu small bro ni ma "
Cikin tsananin murna ta rungume shi tare da cewa "Masha Allah Alhmdllh Yeeeeeee xan je kano "
D'an hararar ta yayi yana cewa "da haka xaki Kano da wannan katon cikin ke da xuwa kano sai kin haihu yarinya "
Kwa6e fuska tayi ta fara kukan shagwa6a ita fah sai taje har da shure shuren kafa irin na yara Idan xasu yi kuka tuni hankalin shi ya tashi don baya k'aunar ganin nauwaran shi a haka nan ya dawo lalla6a ta tare da yarda xasu je sai lokacin ta dai na kukan daman ae na k'ak'ale ne ko hawayen kirki babu sai murxar ido girgixa kai yayi yana murmishi kawai ya d'an ja kumatun ta yana cewa
"habibty rigima don kin ga bana jurar ganin ki Kina cikin damuwa shi yasa kike yanda kike so"
D'an hararar shi tayi da sauri ya dafe baki yana cewa "su6utar baki ne sorry "
Gaba d'aya suka kwashe da dariya sai jin maganar twins suka yi suna cewa "papa mamee dariyar me kuke? "
Abduljabbar da nauwara suka Kalli juna tare da yin murmishi nauwara tace " ammi ce ta haihu an samu boy" nan suka fara tsallen murna suna dariya.
Bayan k'wana 2 da haihuwar suka tarkato xuwa kano har da aunty asma'u da yaranta nan fah gida ya cika da 'ya'ya da jikoki don su fa'iza, aunty kausar, jiddah, aunty safiyya dasu inna da baffah da saleem kamar had'in baki duk rana d'aya suka xo gida ya cika umma da aunty sadiya sun kasa xama waje d'aya sai anan ake dasu, barin ma nauwara motsi Kad'an sai ta tambayi nauwara me take so kula wa sosai take bata, babyn ammi yaci sunan abban su nauwara wato sa'eed don yace ameer mai sunan abban su nauwara daban shi ma nashi sa'eed d'in daban.
Ranar suna jaririn yaci sunan sa'eed suna ce mishi arfat, bayan suna da k'wana 2 su nauwara suka koma abuja, haka lokaci ya cigaba da tafiya cikin nauwara yana wata 8 fa'iza ta haihu d'a namiji tana haihuwa da k'wana 3 jiddah ma Allah ya sauke ta lafia ta samu diya mace murna Wajen jiddah ba'a magana har da kukan ta na farinciki ta gode wa Allah da ya bata haihuwa daman ashe haka yara suke da dad'i wayyo Allah daman ana dawo da rayuwa baya da ta goge abubuwan da ta aikata a cikin rayuwar ta amman ina ya riga da ya wuce sai addu'ar Allah ya gafarta mana kura kuran mu Ameeen
Anyi suna d'an fa'iza yaci sunan daddyn Dr muh'd Wato Abdullah suna kiran shi da daddy sannan er jiddah kuwa Mufeedah suka sanya mata.
K'ememe abduljabbar barin nauwara xuwa suna ita ma bata sa ran xuwan ba saboda yanda cikin ta ya girma sosai ko taje baxa ta sake ba, yanxu nauwara kad'ai ake xuba idon haihuwar ta iyaye da en uwa sai addu'ar sauka lafia suke mata, abduljabbar kuwa tun da cikin haihuwar nauwara ya tsaya tsayuwar dare yake sosai da addu'ar Allah ya sauke ta lafia duk gaba d'aya baya cikin nutsuwar shi saboda tsananin tausayin ta ganin yanda take fama da ciki duk ta kumbura musamman kafafuwan ta.
Tuni saleem sun dinke da Hanan babbar er aunty asma'u suna xuba soyayya kuma kowa yasan da haka a cikin en uwa kuma Anyi farin ciki sosae baran ma nauwara da yake yanxu ta dawo wajen ta da xama tana d'an taya ta ayyukan da er aiki baxa ta yi mata.
Ranar Thursday da safe nauwara ta tashi da nakuda ganin yanda ta ke wahala gaba d'aya Abduljabbar ya gigice ya kid'ime ya ma kasa yin komai sai sannu kawai yake xuba mata, sai da Hanan ta kirawo aunty asma'u nan da nan taxo gidan tana fad'an me yasa bai kaita asibiti, shi sai lokacin ma ya tuna da wani asibiti don duk ya gigice kamar ba soja ba baya jurar ganin habibty di'n shi cikin wahala ne, cikin kankanin lokaci suka isa asibitin aka kaita room d'in haihuwa K'ememe abduljabbar yak'i fita daga d'akin yana rik'e da nauwara yana xuba mata sannu awan su 3 acikin asibitin Kafin nauwara ta haihu tarihi ya mai mai ta kanshi don 'ya'ya biyu reras ta sake haihuwa sai dai duk mata ne kyawawa masu kama da nauwara.
Nan fah murna ta ishe abduljabbar ya rasa inda xai sa kanshi don tsananin farinciki haihuwa 2 amman 'ya'ya hud'u lallai Allah ba k'aramin kyauta yayi mishi ba da ya axurta da nauwara, sai da ya tabbatar nauwara ta dawo dai dai har tayi wanka ta samu baccin hutu tukunna ya kar6o yaran shi daga hannun aunty asma'u har tana mishi tsiya shi dai kawai murmishi yake, nan aka fara kiran en uwa da abokanan arxiki ana sanar dasu nauwara ta haihu ta samu twins duk mata.
Sai dare aka sallame su daga asibitin bayan an tabbatar ba wata matsalar suka dawo gida nan fa na'eem da ameer suka dunga tsallen murna sun samu kanne, washe gari umma da aunty sadiya suka xo ganin yara k'wanan su 2 suka juya xuwa kano, shirye shiryen suna sosai Aunty asma'u take shirya ita dasu fa'iza ana sauran k'wana 2 suna su fa'iza, aunty kausar, jiddah da aunty maryam da aunty safiyya suka taho abuja saboda shirin suna.
Kaya sosai abduljabbar ya had'a wa nauwara da twins na'eem da ameer sannan twins d'in shi mata, nauwara har da kyautar dankareriyar mota da yayi mata tare da wata sark'ar goal mai tsananin tsada ba k'aramin kashe kud'i yayi ba har nauwara tana mishi maganar kashe kud'in Yayi yawa yace mata ta barshi yayi komai yana da lokaci kuma sun fi k'arfin komai a wajen shi rungume shi nauwara tayi tana jin dad'in yanda Allah ya bata miji nagari.
Kaiii twins fa sunyi goshi kaya ta ko'ina nauwara take samu umma, Abba, ammi, aunty sadiya, aunty asma'u, aunty kausar, aunty maryam, aunty safiyya, inna, baffah, saleem, fa'iza, jiddah dukkan su kowanne da nashi abin arxikin nauwara har ta rasa bakin godiya har da aiken Dr muh'd da aminu kaya masu tsada sosai wai a sawa twins.
Abdulkareem ma kyautar ta daban ya aikowa da twins har da sark'ar goal guda biyu masu tsada, ya taya abokin shi murnar samun twins.
Ranar suna twins sun ci sunan umma fatyma d'ayar kuwa taci sunan safah sai suke kiran wanda taci sunan umma marwa kenan safah da marwah sai fatan Allah ya raya su cikin addinin islama,walimah su aunty asma'u suka shirya anci ansha an watse.
Bayan suna da k'wana 2 kowa ya watse aka bar nauwara da abduljabbar sai en yaran su a gida suna cigaba da kula wa dasu cikin tsananin farinciki da k'aunar yaran nasu.
Bayan sunyi arba'in suka yo kano suka yi sati d'aya sannan taje kaduna tayi wa su inna k'wanaki uku acan sannan suka koma abuja, a dai dai lokacin aka yanke bikin saleem da Hanan wata biyu masu xuwa don Abba yace baxai shige wannan axumin ba bai yi mishi aure ba.
Komai nisan lokaci aka sa xai xo har ya shige dashi nan har bikin saleem yaxo duk wasu shirye shirye an gama sun tarkato kano gaba d'aya don a gabatar da bikin da yake kuma mijin aunty asma'u shi iyayen shi en kano ne don hka komai yaxo da sauk'i an kammala biki lafia amarya Hanan ta tare a gidan ta da yake kaduna, daga hka kowa ya tarwatse ya nufi nashi gidan.
*BAYAN SHEKARU 6*
Aishat A muh'd
[4/30, 20:18] Umar Dalha: 🍀🍀☘☘🍀🍀
*K'ARSHEN WAHALA*
🍀🍀☘☘🍀🍀
*written by*
Aishat A muh'd
*K'ARSHE* (last page)
Cikin nauwara ya shiga wata na shida yayi girma sosae kamar nasu twins abduljabbar ba k'aramin tausaya mata yake ba kullum ya dawo daga aiki baya fita xai xauna kusa da ita yana lalla6a ta tare da bata labarai masu dad'i da ban dariya ita kuma tana nannad'e a jikin shi tana dariya haka na'eem da ameer xasu xo su kewaye su ana yi dasu kulawa sosai yake bata .
Kamar yau tana xaune a falon down stairs tana sanye da simple gown don tafi mata dad'in sawa gaban ta fruit salad ne abduljabbar yana gefen ta yana bata a baki aka kirawo shi a waya da sauri nauwara ta mik'a mishi wayar da yake tana hannun ta ganin sunan abba ne d'aga wa yayi da sallama bayan ya gaida abba ne yake sanar dashi ammi ta haihu an sami baby boy tuni fuskar abduljabbar ta fad'ad'a da fara'a sosai Alhmdullilah ya furta bayan ya ajiye wayar nauwara wadda ta xuba mishi ido tace
"waya haihu ne?"
"ammi ce ta haihu yanxu an samu baby boy "
Cikin wani irin sauri ta mik'e tsaye tana cewa wanda har sai da marar ta ta d'an murd'a kan a hankali ta dafe wajen tare da furta washh amman bata bi ta kanta ba tare da cewa
"da gaske kake don Allah "
Kamo ta yayi ya xaunar da ita kan kafafun shi ya d'an d'aure fuska yace "ban hana Ki tashi da sauri haka ba sai kin jiwa kanki ciwo? "
Langa6e kai tayi tare da fad'in "sorry " d'an murmishi yayi Kafin yace "da gaske nake miki ammi ta haihu na samu small bro ni ma "
Cikin tsananin murna ta rungume shi tare da cewa "Masha Allah Alhmdllh Yeeeeeee xan je kano "
D'an hararar ta yayi yana cewa "da haka xaki Kano da wannan katon cikin ke da xuwa kano sai kin haihu yarinya "
Kwa6e fuska tayi ta fara kukan shagwa6a ita fah sai taje har da shure shuren kafa irin na yara Idan xasu yi kuka tuni hankalin shi ya tashi don baya k'aunar ganin nauwaran shi a haka nan ya dawo lalla6a ta tare da yarda xasu je sai lokacin ta dai na kukan daman ae na k'ak'ale ne ko hawayen kirki babu sai murxar ido girgixa kai yayi yana murmishi kawai ya d'an ja kumatun ta yana cewa
"habibty rigima don kin ga bana jurar ganin ki Kina cikin damuwa shi yasa kike yanda kike so"
D'an hararar shi tayi da sauri ya dafe baki yana cewa "su6utar baki ne sorry "
Gaba d'aya suka kwashe da dariya sai jin maganar twins suka yi suna cewa "papa mamee dariyar me kuke? "
Abduljabbar da nauwara suka Kalli juna tare da yin murmishi nauwara tace " ammi ce ta haihu an samu boy" nan suka fara tsallen murna suna dariya.
Bayan k'wana 2 da haihuwar suka tarkato xuwa kano har da aunty asma'u da yaranta nan fah gida ya cika da 'ya'ya da jikoki don su fa'iza, aunty kausar, jiddah, aunty safiyya dasu inna da baffah da saleem kamar had'in baki duk rana d'aya suka xo gida ya cika umma da aunty sadiya sun kasa xama waje d'aya sai anan ake dasu, barin ma nauwara motsi Kad'an sai ta tambayi nauwara me take so kula wa sosai take bata, babyn ammi yaci sunan abban su nauwara wato sa'eed don yace ameer mai sunan abban su nauwara daban shi ma nashi sa'eed d'in daban.
Ranar suna jaririn yaci sunan sa'eed suna ce mishi arfat, bayan suna da k'wana 2 su nauwara suka koma abuja, haka lokaci ya cigaba da tafiya cikin nauwara yana wata 8 fa'iza ta haihu d'a namiji tana haihuwa da k'wana 3 jiddah ma Allah ya sauke ta lafia ta samu diya mace murna Wajen jiddah ba'a magana har da kukan ta na farinciki ta gode wa Allah da ya bata haihuwa daman ashe haka yara suke da dad'i wayyo Allah daman ana dawo da rayuwa baya da ta goge abubuwan da ta aikata a cikin rayuwar ta amman ina ya riga da ya wuce sai addu'ar Allah ya gafarta mana kura kuran mu Ameeen
Anyi suna d'an fa'iza yaci sunan daddyn Dr muh'd Wato Abdullah suna kiran shi da daddy sannan er jiddah kuwa Mufeedah suka sanya mata.
K'ememe abduljabbar barin nauwara xuwa suna ita ma bata sa ran xuwan ba saboda yanda cikin ta ya girma sosai ko taje baxa ta sake ba, yanxu nauwara kad'ai ake xuba idon haihuwar ta iyaye da en uwa sai addu'ar sauka lafia suke mata, abduljabbar kuwa tun da cikin haihuwar nauwara ya tsaya tsayuwar dare yake sosai da addu'ar Allah ya sauke ta lafia duk gaba d'aya baya cikin nutsuwar shi saboda tsananin tausayin ta ganin yanda take fama da ciki duk ta kumbura musamman kafafuwan ta.
Tuni saleem sun dinke da Hanan babbar er aunty asma'u suna xuba soyayya kuma kowa yasan da haka a cikin en uwa kuma Anyi farin ciki sosae baran ma nauwara da yake yanxu ta dawo wajen ta da xama tana d'an taya ta ayyukan da er aiki baxa ta yi mata.
Ranar Thursday da safe nauwara ta tashi da nakuda ganin yanda ta ke wahala gaba d'aya Abduljabbar ya gigice ya kid'ime ya ma kasa yin komai sai sannu kawai yake xuba mata, sai da Hanan ta kirawo aunty asma'u nan da nan taxo gidan tana fad'an me yasa bai kaita asibiti, shi sai lokacin ma ya tuna da wani asibiti don duk ya gigice kamar ba soja ba baya jurar ganin habibty di'n shi cikin wahala ne, cikin kankanin lokaci suka isa asibitin aka kaita room d'in haihuwa K'ememe abduljabbar yak'i fita daga d'akin yana rik'e da nauwara yana xuba mata sannu awan su 3 acikin asibitin Kafin nauwara ta haihu tarihi ya mai mai ta kanshi don 'ya'ya biyu reras ta sake haihuwa sai dai duk mata ne kyawawa masu kama da nauwara.
Nan fah murna ta ishe abduljabbar ya rasa inda xai sa kanshi don tsananin farinciki haihuwa 2 amman 'ya'ya hud'u lallai Allah ba k'aramin kyauta yayi mishi ba da ya axurta da nauwara, sai da ya tabbatar nauwara ta dawo dai dai har tayi wanka ta samu baccin hutu tukunna ya kar6o yaran shi daga hannun aunty asma'u har tana mishi tsiya shi dai kawai murmishi yake, nan aka fara kiran en uwa da abokanan arxiki ana sanar dasu nauwara ta haihu ta samu twins duk mata.
Sai dare aka sallame su daga asibitin bayan an tabbatar ba wata matsalar suka dawo gida nan fa na'eem da ameer suka dunga tsallen murna sun samu kanne, washe gari umma da aunty sadiya suka xo ganin yara k'wanan su 2 suka juya xuwa kano, shirye shiryen suna sosai Aunty asma'u take shirya ita dasu fa'iza ana sauran k'wana 2 suna su fa'iza, aunty kausar, jiddah da aunty maryam da aunty safiyya suka taho abuja saboda shirin suna.
Kaya sosai abduljabbar ya had'a wa nauwara da twins na'eem da ameer sannan twins d'in shi mata, nauwara har da kyautar dankareriyar mota da yayi mata tare da wata sark'ar goal mai tsananin tsada ba k'aramin kashe kud'i yayi ba har nauwara tana mishi maganar kashe kud'in Yayi yawa yace mata ta barshi yayi komai yana da lokaci kuma sun fi k'arfin komai a wajen shi rungume shi nauwara tayi tana jin dad'in yanda Allah ya bata miji nagari.
Kaiii twins fa sunyi goshi kaya ta ko'ina nauwara take samu umma, Abba, ammi, aunty sadiya, aunty asma'u, aunty kausar, aunty maryam, aunty safiyya, inna, baffah, saleem, fa'iza, jiddah dukkan su kowanne da nashi abin arxikin nauwara har ta rasa bakin godiya har da aiken Dr muh'd da aminu kaya masu tsada sosai wai a sawa twins.
Abdulkareem ma kyautar ta daban ya aikowa da twins har da sark'ar goal guda biyu masu tsada, ya taya abokin shi murnar samun twins.
Ranar suna twins sun ci sunan umma fatyma d'ayar kuwa taci sunan safah sai suke kiran wanda taci sunan umma marwa kenan safah da marwah sai fatan Allah ya raya su cikin addinin islama,walimah su aunty asma'u suka shirya anci ansha an watse.
Bayan suna da k'wana 2 kowa ya watse aka bar nauwara da abduljabbar sai en yaran su a gida suna cigaba da kula wa dasu cikin tsananin farinciki da k'aunar yaran nasu.
Bayan sunyi arba'in suka yo kano suka yi sati d'aya sannan taje kaduna tayi wa su inna k'wanaki uku acan sannan suka koma abuja, a dai dai lokacin aka yanke bikin saleem da Hanan wata biyu masu xuwa don Abba yace baxai shige wannan axumin ba bai yi mishi aure ba.
Komai nisan lokaci aka sa xai xo har ya shige dashi nan har bikin saleem yaxo duk wasu shirye shirye an gama sun tarkato kano gaba d'aya don a gabatar da bikin da yake kuma mijin aunty asma'u shi iyayen shi en kano ne don hka komai yaxo da sauk'i an kammala biki lafia amarya Hanan ta tare a gidan ta da yake kaduna, daga hka kowa ya tarwatse ya nufi nashi gidan.
*BAYAN SHEKARU 6*