← Book details Karshen Wahala Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 60 OF 73

Sashe 60

Karshen Wahala Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yana nan xaune suka fito a shirye duk sun canja kayan jikin su alamar wanka tayi ita dasu na'eem da ameer tana rik'e da key d'in mota a hannun ta d'aya hannun tana rik'e da waya mak'ale a kunnen ta hira suke da doctor muh'd yana tambayar ta K'arshen wasan su ita da twins sai abin ya bata dariya don hka ta dunga er dariyar ta cike da jan aji, ya xuba mata ido kallon ta kawai yake don tayi bala'in yi mishi kyau tana sanye da wata yellow da bak'in gown tayi rolling da veil bak'i da adon flowers yellow sai tayi amfani da black shoes marasa tudu sosai maganar da tayi ita ta dawo dashi hayyacin shi wanda ta kusan haddasa mishi bugawar xuciyar shi
"Haba doctor kada ka damu Allah ya kawo ka lafia kai dai idan kaxo xaka ga irin kewar ka damu kayi "
D'an langa6e kai tayi tana sauraran abin da yake cewa ganin Yah abduljabbar ya xuba mata ido da alamar ranshi ya fara 6aci don hka ta dad'a shagwa6e wa tace
"ah ka wuce nan a wurina Bari naje na dawo xamu shan ice cream ne"
Cikin mamaki tace "kishi kuma? ",
"Haba kasan bana kula kowa sai kai saboda xuciya ta..........."
Kafin ta ankara taji an warce wayar da sauri ta d'ago kanta karaf suka had'a ido da abduljabbar idanun shi sunyi jawur dasu sai faman huci yake duk da ta tsorata da ganin yanayin shi amman sai ta dake cikin d'aure fuska tace
"lafia ina waya ka kar6e min? "
Wata harara ya watsa mata kafin kuma a fusace yace
"da uban wa kike waya?"
Sam ta manta dasu twins a wajen ta turo baki gaba sannan tace
"da my sweet darling nake Mag........ "
kafin ta K'arasa fad'i taji an murd'e bakin nata da k'arfi axaba ta ishe ta ga ba bakin yin ihu umma ta kawo agaji sai da yaga ta jigata idanun ta sunyi ja ga hawaye yana fita a idon sannan ya cikata wani wahalalen numfashi take sauke wa wata er k'ara ta saki jin ya kamo gashin kanta da hannun shi cikin tsawa yace
"wlh na sake jin Kinyi waya da wani katon sai nayi 6a66allaki a gidan nan "
"wlh baka isa ka hanani kula kowa ba kuma wallahi baxan yarda da wannan muguntar ba ina ruwan ka dani da bakin ka kace ka tsanane fah naje nayi rayuwar da nake so "
Lokaci d'aya jikin shi yayi wani bala'in yin sanyi a hankali ya cika mata gashin kanta ya xube kan kujera tare da nutsar da hannun shi cikin gashin kanshi, kallon shi tayi taja tsaki tare da kama hannun su twins wad'anda har sun fara kuka ganin mameen su na kuka da kanta tayi driving d'in xuwa wurin shan ice cream da pizza nd shawarma ta siyo sannan suka dawo gida

Lokacin da ta shiga falo ba k'aramin mamaki tayi ba ganin har yanxu abduljabbar yana nan Inda ta barshi sai dai yanxu ya kwanta a rigingine kan kujerar ta6e baki tayi ta shige kitchen don sanya ice cream a frige sannan ta fito ta tarar na'eem da ameer sun sake dashi har suna bashi labari yana d'an murmishi tare da shafa musu kan su ganin ta fito daga kitchen yasa shi mik'e wa tsaye yana cewa
"taimaka min da abinci I'm hungry "
Bata Kalli Inda yake ba tayi gaba tana cewa
"ka nemi house girl ta baka ni bani da wannan time d'in "
"nauwarah bakya afuwa ne, na baki hak'uri kinki ki hak'ura "
"ehh baxan hak'ura ba din "
Jin alamar ya biyo bayan ta yasa ta watsar da ledar hannun ta ta shawarma ta xura a guje ta fad'a d'aki tare da murxa key
Sunkuya wa yayi ya d'auki ledar ya dawo falo wajen na'eem da ameer wanda gaba d'aya hankalin su yana kan tv suna kallon cartoon a tashar mbc 3 suna shan ice cream di'n su hankali kwance

Sai da ya cinye shawarma biyu Sannan ya tashi ya d'auko fresh milk mai sanyi yasha cikin glass cup d'aya sannan yaji shi dai dai don k'wanakin nan ba k'aramin hora kanshi da yunwa yake ba

A hka umma ta dawo ta ganshi Ko kallon Inda yake bata yi ba ta haye stairs fa'iza ce ta gaida shi ita ma ta wuce saleem ne ya xauna kusa dashi ya gaida shi sannan suka fara er hira bai nuna mishi komai don yana son abduljabbar sosai guy d'in yana birge shi kuma yana nan yana addu'a sai sun mayar da auren su da aunty nauwara sai da aka kirawo sallahr mangarib sannan suka tafi masallaci acan suka hadu da abba dakyar abba ya amsa mishi gaisuwar shi duk jikin abduljabbar yayi masifar yin sanyi dole ya nemi su abba su yafe mishi ko yaga dai dai a rayuwar shi iyaye sun fi k'arfin wasa fushin su ba k'aramin tashin hankali ba ne akan shi

Har falon abba abduljabbar ya bishi ya dunga bashi hak'uri akan laifin da yayi tare da alkawarin baxai sake aikata hkan ba sharrin xuciya ce da rashin bincike dakyar abba ya hak'ura sannan yayi mishi nasiha sosae akan saurin yanke hukuncin cikin fushi daga K'arshe ya nemi da dole ya mayar da jiddah d'akin ta don baxai xauna a haka ba laifi ne tunda ta riga ta aikata ya wuce sannan tayi nadama sosae don taxo ta bamu hak'uri har da nauwara kuma ta hak'ura ta yafe mata

Bashi da yanda xai yi ya amince da abin da abba yace tunda sulhu yake nema can kuma yace
"am uhm abba don Allah nauwara fah ina son na mayar da ita "
Wani kallo abba ya watsa mishi ba shiri yayi shiru fuska a d'aure yace
"ai nauwara Kun rabu har abada tunda kayi kunnen uwar shegu da abin da umman ka tace gwara ta xa6i wanda xata iya jin dad'in xama dashi wanda xai dunga bincike Kafin ya xartar da hukunci "
Da k'arfi abduljabbar yace "nooo Abba kada kace hka ina son ta idan na rasa ta xan iya shiga wani hali ka taimaka min Abba na same ta nayi alkawari baxan sake aikata hkan ba please "
Sosai ya bawa Abba tausayi amman ya dake yak'i nuna mishi yaji tausayin shi don yana so ya shiga taitayin shi gaba baxai sake aikata hkan ba
"ni na gama magana tashi ka ban wuri xan huta"
Kallon abban yayi sannan yace "I'm sorry Abba Idan na 6ata maka rai Gud nyt "
yana fad'in hka ya fice daga falon jikin shi a matuk'ar sanyaye Kai tsaye part d'in shi dake cikin gidan ya nufa ko'ina tsaf a gyare xube wa yayi kan bed bai ankara ba sai jin saukar abu mai d'umi yaji afuskar shi alamar hawaye ne ya kasa rik'e su har sai da suka xubo mishi kusan Kwana yayi baiyi baccin kirki ba sai juye juye xuciyar shi a kuntace

Tun daga ranar nauwara da abduljabbar basu sake had'u ba da junan su duk da yana bala'in son ganin nata kuwa amman ba fuska wajen umma

Misalin karfe 5 na yamma nauwara tayi parking d'in motar su a bakin jifatu store suka fito ita da fa'iza daga motar sun ci gayu cikin wata atampha d'inkin fitted gown kowannen su sai dai different colours na atamphar sunyi matuk'ar yin kyau Idan ka Kalli nauwara baka ce ta haifi na'eem da ameer ba kai tsaye cikin jifatun suka shiga nan suka fara duba abubuwan da suke buk'ata tana cikin duba perfumes taga wanda take nema takai hannu xata dauka sai taga wani hannu daban ya d'auke shi da sauri d'an d'ago ido tayi don taga wane wannan karaf suka had'a ido da wani kyakkyawan matashi yana murmishi a fuskar shi ta juya xata tafi taji yace
"nauwarah ina saleem?? "
cikin tsananin mamaki ta juyo ta kalle shi har yanxu murmishi ne a fuskar shi
"Kina mamaki ne Inda na sanku nasan baxa ki gane ni ba da saleem yana nan xai gane ni"
"don Allah malam kai wane, ina kasan mu? "
"Aminu ne"
Ya fad'a mata "wanne aminu kuma? "
"Aminu mijin hindatu wanda kuka xauna a hannun shi "
xaro ido tayi cike da tsantsar mamaki da farin ciki take kallon shi tace
"don Allah da gaske kai ne "
"wallahi nine nauwara tun lokacin da kuka shigo na gane ki ban k'ara tabbatar da hkan ba sai da na kirawo sunan ki dana saleem naga kin jiyo sannan na gane ki"
Nan suka gaisa tace "ina aunty hindatu da yara "
"sunan tare ma muke dasu ai xaku gaisa "
Cikin er dariya tace "ah mai xai hana kuwa"
Fa'iza wadda take gefe tana kallon su nauwara ta gabatar mishi da ita suka gaisa suna tsaye suna er hira duk nauwara ta tak'ura sosai da yanda aminu yake kallon ta tsoron ta kada matar shi hindatu ta xo yana wannan kallon nata.......

( _dafatan mai karatu baku mance aminu wanda ya taimaki su nauwara har suka xauna a hannun shi Kafin hindatu matar shi ta kore su daga gidan_)

Aishat A muh'd

🍀🍀☘☘🍀🍀
*K'ARSHEN WAHALA*
🍀🍀☘☘🍀🍀

*written by*
Aishat A muh'd

*~Pg 89~*

A fusace ya K'arasa wajen aminu ya mik'a mishi hannu alamar su gaisa wani kallon kaskanci yake watsa mishi kafin ya juyo kan nauwara wadda ta had'e fuska tana jiran taji da mai yaxo Kafin ta ankara taji ya fisgo hannun ta yana janta har xuwa falon umma suka bar aminu a tsaye baki bud'e yana tunanin shi kuma wannan wane, don baisan abduljabbar kuma bai ta6a ganin twins ba da yasan wane shi kamar yanda Dr muh'd ya gane shi ba tare da an fad'a mishi ba, haka yaja motar shi jikin shi a sanyaye ya bar gidan
Chapter 60 · 0% Book details