Sashe 4
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ko da taje rijiyar makil take da mutane wad'anda wasu da yawa duka tsararta ne, tun daga nesa suna hangota wata ta yafito wata da ke kusa da ita tace
"Ga fa K'arangiya Nan Wai ashe aljanu ne da ita shiyasa ma masifarta kullum take gaba gaba"
Kafin Yar uwar ta bada amsa Dije ta k'araso ta ajiye bokitinta ta rik'e kugu, Kai tsaye ta matsa jikin rijiyar ta ce da wata mai suna Bintalo ta bata guga ta cika bokitinta, Bintalo ta yi mata kallon banza tace
"Kina so ki cika da wuri me ya hana ki zo da taki gugar?"
Dije tace,. "Taki nike ra'ayin dibar ruwan da ita zaki bani ko sai na janyo maki asara?"
Bintalo ta dafe gugarta da k'afa ta rik'e kugu tace,. "Me zaki iya yi ko an Gaya maki Ni ina tsoronki ne kamar kowa? To WALLAHI kika kawon wasa sai na maki danbanzan duka a wurinn...."
Kafin ta Kai k'arshe sai ko taji saukar mari akan fuskarta, Bintalo ta zabura zata rama gugarta ta sub'uce ta fad'a rijiyar, cike da takaici taci kwalar Dije ta shaketa saboda tafi Dije girma nesa, kafin kace me idon DIJE sun yi ja cikin tsananin fushi tace
"Sakeni Bintalo"
Bintalo ta zakalkalo tace,. "Anki a sakeki ba za'a sake kin ba kiyi abunda zaki iya"
Dije tace "nace ki sakeni Bintalo"
Bintalo ta k'ara shaketa cikin masifa tace, "Sai kin fiddo man gugata da kika sa ta fad'a ko ina sakinki, WALLAHI yau sai na ga k'arshen rashin kunyarki ba aljanu ba ko iccen kuka ne akanki sai na ci Ubanki..... "
Karaf! Sai jin k'arar saukar bokitin k'arfe aka yi a goshin Bintalo Dije ta kwad'a mata kasan bokitin, Aiko Bintalo ta fasa k'ara kafin kace me jini ya fara wanke mata fuska.
😳na yi nan🏃🏻♀️🏃🏻♀️wlh Babu ruwana kar ace Ina nan aka yi 🏃🏻♀️🏃🏻♀️
Akafta🤣🙌🏻
D/AUTA ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*COMMENTERS INA MAKU JINJINAR BAN GIRMA🤣👍🏻*
*Lamba ta 5*
Bintalo tana shafo goshinta ta ga jini ta fad'i k'asa tana kururuwa, gaba d'aya mutanen da ke wurin hankali a tashe suka fara salati, a cikin matasan 'yanmatan da ke wurin wata ta zo da gudu ta cire dankwalin Bintalon ta d'aure mata goshin jabau! Bintalo Kam sai ihu take wasu suka rikata zuwa gidansu.
DIJE kam ganin an bar gugunan d'ibar ruwa an nufi wajen Bintalo ana sallallami yasa ta cika bokitinta dam! Ta d'ora akai har ta fara tafiya, hankalin mutanen da ke wajen ya dawo kanta aiko wasu da yawa suka fara jifarta da miyagun kalamai suna aibatata, ita kam ko juyowa bata yi ba ta ci gaba da tafiyarta don ita kanta ganin jinin da ke fita a goshin Bintalon ya tsoratata, sai dai ta mazge kawai don kada a gano taji tsoro ace za'a ci zarafinta a banza.
Ko da ta shigo gidan da sanyin jiki ta juye ruwan ta ajiye bokitin zata shige d'aki, Inna Hasiya ta bita da kallo tace
"Ke lafiyarki na ganki wata sukuku haka? Ko karyar ciyon ne ya tashi don ba kyason komawa debo ruwan?"
Dije ta zumburo Baki tace,. "Ba Bintalo ba ce ta jani muka yi fad'a, kuma WALLAHI sai da nace ta kyaleni ta kyaleni taki to ai gashi nan yanzu ta janyo goshinta ya fashe jini sai tsiyaya yake yi"
INNA ta zaro Ido waje dafe da kirji tace,. "Goshinta ya fashe ko dai kin fasa mata? Na shiga Ukuna Ni Hasiya wai Dije kasheni kike so kiyi ne? kulluma da sabuwar masifar da zaki jajibo muna kisa mutane su yi ta ganin kamar bama tsawatar maki, to bari kiji WALLAHI Wannan karon sai dai in kasheki za'ayi a kasheki amman Ni Kam ba hannuna ba k'afata tunda ke kunnuwan Kashi ne da ke"
Tana k'are maganar cikin k'unar Rai tayi madafi inda taci gaba da tuka tuwon masararta, tana yi tana fad'a Dije ta shige d'aki sum sum tana matsar kwallah.
Aiko minti biyar a tsakani sai ga tashin muryar Iya Mero Uwar Bintalo, tun daga farkon shigowa Gidan take zazzaga ruwan bala'i har ta shigo Gidan rik'e da hannun Bintalo tare da wasu Yan bani na'iya masu zuwa ganin k'wam.
Iya Mero tana shigowa ta fara fad'in,
"Ina Hasiya fito kiga abunda tsinanniyar 'yarki ta yiwa Bintalo, WALLAHI Ni Kam bazan tab'a lamunta da rashin mutuncin da take yiwa mutane ba, don in kowa ya kyaleta Ni bazan kyaleta ba Dole ne sai na ramawa Bintalo itama in fasa mata goshin ta ji inda dad'i"
INNA ta fito daga madafi tana sharce majina saboda hayakin da ya turnuke d'akin madafin yasa idonta sunyi jawur, ta goge fuskarta da gefen zanenta ta k'araso wajen tace
"Don ALLAH Mero kiyi hakuri WALLAHI d'a ne ka haifeshi baka haifi halinshi ba, don da ta Ni Dije take bi to ko hannu aka saka mata a baki bazata ciza ba"
Ta nufo wurin Bintalo ta rik'ota da nufin taga yanayin raunin, aiko Iya Mero ta tureta da k'arfi ta shiga gaban Bintalo tare da cire mayafinta ta sha d'amara a masifance tace
"Ba wani dad'in bakinki da zai yi tasiri a wurina don yau dole ne sai na ramawa Bintalo abunda 'yarki ta yi mata don d'a baifi d'a ba da zaki wani kalallameni da dad'in baki to bazan hak'ura din ba sai na rama mata"
INNA cikin b'acin Rai ta shiga d'aki ta janyo Dije da ke makure Kan gadon bonon Innar suka fito d'akin, Inna janye da ita har sai da ta Kai Dije gaban Iya Meron ta saketa, sannan ta d'auko bokitin karfen ta ajiye gabanta tace,
"Ga ki gata nan Mero don ALLAH ki kasheta kar ki barta da ranta"
Cikin borin kunya Mero ta d'aga hannu ta zabgawa Dije wani Uban mari har sai da ta hantsila, aiko dukawar da Dije zata yi bata taso ba sai da kafafuwan Iya Mero sai gata ko tim! A k'asa tana salati zane ya wancakale gefe, sai fad'in take yi
"Ku ke ganinmu ba mu muke ganinKu ba...."
DIJE sai harararta take tana wani ciccika tana kumbura saboda tsananin b'acin Rai.
Yara kam da ke tsaye suna kallo sai ihu suke yi suna dariyar wallen da Iya Mero ta yi, aiko suka fara fad'in
" Ku zo ku ga Dije ta yasar da Innar Bintalo k'asa"
Bintalo tana ganin abunda Dije ta yiwa Innarta ta yo kan DIJE cikin zafin nama ta fara kai mata duka, Dije ta yi tsalle kamar wata zakanya ta sakarwa Bintalo duka a saman goshin, aiko Bintalon ta fasa wata arniyar k'ara ta durk'ushe tana ihu dafe da goshinta da ya sake fashewa da jini daga kanikancin da aka yi mata a shagon sai da maganin da ke kauyen, Iya Mero ta mik'e cike da jin kunyar abunda Dije ta yi mata gaban yara ta rik'o Bintalo da ke ihun wayyo goshinta tace
"Zo muje wurin Maigari tunda ita Uwarta ta kasa ALLAH wadaran wata haifuwa, WALLAHI Allah ya'isa tsakaninmu da ku Hasiya, kin haifo muna jaraba kin kawo muna cikin gari ta zame muna karfen k'afa"
Aiko ta ja Bintalon tana kuka tana ihu suka fita yaran suka bi su buuu! A baya suna dariya, Inna da ke kitchen tana ta sabgarta suna fita ya fito ta rufe Dije da duka ta ko'ina saboda haushinta da ya rufeta, sai ga Baffah ya shigo cikin tashin hankali saboda labari ya je masa irin aika aikar da Dije ta yiwa Bintalo, Yana kan hanyar zuwa gidansu Iya Meron ne aka ce dashi sunyi gidanshi takakka, shine ya nufo gidan da sauri don tsoron abunda zai je ya dawo don yasan halin Dije sarai ba za'a kwashe da ita ta dad'i ba.
Sai ko gashi ya taradda INNA Hasiya tana dukanta, aiko dakyar ya kwaceta a hannunta saboda zuciyar INNA ta Kai wuya da halin Dijen shiyasa ta yi ta jibgarta kamar ba gobe.
Dije Kam sai ihu take yi tana Kiran sunan Baffa tana fad'in
"Wayyo ALLAH ta karyani ta karya man hannu Baffa"
Baffah ya jata ya zaunar da ita akan tabarmar da Inna ta shinfida masa wadda ta zama ka'ida kullum sai an shimfidata saboda cin abincin dare.
Ya Fara lallashinta yana bata baki da kyar ya ciyo kanta ta daina kukan sai dai kam bata daina sauke ajiyar zuciya ba tana ciccika, don kam ta jibgu iya jibga a hannun INNA.
Har sai da aka kira sallahr Magrib sannan ya daina lallashin da yake yi mata, yace taje ta yi sallah kafin ya dawo ya siyo mata tsiren da take so mai shegen dad'i, Dije ta mik'e tana gunguni ta yi arwallah ko d'akin Innar kin shiga tayi anan waje ta shinfida tabarmarta ta yi sallahr tana kumbure kumburen fuska.
Baffah ya dawo rik'e da bak'ar ledar ya zo har gabanta ya ajiye yace, "gashi kici ko tsoka bance ki baiwa kowa ba, kici ke kad'ai abunki gobe ma zan siyo maki wani in har naga kin saki fuskarki kin daina fushi"
Dije ta karb'i ledar ta ajiye gabanta ciki ciki tayi godiya ta dunk'ule cikin kafafuwanta tana turo Baki, ko da ma aka gama abinci kin ci ta yi don daman wannan halinta ne duk lokacin da take fushi bata cin abinci sai kowa yayi kwana, in taji yunwa ta matsa mata sannan ne take fitowa a sace ta ci ta koma.
To haka abun yake ko yau don kuwa ko Naman da Baffah ya siyo matan bata ci ba har sai da taga kowa yayi bacci, sannan ta canyeshi tas amman bata daina jin yunwa ba don rabonta da abinci tun safe kafin su je daji yin ciyawa, aiko ta fito Sadaf Sadaf ta nufi madafi, ta debo abincin tana ci tana tunanin abunda zata yi ta soshe dukan da Inna ta yi mata, aiko tana gama cin abincin ta sha ruwa ta yi gyatsa sanna fara d'auko tabarya ta bud'e turmin da ke kife ta fara daka iya k'arfinta tana lugude tana tana kad'a turmin tana waka sama sama.
"Ga fa K'arangiya Nan Wai ashe aljanu ne da ita shiyasa ma masifarta kullum take gaba gaba"
Kafin Yar uwar ta bada amsa Dije ta k'araso ta ajiye bokitinta ta rik'e kugu, Kai tsaye ta matsa jikin rijiyar ta ce da wata mai suna Bintalo ta bata guga ta cika bokitinta, Bintalo ta yi mata kallon banza tace
"Kina so ki cika da wuri me ya hana ki zo da taki gugar?"
Dije tace,. "Taki nike ra'ayin dibar ruwan da ita zaki bani ko sai na janyo maki asara?"
Bintalo ta dafe gugarta da k'afa ta rik'e kugu tace,. "Me zaki iya yi ko an Gaya maki Ni ina tsoronki ne kamar kowa? To WALLAHI kika kawon wasa sai na maki danbanzan duka a wurinn...."
Kafin ta Kai k'arshe sai ko taji saukar mari akan fuskarta, Bintalo ta zabura zata rama gugarta ta sub'uce ta fad'a rijiyar, cike da takaici taci kwalar Dije ta shaketa saboda tafi Dije girma nesa, kafin kace me idon DIJE sun yi ja cikin tsananin fushi tace
"Sakeni Bintalo"
Bintalo ta zakalkalo tace,. "Anki a sakeki ba za'a sake kin ba kiyi abunda zaki iya"
Dije tace "nace ki sakeni Bintalo"
Bintalo ta k'ara shaketa cikin masifa tace, "Sai kin fiddo man gugata da kika sa ta fad'a ko ina sakinki, WALLAHI yau sai na ga k'arshen rashin kunyarki ba aljanu ba ko iccen kuka ne akanki sai na ci Ubanki..... "
Karaf! Sai jin k'arar saukar bokitin k'arfe aka yi a goshin Bintalo Dije ta kwad'a mata kasan bokitin, Aiko Bintalo ta fasa k'ara kafin kace me jini ya fara wanke mata fuska.
😳na yi nan🏃🏻♀️🏃🏻♀️wlh Babu ruwana kar ace Ina nan aka yi 🏃🏻♀️🏃🏻♀️
Akafta🤣🙌🏻
D/AUTA ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*COMMENTERS INA MAKU JINJINAR BAN GIRMA🤣👍🏻*
*Lamba ta 5*
Bintalo tana shafo goshinta ta ga jini ta fad'i k'asa tana kururuwa, gaba d'aya mutanen da ke wurin hankali a tashe suka fara salati, a cikin matasan 'yanmatan da ke wurin wata ta zo da gudu ta cire dankwalin Bintalon ta d'aure mata goshin jabau! Bintalo Kam sai ihu take wasu suka rikata zuwa gidansu.
DIJE kam ganin an bar gugunan d'ibar ruwa an nufi wajen Bintalo ana sallallami yasa ta cika bokitinta dam! Ta d'ora akai har ta fara tafiya, hankalin mutanen da ke wajen ya dawo kanta aiko wasu da yawa suka fara jifarta da miyagun kalamai suna aibatata, ita kam ko juyowa bata yi ba ta ci gaba da tafiyarta don ita kanta ganin jinin da ke fita a goshin Bintalon ya tsoratata, sai dai ta mazge kawai don kada a gano taji tsoro ace za'a ci zarafinta a banza.
Ko da ta shigo gidan da sanyin jiki ta juye ruwan ta ajiye bokitin zata shige d'aki, Inna Hasiya ta bita da kallo tace
"Ke lafiyarki na ganki wata sukuku haka? Ko karyar ciyon ne ya tashi don ba kyason komawa debo ruwan?"
Dije ta zumburo Baki tace,. "Ba Bintalo ba ce ta jani muka yi fad'a, kuma WALLAHI sai da nace ta kyaleni ta kyaleni taki to ai gashi nan yanzu ta janyo goshinta ya fashe jini sai tsiyaya yake yi"
INNA ta zaro Ido waje dafe da kirji tace,. "Goshinta ya fashe ko dai kin fasa mata? Na shiga Ukuna Ni Hasiya wai Dije kasheni kike so kiyi ne? kulluma da sabuwar masifar da zaki jajibo muna kisa mutane su yi ta ganin kamar bama tsawatar maki, to bari kiji WALLAHI Wannan karon sai dai in kasheki za'ayi a kasheki amman Ni Kam ba hannuna ba k'afata tunda ke kunnuwan Kashi ne da ke"
Tana k'are maganar cikin k'unar Rai tayi madafi inda taci gaba da tuka tuwon masararta, tana yi tana fad'a Dije ta shige d'aki sum sum tana matsar kwallah.
Aiko minti biyar a tsakani sai ga tashin muryar Iya Mero Uwar Bintalo, tun daga farkon shigowa Gidan take zazzaga ruwan bala'i har ta shigo Gidan rik'e da hannun Bintalo tare da wasu Yan bani na'iya masu zuwa ganin k'wam.
Iya Mero tana shigowa ta fara fad'in,
"Ina Hasiya fito kiga abunda tsinanniyar 'yarki ta yiwa Bintalo, WALLAHI Ni Kam bazan tab'a lamunta da rashin mutuncin da take yiwa mutane ba, don in kowa ya kyaleta Ni bazan kyaleta ba Dole ne sai na ramawa Bintalo itama in fasa mata goshin ta ji inda dad'i"
INNA ta fito daga madafi tana sharce majina saboda hayakin da ya turnuke d'akin madafin yasa idonta sunyi jawur, ta goge fuskarta da gefen zanenta ta k'araso wajen tace
"Don ALLAH Mero kiyi hakuri WALLAHI d'a ne ka haifeshi baka haifi halinshi ba, don da ta Ni Dije take bi to ko hannu aka saka mata a baki bazata ciza ba"
Ta nufo wurin Bintalo ta rik'ota da nufin taga yanayin raunin, aiko Iya Mero ta tureta da k'arfi ta shiga gaban Bintalo tare da cire mayafinta ta sha d'amara a masifance tace
"Ba wani dad'in bakinki da zai yi tasiri a wurina don yau dole ne sai na ramawa Bintalo abunda 'yarki ta yi mata don d'a baifi d'a ba da zaki wani kalallameni da dad'in baki to bazan hak'ura din ba sai na rama mata"
INNA cikin b'acin Rai ta shiga d'aki ta janyo Dije da ke makure Kan gadon bonon Innar suka fito d'akin, Inna janye da ita har sai da ta Kai Dije gaban Iya Meron ta saketa, sannan ta d'auko bokitin karfen ta ajiye gabanta tace,
"Ga ki gata nan Mero don ALLAH ki kasheta kar ki barta da ranta"
Cikin borin kunya Mero ta d'aga hannu ta zabgawa Dije wani Uban mari har sai da ta hantsila, aiko dukawar da Dije zata yi bata taso ba sai da kafafuwan Iya Mero sai gata ko tim! A k'asa tana salati zane ya wancakale gefe, sai fad'in take yi
"Ku ke ganinmu ba mu muke ganinKu ba...."
DIJE sai harararta take tana wani ciccika tana kumbura saboda tsananin b'acin Rai.
Yara kam da ke tsaye suna kallo sai ihu suke yi suna dariyar wallen da Iya Mero ta yi, aiko suka fara fad'in
" Ku zo ku ga Dije ta yasar da Innar Bintalo k'asa"
Bintalo tana ganin abunda Dije ta yiwa Innarta ta yo kan DIJE cikin zafin nama ta fara kai mata duka, Dije ta yi tsalle kamar wata zakanya ta sakarwa Bintalo duka a saman goshin, aiko Bintalon ta fasa wata arniyar k'ara ta durk'ushe tana ihu dafe da goshinta da ya sake fashewa da jini daga kanikancin da aka yi mata a shagon sai da maganin da ke kauyen, Iya Mero ta mik'e cike da jin kunyar abunda Dije ta yi mata gaban yara ta rik'o Bintalo da ke ihun wayyo goshinta tace
"Zo muje wurin Maigari tunda ita Uwarta ta kasa ALLAH wadaran wata haifuwa, WALLAHI Allah ya'isa tsakaninmu da ku Hasiya, kin haifo muna jaraba kin kawo muna cikin gari ta zame muna karfen k'afa"
Aiko ta ja Bintalon tana kuka tana ihu suka fita yaran suka bi su buuu! A baya suna dariya, Inna da ke kitchen tana ta sabgarta suna fita ya fito ta rufe Dije da duka ta ko'ina saboda haushinta da ya rufeta, sai ga Baffah ya shigo cikin tashin hankali saboda labari ya je masa irin aika aikar da Dije ta yiwa Bintalo, Yana kan hanyar zuwa gidansu Iya Meron ne aka ce dashi sunyi gidanshi takakka, shine ya nufo gidan da sauri don tsoron abunda zai je ya dawo don yasan halin Dije sarai ba za'a kwashe da ita ta dad'i ba.
Sai ko gashi ya taradda INNA Hasiya tana dukanta, aiko dakyar ya kwaceta a hannunta saboda zuciyar INNA ta Kai wuya da halin Dijen shiyasa ta yi ta jibgarta kamar ba gobe.
Dije Kam sai ihu take yi tana Kiran sunan Baffa tana fad'in
"Wayyo ALLAH ta karyani ta karya man hannu Baffa"
Baffah ya jata ya zaunar da ita akan tabarmar da Inna ta shinfida masa wadda ta zama ka'ida kullum sai an shimfidata saboda cin abincin dare.
Ya Fara lallashinta yana bata baki da kyar ya ciyo kanta ta daina kukan sai dai kam bata daina sauke ajiyar zuciya ba tana ciccika, don kam ta jibgu iya jibga a hannun INNA.
Har sai da aka kira sallahr Magrib sannan ya daina lallashin da yake yi mata, yace taje ta yi sallah kafin ya dawo ya siyo mata tsiren da take so mai shegen dad'i, Dije ta mik'e tana gunguni ta yi arwallah ko d'akin Innar kin shiga tayi anan waje ta shinfida tabarmarta ta yi sallahr tana kumbure kumburen fuska.
Baffah ya dawo rik'e da bak'ar ledar ya zo har gabanta ya ajiye yace, "gashi kici ko tsoka bance ki baiwa kowa ba, kici ke kad'ai abunki gobe ma zan siyo maki wani in har naga kin saki fuskarki kin daina fushi"
Dije ta karb'i ledar ta ajiye gabanta ciki ciki tayi godiya ta dunk'ule cikin kafafuwanta tana turo Baki, ko da ma aka gama abinci kin ci ta yi don daman wannan halinta ne duk lokacin da take fushi bata cin abinci sai kowa yayi kwana, in taji yunwa ta matsa mata sannan ne take fitowa a sace ta ci ta koma.
To haka abun yake ko yau don kuwa ko Naman da Baffah ya siyo matan bata ci ba har sai da taga kowa yayi bacci, sannan ta canyeshi tas amman bata daina jin yunwa ba don rabonta da abinci tun safe kafin su je daji yin ciyawa, aiko ta fito Sadaf Sadaf ta nufi madafi, ta debo abincin tana ci tana tunanin abunda zata yi ta soshe dukan da Inna ta yi mata, aiko tana gama cin abincin ta sha ruwa ta yi gyatsa sanna fara d'auko tabarya ta bud'e turmin da ke kife ta fara daka iya k'arfinta tana lugude tana tana kad'a turmin tana waka sama sama.