Sashe 58
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dije ta matso ƙwallar da ta maƙale a idonta tace, "Ni ba ma wannan ba da wane idon zan kalleta idan ta gano abunda ka yi mani?"
Ya sosa kanshi yace
"To ni me ma na yi maki? Salon ki je ki haɗani da ita ko?"
Ta yi saurin kallonshi tace "au kana nufin ka manta abunda ka yi kenan lalle, to ko WALLAHi in baka bini a hankali ba tsaf zan fayyace mata komi"
Ba shiri ya fashe da dariya yace "to na biki a hankalin don ALLAH kar ki fallasani don nasan ƙaramin aikinki ne, idan kuma ke baki san yanda ake rufe sirrin miji ba to ki tona ɗin sai inga da ni da ke waye zai jiyo kunya?"
Wasu hawaye suka zubo mata akan fuska tace, "WALLAHi ALLAH baka kyauta man ba, yanzu shikenan zata gano na iskance"
Ya yi shiru yana saurarenta tana kuka tana soki burutsun zantukkanta, har suka je bakin gate ɗin gidan sannan ta sake fashewa da wani sabon kukan, cike da mamakinta da fargabar da ta cika masa zuciya ya yi parking ya fito suna gaisawa da ma'aikatan gidan, Dije kam kasa motsi ta yi har sai da ta ji yo muryar Fiddo tana yi wa Safwan Oyoyo.
Sannan ta muskuta da ƙyar ta fito tana goge hawayen da suka ɓata mata fuska, ganin yaran wata yayarsu Safwan ɗin sun nufota suna faɗin
"Oyoyo sannu da zuwa" yasa ta washe ta taryesu da murnarta ta ɗauki ƙaramin yaron, ko kallon Fiddo da shi bata yi ba ta fara taku a hankali cikin ƙarfin hali ta shiga cikin gidan, Safwan ya bi bayanta da kallo cikin tausayawa halin da take ciki a zuciyarshi, Fiddo ma shi ta bi da kallo tana faɗin
"Ai WALLAHi yayanmu duk abunda Hajiya ta yi maka ka fanshe akanta, kana ga fa tunda ta bar gidan nan bamu sake ganin fuskar Hajiya ba, kullum zancenta ɗaya ne ALLAH ya dawo da wannan ƴar ƙauyen lafiya, ita bata ko ta jin taka sai ta ɗiyar wasu haka kawai ta zo ta ƙwace muna fada a wurin Hajiya, yawwa ina zancen da ta ji muna yi da kai....? shikenan fa ta hau akan cewa wai ni da kai ne muka haɗa kai muka sa ƴar ƙauyen ta bar gidan, duk rantsuwar da nasha yi mata fa bata yarda da ba hannunmu ba"
Safwan ya bita da kallo mai cike da harara yace, "to wai ke wa ma ya tambayeki wannan uban surutun da kike yi? Yarinya dai gata na dawo da ita to kuma yanzu me yayi saura?"
Fiddo cikin tsoron yanayinshi da taga ya canza a lokaci ɗaya yasa ta sha jinin jikinta ta ce "ka yi haƙuri big bros Bari in shiga ciki kafin ka ƙaraso"
Da sauri ta shige ta barshi yana tunanin ya shiga ko ya bari sai dare ya sulalo ya shige ɗakinshi?, Wata zuciya tace da shi ya shiga kawai ya roƙeta yafiya ya sauke nauyin, ya mazge ya ja ƙafafuwanshi ya shiga gidan cikin fargaba, yana ta rokon ALLAH a zuciyarshi akan kada yasa Hajiya ta ja abun da tsauri.
Sai dai yanayin da yaga ta tarbeshi ne yasashi shan jinin jikinshi amman a hakan ya ƙoƙarta yace,
"Don Allah Hajiyarmu ki yi haƙuri WALLAHi......."
Ta yi saurin ɗaga masa hannu tace, "ajiye ban haƙurinka ni ba shi nake buƙata ba, yarinya dai gata ta dawo hannuna to kaji da kanka kawai don ALLAH"
Safwan zai fara yi mata magiya ta katsa masa tsawa tare da bashi umurnin fita ɗakin, ya miƙe ba shiri ya fice cikin ƙunar zuciya, Hajiyar ta bugawa Fiddo da ke tsaye wata uwar harara itama ta fice sum sum, ta kalli Dije da ke zaune tana sharar ƙwallah ta ce
"Ke kuma jeki ɗaki ki jirani kafin in zo"
Dije ta miƙe a hankali ta fara ɗingisa ƙafa Hajiya ta bi ta da kallo har ta shige, cikin tausayawa ta dawo da kallonta ga Yayarsu Safwan ɗin tace
"Ummi ki kirashi kawai yanzu tunda har mun samu ta dawo lafiya, gobe idan ALLAH ya kaimu tun da sassafe sai ku kama hanya, saboda bana son ma yasan ke ce kika tafi da ita, don nasan halinshi bana don ya dameki akan sai an bashi ita"
Aunty Ummi ta yi shiru sannan tace, "Hajiyarmu naga kamar yanzu yana son Matarshi fa ki yi haƙuri ki yafe mashi don ALLAH Hajiyarmu"
Cikin tsananin ɓacin rai tace "eh nasani Kuma a sanadiyar hakan ma ne nike son nuna masa cewa ko shege yana da ranar shi, saboda haka ki yi abunda nace da ke kawai umurni na baki ba shawararki na nema ba"
Cikin sanyin jiki Ummi ta ɗaga waya ta kira wani mai suna Garba, bayan ya ɗauka tace da shi gobe tun da sassafe ya zo ya ɗaukesu ya yi driving ɗinsu ita da yaranta zuwa Abuja.
SAFWAN kam yana fitowa kiran Ruma yana shigowa wayarshi, ganin mai kiran har yaso kar ya ɗauka ganin ta dameshi da kiran ne yasa ya ɗaga, cikin Muryar kuka Ruma tace
"Don Allah ka zo Zee tana cikin mawuyacin hali kuma ba wanda take kira sai sunanka, plss ka zo WALLAHI tana unconscious we need your help seriously kuma urgent plss and plss"
Wata sabuwa🤦🏻♀️
Akafta😉
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Ku yi haƙuri ku yi haƙuri ni ma ba haka na so ba😢*
*Lamba ta 55*
Cikin wani sabon tashin hankali tare da kiɗimewa ya koma wurin Hajiyar, yana sanar da ita halin da Zee take ciki tare neman izininta akan komawar da yake son yi Gomben, ba tare da wata damuwa ba ta ce da shi ALLAH ya tsare, har ya fito ya dawo yana sosa kai yace
"Khadija fa? Don Allah zan bata saƙo kafin in tafi"
Hajiyar tace da shi tana ciki ya yi saurin shigewa ɗakin zuciyarshi cike da tunanin abubuwa da yawa a ranshi, sai dai yanayin da ya taradda ita ne yasa gwiwowinsa suka yi sanyi, cikin mutuwar jiki ya ja ƙafafuwanshi ya isa wurin da take kwance tana ta cisgar kuka, ya yi saurin duƙawa gaban gadon tare da ƙoƙarin ɗago fuskarta amman ta ƙi ba shi damar hakan, cikin damuwa ya ce
"Haba khadija yanzu kuma me aka yi maki?don ALLAH ki yi haƙuri ki yafe mani abunda na yi maki, Ni ma ba da son raina ba na kasa controlling kaina ne shiyasa, ban san me yasa na sake aikata maki abunda na yi ba duk da nasan zan cutar da ke, plss ki yafe mani don ALLAH, plss ki ɗago fuskarki ki ce dani kin yafe mani don ALLAH"
Dije taƙi ɗago fuskar haka ma ta ƙi daina kukanta, yana cikin magiyar ne kira ya sake shigowa wayarshi, cikin sauri ya fiddo wayar ya duba ganin Daddyn Zee ne da kanshi yasa ya yi saurin ɗagawa, cikin muryar kuka mai haɗe da tashin hankali Daddyn Zee ya ce da shi
"Don Allah ka zo ƴata zata rasa ranta a sanadinka, plss ka bi yo jirgi urgently ake buƙatar ganinka, don ALLAH ka taimaki rayuwar ƴata ka zo"
Ya ce "insha ALLAHu zan zo soon" sannan ya kashe wayar ya miƙe jkinshi yana rawa ya kalli Dije da ke ta kukanta, cikin damuwa ya ce
"Ni zan je Gombe yanzu Khadija ki yi man addu'ar dawo wa lafiya kinji?"
Yana ƙare maganar ya duƙo da kanshi saitin fuskarta ya sakar mata da wani kiss a kumata sannan ya fice da saurinshi, daga nan inda take tana ji yo shi yana yin sallama da su Hajiyar, haka kawai ta ji kamar ta tashi ta bishi ta sanar da shi ta yafe masa, amman wata zuciyar ta gargaɗeta akan kada ta yi hakan saboda kunyar idonsu Hajiya da Aunty Ummin da ke falon, sai dai a zuciyarta ta yi masa fatar ALLAH ya dawo da shi lafiya, saboda bata fahimci ko wanene ya yi kiran nashi ba, ammsn taji rashin son tafiyar har cikin ranta.
Tana kwance ɗakin ne Hajiyar ta shigo ta yi toilet minti biyar a tsakani sai gata ta fito ta ce da ita ta biyota toilet ɗin, cikin fargaba Dije ta miƙe ta tako a hankali saboda zafin da take ji yana ratsata, sai dai ganin fuskar Hajiyar a haɗe ya sa ta yi saurin gyara tafiyar cikin ƙarfin hali, Hajiyar ta maka mata wata uwar harara ta ce
"Ki cire komi naki ki shiga cikin ruwan nan ki buɗa ƙafafuwanki da kyau su ratsa jikinki, ki yi haka har sau uku duk kika tara ruwan kinga wannan maganin ki zuba a cikin sannan ki sake shiga, idan kuma baki yi yanda na ce da ke ba to ni zan zo da kaina in yi maki, tunda ke Kika janyo wa kanki duk abunda ya yi maki, to ai ga shi nan ya barki da jinyar jiki shi ko a jikinshi"
Cikin fushi ta fice toilet ɗin tana ta ƙananan faɗa, Dije ta bi ruwan da ke cike da bahon wankan har turirin ɗimi suke yi, amman saboda gudun ta zo ta yi matan kamar yanda ta faɗa ya sa ta yi saurin cire kayanta ta shige ruwan zafin ta zauna, ruwan suna shiga jikinta tana yarfa hannu tare da cije leɓe har suka dallashe, sannan ta fara jin ƙarfi a jikinta ta yi hakan sau uku kamar yanda Hajiya ta ce sannan ta yi wanka ta fito, sai gata tana takawa da kyau duk wani zafi da take ji ya rage sosai, bayan ta shirya ta ci abinci ne Hajiyar ta zaunar da ita ta ce
Ya sosa kanshi yace
"To ni me ma na yi maki? Salon ki je ki haɗani da ita ko?"
Ta yi saurin kallonshi tace "au kana nufin ka manta abunda ka yi kenan lalle, to ko WALLAHi in baka bini a hankali ba tsaf zan fayyace mata komi"
Ba shiri ya fashe da dariya yace "to na biki a hankalin don ALLAH kar ki fallasani don nasan ƙaramin aikinki ne, idan kuma ke baki san yanda ake rufe sirrin miji ba to ki tona ɗin sai inga da ni da ke waye zai jiyo kunya?"
Wasu hawaye suka zubo mata akan fuska tace, "WALLAHi ALLAH baka kyauta man ba, yanzu shikenan zata gano na iskance"
Ya yi shiru yana saurarenta tana kuka tana soki burutsun zantukkanta, har suka je bakin gate ɗin gidan sannan ta sake fashewa da wani sabon kukan, cike da mamakinta da fargabar da ta cika masa zuciya ya yi parking ya fito suna gaisawa da ma'aikatan gidan, Dije kam kasa motsi ta yi har sai da ta ji yo muryar Fiddo tana yi wa Safwan Oyoyo.
Sannan ta muskuta da ƙyar ta fito tana goge hawayen da suka ɓata mata fuska, ganin yaran wata yayarsu Safwan ɗin sun nufota suna faɗin
"Oyoyo sannu da zuwa" yasa ta washe ta taryesu da murnarta ta ɗauki ƙaramin yaron, ko kallon Fiddo da shi bata yi ba ta fara taku a hankali cikin ƙarfin hali ta shiga cikin gidan, Safwan ya bi bayanta da kallo cikin tausayawa halin da take ciki a zuciyarshi, Fiddo ma shi ta bi da kallo tana faɗin
"Ai WALLAHi yayanmu duk abunda Hajiya ta yi maka ka fanshe akanta, kana ga fa tunda ta bar gidan nan bamu sake ganin fuskar Hajiya ba, kullum zancenta ɗaya ne ALLAH ya dawo da wannan ƴar ƙauyen lafiya, ita bata ko ta jin taka sai ta ɗiyar wasu haka kawai ta zo ta ƙwace muna fada a wurin Hajiya, yawwa ina zancen da ta ji muna yi da kai....? shikenan fa ta hau akan cewa wai ni da kai ne muka haɗa kai muka sa ƴar ƙauyen ta bar gidan, duk rantsuwar da nasha yi mata fa bata yarda da ba hannunmu ba"
Safwan ya bita da kallo mai cike da harara yace, "to wai ke wa ma ya tambayeki wannan uban surutun da kike yi? Yarinya dai gata na dawo da ita to kuma yanzu me yayi saura?"
Fiddo cikin tsoron yanayinshi da taga ya canza a lokaci ɗaya yasa ta sha jinin jikinta ta ce "ka yi haƙuri big bros Bari in shiga ciki kafin ka ƙaraso"
Da sauri ta shige ta barshi yana tunanin ya shiga ko ya bari sai dare ya sulalo ya shige ɗakinshi?, Wata zuciya tace da shi ya shiga kawai ya roƙeta yafiya ya sauke nauyin, ya mazge ya ja ƙafafuwanshi ya shiga gidan cikin fargaba, yana ta rokon ALLAH a zuciyarshi akan kada yasa Hajiya ta ja abun da tsauri.
Sai dai yanayin da yaga ta tarbeshi ne yasashi shan jinin jikinshi amman a hakan ya ƙoƙarta yace,
"Don Allah Hajiyarmu ki yi haƙuri WALLAHi......."
Ta yi saurin ɗaga masa hannu tace, "ajiye ban haƙurinka ni ba shi nake buƙata ba, yarinya dai gata ta dawo hannuna to kaji da kanka kawai don ALLAH"
Safwan zai fara yi mata magiya ta katsa masa tsawa tare da bashi umurnin fita ɗakin, ya miƙe ba shiri ya fice cikin ƙunar zuciya, Hajiyar ta bugawa Fiddo da ke tsaye wata uwar harara itama ta fice sum sum, ta kalli Dije da ke zaune tana sharar ƙwallah ta ce
"Ke kuma jeki ɗaki ki jirani kafin in zo"
Dije ta miƙe a hankali ta fara ɗingisa ƙafa Hajiya ta bi ta da kallo har ta shige, cikin tausayawa ta dawo da kallonta ga Yayarsu Safwan ɗin tace
"Ummi ki kirashi kawai yanzu tunda har mun samu ta dawo lafiya, gobe idan ALLAH ya kaimu tun da sassafe sai ku kama hanya, saboda bana son ma yasan ke ce kika tafi da ita, don nasan halinshi bana don ya dameki akan sai an bashi ita"
Aunty Ummi ta yi shiru sannan tace, "Hajiyarmu naga kamar yanzu yana son Matarshi fa ki yi haƙuri ki yafe mashi don ALLAH Hajiyarmu"
Cikin tsananin ɓacin rai tace "eh nasani Kuma a sanadiyar hakan ma ne nike son nuna masa cewa ko shege yana da ranar shi, saboda haka ki yi abunda nace da ke kawai umurni na baki ba shawararki na nema ba"
Cikin sanyin jiki Ummi ta ɗaga waya ta kira wani mai suna Garba, bayan ya ɗauka tace da shi gobe tun da sassafe ya zo ya ɗaukesu ya yi driving ɗinsu ita da yaranta zuwa Abuja.
SAFWAN kam yana fitowa kiran Ruma yana shigowa wayarshi, ganin mai kiran har yaso kar ya ɗauka ganin ta dameshi da kiran ne yasa ya ɗaga, cikin Muryar kuka Ruma tace
"Don Allah ka zo Zee tana cikin mawuyacin hali kuma ba wanda take kira sai sunanka, plss ka zo WALLAHI tana unconscious we need your help seriously kuma urgent plss and plss"
Wata sabuwa🤦🏻♀️
Akafta😉
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Ku yi haƙuri ku yi haƙuri ni ma ba haka na so ba😢*
*Lamba ta 55*
Cikin wani sabon tashin hankali tare da kiɗimewa ya koma wurin Hajiyar, yana sanar da ita halin da Zee take ciki tare neman izininta akan komawar da yake son yi Gomben, ba tare da wata damuwa ba ta ce da shi ALLAH ya tsare, har ya fito ya dawo yana sosa kai yace
"Khadija fa? Don Allah zan bata saƙo kafin in tafi"
Hajiyar tace da shi tana ciki ya yi saurin shigewa ɗakin zuciyarshi cike da tunanin abubuwa da yawa a ranshi, sai dai yanayin da ya taradda ita ne yasa gwiwowinsa suka yi sanyi, cikin mutuwar jiki ya ja ƙafafuwanshi ya isa wurin da take kwance tana ta cisgar kuka, ya yi saurin duƙawa gaban gadon tare da ƙoƙarin ɗago fuskarta amman ta ƙi ba shi damar hakan, cikin damuwa ya ce
"Haba khadija yanzu kuma me aka yi maki?don ALLAH ki yi haƙuri ki yafe mani abunda na yi maki, Ni ma ba da son raina ba na kasa controlling kaina ne shiyasa, ban san me yasa na sake aikata maki abunda na yi ba duk da nasan zan cutar da ke, plss ki yafe mani don ALLAH, plss ki ɗago fuskarki ki ce dani kin yafe mani don ALLAH"
Dije taƙi ɗago fuskar haka ma ta ƙi daina kukanta, yana cikin magiyar ne kira ya sake shigowa wayarshi, cikin sauri ya fiddo wayar ya duba ganin Daddyn Zee ne da kanshi yasa ya yi saurin ɗagawa, cikin muryar kuka mai haɗe da tashin hankali Daddyn Zee ya ce da shi
"Don Allah ka zo ƴata zata rasa ranta a sanadinka, plss ka bi yo jirgi urgently ake buƙatar ganinka, don ALLAH ka taimaki rayuwar ƴata ka zo"
Ya ce "insha ALLAHu zan zo soon" sannan ya kashe wayar ya miƙe jkinshi yana rawa ya kalli Dije da ke ta kukanta, cikin damuwa ya ce
"Ni zan je Gombe yanzu Khadija ki yi man addu'ar dawo wa lafiya kinji?"
Yana ƙare maganar ya duƙo da kanshi saitin fuskarta ya sakar mata da wani kiss a kumata sannan ya fice da saurinshi, daga nan inda take tana ji yo shi yana yin sallama da su Hajiyar, haka kawai ta ji kamar ta tashi ta bishi ta sanar da shi ta yafe masa, amman wata zuciyar ta gargaɗeta akan kada ta yi hakan saboda kunyar idonsu Hajiya da Aunty Ummin da ke falon, sai dai a zuciyarta ta yi masa fatar ALLAH ya dawo da shi lafiya, saboda bata fahimci ko wanene ya yi kiran nashi ba, ammsn taji rashin son tafiyar har cikin ranta.
Tana kwance ɗakin ne Hajiyar ta shigo ta yi toilet minti biyar a tsakani sai gata ta fito ta ce da ita ta biyota toilet ɗin, cikin fargaba Dije ta miƙe ta tako a hankali saboda zafin da take ji yana ratsata, sai dai ganin fuskar Hajiyar a haɗe ya sa ta yi saurin gyara tafiyar cikin ƙarfin hali, Hajiyar ta maka mata wata uwar harara ta ce
"Ki cire komi naki ki shiga cikin ruwan nan ki buɗa ƙafafuwanki da kyau su ratsa jikinki, ki yi haka har sau uku duk kika tara ruwan kinga wannan maganin ki zuba a cikin sannan ki sake shiga, idan kuma baki yi yanda na ce da ke ba to ni zan zo da kaina in yi maki, tunda ke Kika janyo wa kanki duk abunda ya yi maki, to ai ga shi nan ya barki da jinyar jiki shi ko a jikinshi"
Cikin fushi ta fice toilet ɗin tana ta ƙananan faɗa, Dije ta bi ruwan da ke cike da bahon wankan har turirin ɗimi suke yi, amman saboda gudun ta zo ta yi matan kamar yanda ta faɗa ya sa ta yi saurin cire kayanta ta shige ruwan zafin ta zauna, ruwan suna shiga jikinta tana yarfa hannu tare da cije leɓe har suka dallashe, sannan ta fara jin ƙarfi a jikinta ta yi hakan sau uku kamar yanda Hajiya ta ce sannan ta yi wanka ta fito, sai gata tana takawa da kyau duk wani zafi da take ji ya rage sosai, bayan ta shirya ta ci abinci ne Hajiyar ta zaunar da ita ta ce