Sashe 9
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shi dai Kam bai ma san tana yi ba don hasali ma shi kwata kwata hankalinshi baya wurinsu yana cen tunanin ta yaya zai iya zama kauyen har ma yayi rayuwa a cikinta?.
Bayan sun shige ne Maigarin ya dawo da hankalinshi garesu ya Kai kallonshi ga Dijen yace,. "Wai ke me yasa ba kya jin kunyar yin k'arya? Idan baki gane abunda takardar ta kunsa ba ai sai ki bari wad'anda suka sani suyi bayani yafi da ki tayarwa da mutane hankali a banza"
Dije ta muskuta ta kalli Tambari ta mere masa baki tace,. "Ai Ni na zaci sak'on da ke ciki kenan don na gansu da kayan sojoji"
Maigari zai sake yin magana Liman yayi saurin fad'in,. "ALLAH ya kyauta yanzu ayi abunda yasa aka taraku dai ba wani zakale zakalen magana aka ce ki zo wa mutane ba da su ba"
Ya katse abun ne don gudun kuma wata b'araka ta kunno Kai ganin sababbin bak'in da suka zo kar su fara cin karo da abunda zai saka su fara jin dama basu zo kauyen ba.
Maigarin ya gyara zamanshi yayi gyaran murya yace,. ,"Miye hadinki da Tambari har kika watsa masa k'asa a Ido kikasa yaji ciyo a hannu ya buge goshinshi?"
Dije ta makawa Tambari harara tace,. "WALLAHI Ni ba dashi nike fad'ana ba don Ni har ma muka gama fad'an ban ma ganshi a wurin ba, sai zan bar wajen ne ma na hangoshi yana mukususu"
Liman yakalli Dije da kyau yace,. "Kiji tsoron ALLAH ki fad'i me ya hadaki da shi?"
Dije ta Sosa kanta tace, "Eh to tunda kace tsakanina da ALLAH WALLAHI ba dashi nike fad'a ba shine ya shigarwa Kanwarshi ya zo zai dakeni Ni Kuma na watsa masa k'asa a ido yaje ya buge da icce ya jiwa kanshi ciyo, idan kuma ba'a yarda ba a tambayi su Hansai gasu nan ai"
Maigarin ya kurawa Dije Ido yana karantar yanayinta sannan yace,. "To munji wannan shi kuma Kiran Mahaifiyarshi da kika yi barauniya fa wa ta tab'a yiwa sata a gabanki"
Dije ta zabura tsaye tace,. "Ai WALLAHI ko a gabanta zan fad'a don tasan naganta lokacin da ta yiwa Innarsu Ladiyo sata har ma na fad'awa Innar Ladiyon sai ko gashi da aka binciketa anga kud'in saboda cikin dankwalinta ta b'oyesu, har ma ........."
Sunne Kan da Babansu Tambari yayi yana girgizar kai yasa Maigarin saurin dakatar da ita yace,. "To munji baki abun magana amman kisani ko da wasa kika sake cewa da ita barauniya sai kin karb'i hukunci, don Kinga wad'annan bak'in to su zan baiwa ke su kaiki birni asakaki gidan kaso a rufe ayi ta gana maki azaba, kinga shikenan bazaki sake ganin Innarki da Baffahnki ba, muma mu huta da bari barin da kike sakamu kullum safiya, haka fa kika fasawa yarinyar cen Bintalo goshi suka kawo kararki anan na basu hakuri dakyar suka hak'ura, yanzu haka ma Uwar d'akina tana cen tana fama da k'afa tun lokacin da kika zo muna da zancen Kura, to kiji ki k'ara ji kika yarda kika sake wani laifi a wannan karon ba zaki sha ta dad'i ba"
Dije ta yi fiki fiki da Ido alamun tsoro ya shigeta fuskarta a kumbure tace,. "To ai sune suke tsokalo fad'an ko banso muyi fad'a ba sai sun janyo anyi, suma a ja masu kunne su daina shiga sabgata"
Maigari yayiwa Tambari da Dijen iyaka haka ma su Hansai duka sai da ya ja masu kunne sosai akan kada su koma janyo abunda zai had'asu fad'a da kowa a garin bale ita kanta Dijen.
Haka aka gama aka baiwa Mahaifinsu Tambari hak'uri aka aje akan za'a ga Baffann Dije idan ya dawo shima a sanar dashi ya ja kunnuwan 'yarshi.
Har sun tashi zasu bar wajen Dije ta koma ta zauna tace,. "Nace ciyawar ita Kam har yanzu ba'a Kai ba"
Maigarin ya kawar da kanshi gefe yace,. "Kije Gida idan baki ganta ba ki dawo ki karb'a"
Dije ta mike cikin sanyin jiki tace,. "WALLAHI fa yau ban tafi Daji ba idan akuyata bata ci ciyawar ba hanamu baccin dare zata yi"
Maigarin ya waigo cikin b'acin Rai yace,. "To kunatau! Kije tana cen nace akai maki idan an yo"
Sannan Dije ta washe Baki tace,. "Yawwa Nagode ALLAH yasa kafi haka dussar ma ankai nagode duka amman har da gobe zaka aiko man ko?"
A kufule ya d'aga murya yace,. "Har jibi ma kije Gida shikenan"
Dije ta lak'ama kafad'ar su Ladiyo suka tafi suna ta firarsu suna dariya, har sunyi nisa Dije ta dafe Baki tace dasu
"Wai kun ga abunda na gani kuwa?"
Lanti Jummala da Ladiyo Hansai suka had'a baki wajen fad'in
"Bamu kanun labaran mu sha?"
Dije ta sassafta murya tace,. "Kunga wani fi'ili wai Namiji da shafa janbaki?"
Ladiyo ta kyakyalkyale da dariya tace,. "Ashe ba Ni kad'ai nagani ba?"
Hansai tace,. "Kuka sani ko haka Bakinshi yake?"
Lanti tace,. "Injiwa? Baki ganin yanda yake fari tass! Ai irinsu ance cikin injin ake sakasu ana wankesu, garin wankin nasu ne ma bakinsu yake yin ja irin haka"
Dije ta yi wani mere tace,. "Tirr ALLAH ya rabani da canza halittar da Ubangiji ya bani haka kawai garin wankan injin d'in a wanke da zuciyata ta fashe in mutu"
Hansai tace "Ameen to amman naji ance zasu dinga karantar da mu to me zasu karanta muna?"
Lanti tace,. "Wai Boko mu da ko Makarantar ma ba wani zuwanta ake yi ba za'a yi wahalar d'aukosu a kawosu garin nan"
Dije ta harareta tace,. "Kece dai bakya zuwa nikam duk ranar da nasan malamai zasu zo ai kinsan ina zuwa, ku ne dai ba kwa son karatun Shiyasa duk cikinku babu wadda ta iya abacada"
Hansai zata yi magana Ladiyo ta rufe mata Baki tace,. "Ni dai ku zo muje gida kar aga mun dad'e tunda an kashe rigimar"
Hansai tayi gaba Ladiyo tabi bayanta Suka tafi, Dije ta kalli Lanti da Jummala tace,. "Ni fa kunsan me?"
Suka ce "sai kin fad'a"
Dije ta janyo kansu ta yi masu kus kus d'in cewa,. "So nike muje mu ga wadancen bak'in Yan bokon muji shi wancen Mai wankan injin d'in ko ya iya hausar shi"
Lanti ta zaro Ido tace, "Bakiji kashedin da aka yi muna ba halan? Ni dai WALLAHI ban zuwa babu ruwana kunga tafiyata"
Dije ta kalli Jummala tace,. "Kema jeki abunki amman ku sani WALLAHI sai kunsan Ni kuka yiwa rashin nasiha"
Jummala ta kalli Lanti da ke ta sauri ta bar waen ta dawo da kallonta ga fuskar Dije take ta ciccika tana harararta cikin tsoron hukuncin da zata yi masu tace,. "Ni dai muje in raka kin"
Dije ta washe baki tace,. "Ko ke fa zo muje su Kuma ki barni da su zamu had'u ai"
Jummala cikin tsoro da kashedin da Maigarin yayi masu ta bi Dije Suka zagaya ta bayan gidan Maigarin har suka kai bakin k'ofar d'akin da aka ajiye bak'in cikin sanda Dije itace a gaba ta saka hannu ta yaye labulen kad'an ta leka kanta, aiko ta hango dan farin yana sauya tufafi ya zura dogon wandonshi kenan idonshi suka yi caraf da na Dije, aiko ba shiri ta saki labulen aguje ta falfala da gudunta saboda tsoron ganinshi da tayi daga shi sai guntun wando, saboda a rayuwarta kaf bata tab'a cin karo da wani a hakan ba sai ranar.
Mutumin kam cikin sauri ya saka wandon ya mayar da rigar ya fito d'akin da sauri sai dai ko kurar Dije bai hango ba sai Jummala da ke gudu itama a k'ok'arinta na son ganin ta taradda Dijen da ta samu tasha kwana sai balbala gudu take yi kamar wacce zata tashi sama.
Yayi kwafa ranshi a b'ace ya yi tsaye Yana nazarin mafita sannan ya koma d'akin inda ya taradda abokin tafiyarshi ya dawo da kwanon abincin da Maigarin ya Aiko masu.
Cikin tsananin b'acin Rai ya zauna yana huci cikin harshen turanci yace,. "Bazan iya zama a garin nan ba gaskiya , sai da na fad'awa Mama bazan zo ba ta matsa man in zo to ai gashi nan na fara cin karo da takaicin babbak'un kauyawan"
Abokin tafiyarshi yace ,. "Plss Safwan ka fahimci abunda ake so ka gane mana, yanzu miye aibin garin nan ne? gashi Maigarin da mutaneshi sai ina zasu sakamu suke yi sun karbemu hannu bibbiyu fa"
Wanda aka Kira da safwan d'in ya wani mere baki ya gallawa abokin tafiyar tashi harara ya buga wani uban tsaki yace,. "WALLAHI da naga abunda bazan iya ba Ni fecewata zanyi in barka kaji da su, don bazan zauna takaicinsu ya kar ni ba a banza, yanzun nan fa ina k'ok'arin canza kayana ne na hango idon wata bak'ar mage ta zuro Kai tana kallona"
Abokin tafiyarshi ya kyalkyale da wata arniyar dariya yace,. "Anan din ma ka sake had'uwa da wata magen kenan? To kasani ko ita wannan d'in itace Matar ba magen da ka baro a cen ba"
Safwan saboda tsabar takaici ko kallonshi bai sake yi ba yana kammala saka kayan yayi kwanciyarshi, tare da janyo wayarshi da nufin ya yi kira aiko sai gashi yaga gaba d'aya kaf layukanshi babu d'aya mai network duk sun d'auke.
Ba shiri ya Mik'e zaune cikin harshen turanci yace. "Oh sheet! Wannan wane irin bak'in gari ne haka? gaba d'aya basu da service fa ko d'aya"
🤣🤣🤣🤣wasa farin girki shin su waye su Kuma bak'in Yan bokon????.
Akafta😛
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Jinjinar ban girma gareki masoyiyata ta asali mai Sona da zuciya d'aya Yar kanawa d'iyar mutan Yola Alkharin ALLAH ya Kai maki har gadon baccinki, Ina alfakhari da samunki gareni AISHA YOLA kisani sonki cikin jinina yake ALLAH ya bar mu tare har aljannah gaba dai gaba dai tawajena makiyanki fadawanki😛*
*BAK'ON YANAYI COMPLETE ga Mai b'ukata 300 kacal Mai so ta tuntubeni ta wannan number 09032685442*
*Lamba ta 10*
Dije kam tana gudu tana haki har takai gindin wata bishiya ta fadi zaune k'asa tana sauke nishi a wahalce saboda Uban gudun da ta kwaso, Jummala ta k'araso itama tana haki ta fad'i kusa da ita tana hakin tana fad'in
Bayan sun shige ne Maigarin ya dawo da hankalinshi garesu ya Kai kallonshi ga Dijen yace,. "Wai ke me yasa ba kya jin kunyar yin k'arya? Idan baki gane abunda takardar ta kunsa ba ai sai ki bari wad'anda suka sani suyi bayani yafi da ki tayarwa da mutane hankali a banza"
Dije ta muskuta ta kalli Tambari ta mere masa baki tace,. "Ai Ni na zaci sak'on da ke ciki kenan don na gansu da kayan sojoji"
Maigari zai sake yin magana Liman yayi saurin fad'in,. "ALLAH ya kyauta yanzu ayi abunda yasa aka taraku dai ba wani zakale zakalen magana aka ce ki zo wa mutane ba da su ba"
Ya katse abun ne don gudun kuma wata b'araka ta kunno Kai ganin sababbin bak'in da suka zo kar su fara cin karo da abunda zai saka su fara jin dama basu zo kauyen ba.
Maigarin ya gyara zamanshi yayi gyaran murya yace,. ,"Miye hadinki da Tambari har kika watsa masa k'asa a Ido kikasa yaji ciyo a hannu ya buge goshinshi?"
Dije ta makawa Tambari harara tace,. "WALLAHI Ni ba dashi nike fad'ana ba don Ni har ma muka gama fad'an ban ma ganshi a wurin ba, sai zan bar wajen ne ma na hangoshi yana mukususu"
Liman yakalli Dije da kyau yace,. "Kiji tsoron ALLAH ki fad'i me ya hadaki da shi?"
Dije ta Sosa kanta tace, "Eh to tunda kace tsakanina da ALLAH WALLAHI ba dashi nike fad'a ba shine ya shigarwa Kanwarshi ya zo zai dakeni Ni Kuma na watsa masa k'asa a ido yaje ya buge da icce ya jiwa kanshi ciyo, idan kuma ba'a yarda ba a tambayi su Hansai gasu nan ai"
Maigarin ya kurawa Dije Ido yana karantar yanayinta sannan yace,. "To munji wannan shi kuma Kiran Mahaifiyarshi da kika yi barauniya fa wa ta tab'a yiwa sata a gabanki"
Dije ta zabura tsaye tace,. "Ai WALLAHI ko a gabanta zan fad'a don tasan naganta lokacin da ta yiwa Innarsu Ladiyo sata har ma na fad'awa Innar Ladiyon sai ko gashi da aka binciketa anga kud'in saboda cikin dankwalinta ta b'oyesu, har ma ........."
Sunne Kan da Babansu Tambari yayi yana girgizar kai yasa Maigarin saurin dakatar da ita yace,. "To munji baki abun magana amman kisani ko da wasa kika sake cewa da ita barauniya sai kin karb'i hukunci, don Kinga wad'annan bak'in to su zan baiwa ke su kaiki birni asakaki gidan kaso a rufe ayi ta gana maki azaba, kinga shikenan bazaki sake ganin Innarki da Baffahnki ba, muma mu huta da bari barin da kike sakamu kullum safiya, haka fa kika fasawa yarinyar cen Bintalo goshi suka kawo kararki anan na basu hakuri dakyar suka hak'ura, yanzu haka ma Uwar d'akina tana cen tana fama da k'afa tun lokacin da kika zo muna da zancen Kura, to kiji ki k'ara ji kika yarda kika sake wani laifi a wannan karon ba zaki sha ta dad'i ba"
Dije ta yi fiki fiki da Ido alamun tsoro ya shigeta fuskarta a kumbure tace,. "To ai sune suke tsokalo fad'an ko banso muyi fad'a ba sai sun janyo anyi, suma a ja masu kunne su daina shiga sabgata"
Maigari yayiwa Tambari da Dijen iyaka haka ma su Hansai duka sai da ya ja masu kunne sosai akan kada su koma janyo abunda zai had'asu fad'a da kowa a garin bale ita kanta Dijen.
Haka aka gama aka baiwa Mahaifinsu Tambari hak'uri aka aje akan za'a ga Baffann Dije idan ya dawo shima a sanar dashi ya ja kunnuwan 'yarshi.
Har sun tashi zasu bar wajen Dije ta koma ta zauna tace,. "Nace ciyawar ita Kam har yanzu ba'a Kai ba"
Maigarin ya kawar da kanshi gefe yace,. "Kije Gida idan baki ganta ba ki dawo ki karb'a"
Dije ta mike cikin sanyin jiki tace,. "WALLAHI fa yau ban tafi Daji ba idan akuyata bata ci ciyawar ba hanamu baccin dare zata yi"
Maigarin ya waigo cikin b'acin Rai yace,. "To kunatau! Kije tana cen nace akai maki idan an yo"
Sannan Dije ta washe Baki tace,. "Yawwa Nagode ALLAH yasa kafi haka dussar ma ankai nagode duka amman har da gobe zaka aiko man ko?"
A kufule ya d'aga murya yace,. "Har jibi ma kije Gida shikenan"
Dije ta lak'ama kafad'ar su Ladiyo suka tafi suna ta firarsu suna dariya, har sunyi nisa Dije ta dafe Baki tace dasu
"Wai kun ga abunda na gani kuwa?"
Lanti Jummala da Ladiyo Hansai suka had'a baki wajen fad'in
"Bamu kanun labaran mu sha?"
Dije ta sassafta murya tace,. "Kunga wani fi'ili wai Namiji da shafa janbaki?"
Ladiyo ta kyakyalkyale da dariya tace,. "Ashe ba Ni kad'ai nagani ba?"
Hansai tace,. "Kuka sani ko haka Bakinshi yake?"
Lanti tace,. "Injiwa? Baki ganin yanda yake fari tass! Ai irinsu ance cikin injin ake sakasu ana wankesu, garin wankin nasu ne ma bakinsu yake yin ja irin haka"
Dije ta yi wani mere tace,. "Tirr ALLAH ya rabani da canza halittar da Ubangiji ya bani haka kawai garin wankan injin d'in a wanke da zuciyata ta fashe in mutu"
Hansai tace "Ameen to amman naji ance zasu dinga karantar da mu to me zasu karanta muna?"
Lanti tace,. "Wai Boko mu da ko Makarantar ma ba wani zuwanta ake yi ba za'a yi wahalar d'aukosu a kawosu garin nan"
Dije ta harareta tace,. "Kece dai bakya zuwa nikam duk ranar da nasan malamai zasu zo ai kinsan ina zuwa, ku ne dai ba kwa son karatun Shiyasa duk cikinku babu wadda ta iya abacada"
Hansai zata yi magana Ladiyo ta rufe mata Baki tace,. "Ni dai ku zo muje gida kar aga mun dad'e tunda an kashe rigimar"
Hansai tayi gaba Ladiyo tabi bayanta Suka tafi, Dije ta kalli Lanti da Jummala tace,. "Ni fa kunsan me?"
Suka ce "sai kin fad'a"
Dije ta janyo kansu ta yi masu kus kus d'in cewa,. "So nike muje mu ga wadancen bak'in Yan bokon muji shi wancen Mai wankan injin d'in ko ya iya hausar shi"
Lanti ta zaro Ido tace, "Bakiji kashedin da aka yi muna ba halan? Ni dai WALLAHI ban zuwa babu ruwana kunga tafiyata"
Dije ta kalli Jummala tace,. "Kema jeki abunki amman ku sani WALLAHI sai kunsan Ni kuka yiwa rashin nasiha"
Jummala ta kalli Lanti da ke ta sauri ta bar waen ta dawo da kallonta ga fuskar Dije take ta ciccika tana harararta cikin tsoron hukuncin da zata yi masu tace,. "Ni dai muje in raka kin"
Dije ta washe baki tace,. "Ko ke fa zo muje su Kuma ki barni da su zamu had'u ai"
Jummala cikin tsoro da kashedin da Maigarin yayi masu ta bi Dije Suka zagaya ta bayan gidan Maigarin har suka kai bakin k'ofar d'akin da aka ajiye bak'in cikin sanda Dije itace a gaba ta saka hannu ta yaye labulen kad'an ta leka kanta, aiko ta hango dan farin yana sauya tufafi ya zura dogon wandonshi kenan idonshi suka yi caraf da na Dije, aiko ba shiri ta saki labulen aguje ta falfala da gudunta saboda tsoron ganinshi da tayi daga shi sai guntun wando, saboda a rayuwarta kaf bata tab'a cin karo da wani a hakan ba sai ranar.
Mutumin kam cikin sauri ya saka wandon ya mayar da rigar ya fito d'akin da sauri sai dai ko kurar Dije bai hango ba sai Jummala da ke gudu itama a k'ok'arinta na son ganin ta taradda Dijen da ta samu tasha kwana sai balbala gudu take yi kamar wacce zata tashi sama.
Yayi kwafa ranshi a b'ace ya yi tsaye Yana nazarin mafita sannan ya koma d'akin inda ya taradda abokin tafiyarshi ya dawo da kwanon abincin da Maigarin ya Aiko masu.
Cikin tsananin b'acin Rai ya zauna yana huci cikin harshen turanci yace,. "Bazan iya zama a garin nan ba gaskiya , sai da na fad'awa Mama bazan zo ba ta matsa man in zo to ai gashi nan na fara cin karo da takaicin babbak'un kauyawan"
Abokin tafiyarshi yace ,. "Plss Safwan ka fahimci abunda ake so ka gane mana, yanzu miye aibin garin nan ne? gashi Maigarin da mutaneshi sai ina zasu sakamu suke yi sun karbemu hannu bibbiyu fa"
Wanda aka Kira da safwan d'in ya wani mere baki ya gallawa abokin tafiyar tashi harara ya buga wani uban tsaki yace,. "WALLAHI da naga abunda bazan iya ba Ni fecewata zanyi in barka kaji da su, don bazan zauna takaicinsu ya kar ni ba a banza, yanzun nan fa ina k'ok'arin canza kayana ne na hango idon wata bak'ar mage ta zuro Kai tana kallona"
Abokin tafiyarshi ya kyalkyale da wata arniyar dariya yace,. "Anan din ma ka sake had'uwa da wata magen kenan? To kasani ko ita wannan d'in itace Matar ba magen da ka baro a cen ba"
Safwan saboda tsabar takaici ko kallonshi bai sake yi ba yana kammala saka kayan yayi kwanciyarshi, tare da janyo wayarshi da nufin ya yi kira aiko sai gashi yaga gaba d'aya kaf layukanshi babu d'aya mai network duk sun d'auke.
Ba shiri ya Mik'e zaune cikin harshen turanci yace. "Oh sheet! Wannan wane irin bak'in gari ne haka? gaba d'aya basu da service fa ko d'aya"
🤣🤣🤣🤣wasa farin girki shin su waye su Kuma bak'in Yan bokon????.
Akafta😛
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Jinjinar ban girma gareki masoyiyata ta asali mai Sona da zuciya d'aya Yar kanawa d'iyar mutan Yola Alkharin ALLAH ya Kai maki har gadon baccinki, Ina alfakhari da samunki gareni AISHA YOLA kisani sonki cikin jinina yake ALLAH ya bar mu tare har aljannah gaba dai gaba dai tawajena makiyanki fadawanki😛*
*BAK'ON YANAYI COMPLETE ga Mai b'ukata 300 kacal Mai so ta tuntubeni ta wannan number 09032685442*
*Lamba ta 10*
Dije kam tana gudu tana haki har takai gindin wata bishiya ta fadi zaune k'asa tana sauke nishi a wahalce saboda Uban gudun da ta kwaso, Jummala ta k'araso itama tana haki ta fad'i kusa da ita tana hakin tana fad'in