← Book details Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 80 OF 84

Sashe 80

Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Angon ƙarni ma ko da ya zo ya taradda mutane ciccike sai tayashi murna ake yi, sai washe baki yake yi amman idonshi suna cen wajen dubo ta ina zai hango kyautar da ALLAH ya yi masa?, Aiko sai ga shi ya hango babyn hannu wata dattijuwa tana tofeshi da addu'o'i.

Cikin sauri ya nufeta ba kunya ya saka hannu ya karɓe yaron tamkar ya yi ihu saboda daɗin ganin yaron a hannunshi, ba tare da tuna da inda yake ba ya kaiwa yaron kiss a goshi da baki, sannan ya hankalta da mutane bakinshi ya ki rufuwa saboda dariyar kanshi da jin daɗin ganin ɗan shi,sannan ya miƙa yaron yana tambayar Hajiya Mama Dijen ta yi masa nuni da ɗakin da take hutawar, ya nufi ɗakin zuciyarshi fess da farin cikin hangota kwance har a lokacin tana ta baccinta, ya tsaya jikin gadon ya shafo kanta tare da duƙowa ya yi mata kiss sannan ya riƙo hannunta, cikin sauri ta buɗe idonta ta saukesu a kanshi ba shiri ta washe baki da murmushi akan fuskarta ta ce

"Habiby"

Ya riƙe hannunta duka biyu ya ce "sannu da ƙoƙari kin ji? ALLAH ya biyaki da gidan Aljannah, naga yarona Masha ALLAH har ya fiki kyau"

Ta ɓata fuska tare da turo baki ta ce

"Saura ƙiris in fara kishi da shi yasin"

Yana dariya mai cewa cike da zallar ƙaunarta tare da shauƙin sonta da ke ɗibarshi, ya duƙa ya tsotso leɓenta sannan ya ce

"I love You so much my heart desire, ke mahaɗina ce idan ina kusa da ke kina sakani susucewa, don haka kada ki janyo in yi abunda za'a ga na yi rashin kunya"

Dije ta yi masa wani fari da ido ta rausayasu sannan ta ce "ina sonka Habiby"

Cikin zurmawa da salonta ya ce "ina son matata kuma ina son kasancewa da abuta a kullum a koda yaushe kuma a kowane lokaci, amman yanzu sai na yi zaman jira kenan ko? Kwana nawa ne ma ake yi wai?"

Dije ta rufe fuska cike da jin nauyin maganar ta ce "kwana dubu uku ne ake yi ai nasan Habibyna jarumin gaske ne zai iya yin fiye da kwanakin ma "

Ya zaro ido waje baki buɗe ya ce "A wannan karon kam dole ne kowa sai ya gano ragwantakata, cabɗi ki ce in mutu kawai kafin zuwan lokacin"

Dije zata yi magana wata Nurse ta shigo tana dariya musamman ganin yanda suke riƙe da hannun juna gam gam tace

"To luv bird's zaku iya tafiya gida tunda har ta gama hutun, sai ku je cen ku ƙarasa soyayyar"

Dukansu suka kalli juna suna dariya Safwan ya saka hannu aljihu ya fiddo kuɗi bai ma tsaya lissafi ba ya miƙa mata yana faɗin

"To ga goro a tayamu da du'a'in dawwama cikin farantawa juna"

Ta karɓe tana jin daɗi ta fice bayan ta gama zuba masu addu'o'in.

Haka aka tattaro da maijego da jinjirinta da masu zuwa ta ya murna aka nufo gidan Safwan, saboda Hajiya Mama ta ce akai Dijen ɗakinta saboda danginta idan sun zo ta ji daɗin tarbarsu, kuma duk wanda bai san muhallinta ba ya gani, amman ta saka wasu dattijai masu kula da ita waɗanda za su yi mata komi kamar a gabanta, cike da jin daɗi Safwan ya fice bayan ya saukesu ya faɗa shaguna yanata lodo kaya har na hauka, bayan waɗanda suka sissiyo a Abuja sai da ya yiwa Dijenshi set biyu na jakunkuna masu samfurin akwati tsadaddu masu shegen kyau, kowace jaka maƙare da kaya na alfarma sannan ya yi wa boy na shi set guda shi ma tsadaddun kaya, Zee ma da nata set sannann ya yi wa su Hajiya Mama da su fiddo su ma, ya sa aka kwaso masa kayan suka nufi gidan Hajiya Mama ya zubesu gabanta, duk da ta ji daɗi amman ta yi masa faɗan almubazzaranci ba kyau, yana dariya ya ce

"Duk abunda na yi maku Hajiya ai kun fi ƙarfinshi wajena, amman insha ALLAHU zan kiyaye a gaba, don ko wannan don naga khadija ko lefe ban yi mata a lokacin aurenmu ba"

Ta sauke ajiyar zuciya ta ce To ALLAH ya rufa asiri ya ƙara buɗa maka kuma ya baka ikon sauke ɗawainiyar gidanka gaba ɗaya "

Ya ce '"Ameen"

Sannan ta ce idan duhun dare ya shigo ya zo ya kwashi kayanshi ya kaiwa Matanshi, sannan ta yi masa godiyar na su da ya siyo masu tare da saka masa albarka, da addu'ar kariya daga sharrin ko mi ƙankantarshi.

Dije kam tana cen ita jaririnta sun sha wanka sai ƙamshi suke yi, Surayya ta haɗa mata tea mai shegen kauri ta shanye saboda saukowar ruwan nono da wuri, sannan dattijan suka baje wajen da aka keɓe don kawai irin wannan lokacin, anata hidimar dafe dafe da dama mata kunun jegon da Hajiya Mama tasa aka dako tun lokacin da aka yi haifuwar.

Ko da ya dawo gidan ya taradda Zee da su Surayya ɗakin sunata firarsu suna shewar jin daɗi, Dije riƙe da kofin kunun tana sha a hankali saboda zafinshi, ya ƙaraso cikin ɗakin ya kalli Zee da ke goye da yaron ya ce

"Naman boy Daman cen kin iya goyon ne?"

Tana dariya ta juya kanta baya ta kallo yaron ta ce

"Ka ga alama don kuwa ga yarona nan yanata baccinshi don shi ma yasan Uwa ba wasa ba ce"

Gaba ɗaya suka fashe da dariya wajen dariya har Dijen ta ƙware da kunun da ta cika bakinta, sai ga shi da kaiwa wurinta ba shiri yana bubbuga bayanta yana hura mata kai tare da faɗin

"Sannu baby sannu"

Hankalinshi bai kwanta ba har sai da ya ga ta dawo normal sannan ya fara dungure mata kai ya ce ,. "Idan kin san ba zaki natsu ba to ki koma wani gu sai kin shanye kunun ki dawo don bana son wasa da lafiya"

Dije ta yi masa wani kallo cikin marairece fuska sannan ta riƙe kunnenta ta ce

"Am sorry habi....."

Ta kallo Zee ta yi saurin datse cikon maganar, Zee tana dariya ta ce "biby"

Surayya da fiddo suka fashe da dariya saboda yanayin da Zee ta yi maganar tana marairece fuska tana lanƙwashe wuya tare da murguɗa baki, sannan ta kalli su Surry ta ce

"Ku zo mu basu waje tunda a gabanmu ma ba za'a yi muna kawaici ba"

Su Surry Suka fice ɗakin suka barsu sunata kallon Zee cike da dariyar da ta suƙesu, Safwan ya kalli Dijen ya ce

"To Ni yanzu ya zaku yi da ni? Babyna na zo gani na taradda an wani duƙunƙuneshi a baya, ƙarshe ma ga yanzu kin janyo an fice da shi bamu gaisai ba"

Dije ta ɗauki kunun ta kurɓa sannan ta haɗiye ta ce "kun fi kusa ka je ka karɓo tunda baka godewa kulawar da yake samu ba"

Ya kalleta da kyau ya ce "haka ma zaki faɗa?"

Ta sake kurɓa kununta sai da ta cika bakinta sannan matso jikinshi ta janyoshi ta riƙo kanshi ta tallafo ido cikin ido ta goga hancinta da na shi sannan ta nufi bakinshi kamar wani sakarai ya buɗe bakin ta juye masa kunun sannan suka fara zuƙe kunun tare har suka shanye, sai ga shi sun buge da dulmiya cikin wata sabuwar duniya sun manta shaf da cewa ba su kaɗai suke ba har sai da suka ji kukan yaron sannan suka dawo hayyacinsu.

Sai ga fiddo ta zo rungume da shi ta ce tsohuwa ɗaya daga cikin dattijan ta ce ta ba shi nononshi ya tsotsa, Dije ta zaro ido waje ta ce

"To Ni ina nasan yanda zan bashi ??"

Safwan ya karɓi yaron Fiddo ta fice ya sakarwa yaron kiss sannan ya kalleta ya ce

"Oyo bari Abban boy ya koya maki riƙe man shi anan"

Ta karɓa ta rungumeshi ya ɗaga rigarta ta ƙasa ya fito da nonuwan, cike da zallar maitarsu a fili ya shafosu duka ta yi saurin lumshe ido, sannan ya ɗago kan yaron ya saita bakinshi ga ɗaya aiko yaron ya fara tsotsa zumui zumui tsut! tsut! Ta cije baki tana faɗin

"Da zafi Habiby kuma ma WALLAhi ba komi a ciki don ALLAH ka bari har ruwan ya zo a hakan zafi kawai zan sha"

Yana ƙumshe dariyarshi ya cire nonon a bakin yaron ya karɓeshi ya ajiye sannan ya je ya rufo ƙofar ɗakin, ya dawo yana wata dariya ya yi durƙuso a gabanta ya sunkuya ya kai nonon a bakinshi ya fara tsotso cikin mugunta, ta fara tureshi amman hakan bai hanashi tsotse ɗaya tas ya saki ya kama ɗayan ba, sai da ya ɗauki lokaci yana zuƙo nonon sannan ya saki, Dije tana hawaye wahala ta ce

"Shi dai mutum ya kamata yasan ya fara girma, a gaban yaro ko kunya baka ji ba kake wannan halin?"

Yana dariya ya sake ɗauko yaron ya ajiye a gabanta ya saita bakinshi ya saka masa nonon, yaro ya ci gaba da tsotsa har da su sauke ajiyar zuciya, Dije ta bi shi da harara ta ce

"Yasin zaka janyo in horashi tunda akanshi ne ake yi man mugunta"

Yana dariya ya ce "wuta bal bal cin zalin yarona ko a bayana ne ku wa"

Ta murguɗa masa baki tana cije leɓe saboda zafin da take ji yana ratsata, haka yaron kam ya sha iya son ranshi sannan ya koma bacci, Safwan ya karɓeshi ya kwantar da shi ya zauna suna firarsu mai cike da nasu salon son, har sai da suka ji ana ƙwanƙwsa ƙofar ne ya buɗe ya fice su Surry suka shigo suna yi mata tsiya.

Ko da dare ya yi Safwan ya kawo masu kayansu Dukansu sunyi farin ciki ba kaɗan ba, musamman Dije da har sai da ta yi kukan daɗi saboda ganin himilin kaya kuma wai duk nata ita da yaronta, ba shiri ta rungumeshi tana kuka tana yi masa godiya.

Mai jego muma dai kam mun tayaki murna😊

Akafta🤪

D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*

*NA HADIZA D/AUTA*

*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*

*ALHAMDULILLAH!!!!*

*Lamba 71*
Chapter 80 · 0% Book details