Sashe 6
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
INNA ta saka hannu ta dungure mata Kai tace,. "Zaki yi man shiru ko sai na kasheki da mari yanzu?, Ai WALLAHI ba wasu aljanu kece kuma na sake jin kin sake kwata irin wannan rashin mutuncin cikin dare WALLAHI sai jikinki ya gaya maki, ki godewa ALLAH da har aljanun gasken basu kawo maki farmaki ba, don muddin Baki daina kokwayonsu ba WALLAHI wani ya shige jikinki kin boni don ko sai dai ki wayi safiya watarana aga kin mutu, saboda ganinsu za ki yi a gabanki sun fito da siffarsu, kuma kinji ana cewa duk wanda yaga aljanu Ido da Ido da siffarshi ta gaskiya to mutuwa zai yi, amman in har ke kin shirya zuwa Lahira yanzu to kici gaba da koyonsu in kin aza wasa ake"
Dije jikinta ya d'auki rawar tsoro ta makure gefe ta dunkule waje d'aya tana addua, Inna ta maka mata wata hararar ta rab'a gefenta ta yi kwanciyarta hankalinta a kwance don ta gano cewa duk iya shegen Dije ne ba wasu aljanu.
Akafta🤾🏻♂️
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*BAK'ON YANAYI BOOK NE MAI ZAFI HAR KUNA YAKE YI A HANNU SABODA TSABAR TSANANIN ZAK'INSHI BOOK D'IN BAK'ON YANAYI SALONSHI DABAN NE DA KOWANE BOOK DA KA TAB'A KARANTAWA A DUNIYAR LITTAFAI, ZAKU SAMESHI A ARHA DA FARASHIN NERA D'ARI UKU KACAL KUMA ZAKU SAMESHI A COMPLETE DINSHI CIKAKKE MAI B'UKATA TA NEMENI TA WANNAN NUMBER 09032685442 SAYEN NA GARI MAYAR DA KUD'I GIDA SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI👍🏻 DOMIN KUWA BAK'ON YANAYI DAUKE YAKE DA NASHI KALAR SALO KALA KALA KUMA MABANBANTA MASU BURGE MAI KARATU DA SAKASHI SHIGA CIKIN SHAUKI YAYIN KARANTAWA💃🏻*
*Lamba ta 7*
Aiko Dije har safe ko motsin kirki bata sake yi ba saboda ta tsorata da jan kunnen da Inna ta yi mata, don hasali ma har mafalki ta yi wai gasunan sun bayyana da siffarsu sun zo wurinta zasu kasheta, cikin firgici ta falka a zabure tana fad'in
"Don ALLAH kuyi hakuri bazan sake ba na tuba nabi ALLAH da manzonshi, amman in har kunga na sake to ku d'auki mataki"
Inna da ke shigowa d'akin ta d'auro arwallar sallahr Asuba da nufin ta tada ita sai gashi ta taradda ita zaune tsakiyar gado tana sambatu, Inna ta kalleta da kyau tace
"Lafiyarki tun da safe kike yiwa mutane soki burutsun zance?"
Dije ta waiga gefe da gefenta sannan ta fara saukowa gadon tace,. 'ba komi"
INNA ta bita da kallo har ta fice d'akin ta girgiza kai sannan ta shimfida wata sabuwar tabarmar kaba da suke sallah akai ta tada sallahrta.
Dije kam har ta k'are arwallar ta dawo d'akin tunanin mafalkin take yi, jikinta a sanyaye ta yi sallah ta gayar da Inna sannan ta fara bitar karatunta na allo, Inna cikin jin dad'in ganin sauyin Dije ta bita da addu'ar ALLAH yasa abun ya dore a haka, don dai ita jikinta yana bata ko dai da gaske Dijen akwai wasu k'wank'wammai akanta masu sakata jidali da yawan fad'ace fad'ace kullum?, Ta fice zuciyarta cike da jin dad'i ta yi madafi domin ta d'ind'ima masu tuwon da zasu karyawa dashi.
Dije Kam tana k'are bitar karatunta ta jingine allonta ta nufi d'akin Baffah domin ta yi mashi Ina kwana, aiko sai gashi sunyi kicib'is da Usman ta ja baya ya shige d'akin sannan ta bi bayanshi da harara ta shige d'akin itama, Baffah yana kishingide da carbi a hannunshi yana ja yana gyangyadi, jin sallamar Usman yasa ya yi saurin tashi zaune yana amsa masa sallamar fuska a d'aure, ganin Dije a bayanshi yasa ya saki fuskarshi da fara'a tana shirin zama nesa dashi yayi saurin fad'in,. "Matso nan kusa da ni Dijengalata ya jikin naki?"
Dije ta zunburo Baki tace,. "Naji sauk'i sai dai dukan da Yaya Usman yayi mani ashe duk ya farfasa man jikina kallo ka gani Baffah"
Ta k'are maganar tare da zubowar wasu kwallah tana nuna masa tsintsiyar hannunta inda shatin bulalar ya fito rad'am.
Baffah ranshi ya K'ara b'aci cikin d'aure fuska yace da Usman da ke k'ok'arin gayar dashi yace,. "Ajiye gaisuwarka bana so tunda har baka ji kunyar saka bulala ka yiwa Dije irin wannan dukan ba, don tsabar rashin imani Innarku ta daketa da dare ace wai kaima ka bita tsakar dare da dukan kawo wuk'a, to bari kaji muddin ka sake yi mata irin wannan dukan WALLAHI sai na sab'a maka, don nafi son Ni in illataka da hannuna da dai ace Yariman Aljanu ya kawo maka farmaki, don ko Hasiya ALLAH ne ya tsareta da yau bata tashi da idanuwanta ba, duk kuma akan dukan da tayiwa Dijen, Kai ma ka kiyayi kanka da tsokano fushin d'an Gidan mai martaba"
Usman yayi saurin toshe dariyarshi yace,. "WALLAHI Baffah k'arya take yi ba wasu aljanu don da idona na ganta jiya tana rera waka tana dukan rufin madafinmu"
Baffah ya galla masa wata jar harara yace,. "To ka godewa ALLAH da har siffarta ka gani a jiki ba siffarsu ba, to bari kaji Kai kanka zasu iya yin siffarka suje inda suke so bale ta Dijen"
Usman ya yunkura zai tashi yace,. "Ni zan tafi gona Baffah kafin ka shigo" Saboda ganin da yayi idan ya tsaya musu ne zasu ci gaba da yi da shi don gano da Baffah Kam yayi amanna da karyar aljanun Dije.
Baffah ya ce "ba zaka bari ka ci tuwo ba?"
Usman zai yi magana Inna ta shigo da kwanon abincin Baffah ta ajiye, ta kalli Dije dake rakub'e kusa da Baffah'n tace,. "Tashi ki d'auki abincin yayanki ki kai masa dakinshi, kema ki d'auki naki kici ki tafi Makaranta"
Dije ta yunkura ta tashi ranta a bace tana fitowa ta bi hanyar d'akin Usman da kallo ta yi kwafa, saboda d'akin ya nufa ya shige abunshi ko waigota bai yi ba, ta nufi madafin ta bud'a kwanon abincinshi da kullum dashi ake zuba masa abinci ciki, ta bud'a langar ta damko gishiri cike da hannunta ta nutse dashi cikin miyar, ta maida murfin ta rufe ta d'auko tana tafe tana had'e fuska har ta kai dakinshi ta yi sallama ciki ciki ta ajiye kwanon bakin k'ofar shiga d'akin zata wuce, ya yi saurin fad'in
"Ki kawoshi nan a gabana ki ajiye"
Ta fisgi kwanon ta je gabanshi ta ajiye tana wani cin magani har ta zo fita yace,. "Ki kawo man ruwan sha to"
Dije ta fice ko waigoshi bata yi ba sai ko gata da ruwa cike da kofi kamar arzik'i ta ajiye cikin ladabi sannan ta fita da sauri jikinta yana rawa ta nufi wurin Baffah da ke cin tuwonshi har lokacin, ta wani marairecewa tace
"Don Allah Baffah ka rantsewa Yaya Usman akan kada ya sake dukana, don yanzu haka hararata kawai yake yi nasan k'iris yake jira ya kamani yayi ta jibga kamar jaka"
"Baffah yace kyaleshi je kici abincinki ki tafi Makaranta kar kiyi latti yaran da kike karantarwa su yi ta jira"
Dije tuno irin cin zalin d'in da take yiwa yaran makatantar yasa ta kyalkyale da dariya tace,. "Bari in d'auko tuwon nan inci Baffah a gabanka"
Ta nufi madafin da saurinta don tsoron Usman ya cafketa aiko fitowarta ke da wuya taji ya shako wuyanta, Aiko ta fasa k'ara tare da kiran sunan Baffah akan ya kawo mata agaji, sai ko gashi ya fito Usman yana d'aga hannu da nufin ya saukeshi a fuskarta Baffah ya rik'e hannunshi cikin fushi Yace
"Wai kai shikenan ita bazaka barta ta sakata ta wala ba cikin gidan nan? To WALLAHI wannan karon ko kallon banza naga ka sake yi mata sai na rama mata"
Ya fisge hannun Dije daga rikon da Usman yayi mata suka shige dakinshi, Usman ranshi a b'ace ya kalli Inna yace
"Gishiri fa ta saka man a tuwon da kikace ta kai mani, ruwa ma da nace ta debo man duk sai da ta zuba gishirin ciki ina kurbawa ba shiri na furzar saboda bala'in zartsinsu, amman Kinga Baffah laifina ya gani to WALLAHI idan ta cikani sai na karyata cikin Gidan nan"
Baffah ya lek'o kanshi Usman yana gaf da fita yace, "Wanda ya fasa karyata ban gode masa ba, Kai ko ka zuba ido ka ga irin kalar hukuncin da zan dauka kanka"
INNA dai ranta a b'ace tace ,. "Haba Malam ka dubi abun nan fa da idon basira, gishiri fa ta zabga masa a abinci da ruwan sha ina ko Dije taga gaskiya anan?"
Baffah ya yi mata wani kallo yace,. "Anji bata da gaskiyar ku had'u ke da shi ku kasheta"
INNA tace,. "ALLAH ya baka hak'uri ni dai fadar gaskiya ce tawa"
Baffah cikin d'aga murya yace,. "To ba'a so ki rik'e gaskiyarki ku bar Yarinya ta sarara"
Dije dai sai guma lomomin tuwonta take yi tana kammalawa ta wanke hannunta ta ja allonta ta fice, tana tafe tana wakarta har ta kusa kaiwa Makarantar ta hango Hansai da itama tun daga nesa da ta hangota tafe ta k'ara d'aga kafafuwanta da sauri don bata son Dije ta cimmata, aiko Dijen tana hangota ta kwalla mata kira ganin taki tsayawa yasa ta d'aga murya tace,. "WALLAHI in baki tsaya ba na kamaki sai na canza maki kamannu"
Hansai ta tsaya jikinta yana rawa tace,. "Aikena aka yi akace in yi sauri in dawo"
Dije ta k'araso hannunta rik'e da k'ugu tana yiwa Hansai wani kallo tace, "Aikenki aka yi Kuma na ganki da Allo?"
Hansai ta Kai kallonta ga allon cikin rawar Baki tace,. "Allon zan ajiye sai in tafi aiken"
Dije ta dungure mata Kai tace,. "Ke dai kinji haushi WALLAHI bak'ar makaryaciya, na ganoki ai don kinsan kin tonani ne shiyasa kike tsoron mu had'u, amman kinsan kina tsorona Ubanwa yace kije ki sanarwa Maigari Wai k'arya nake yi ba wata Kura?"
Hansai ta zaro Ido tace,. "Ni d'in WALLAHI Ni k'arya ake yi man bani na fad'a ba"
Dije ta ajiye allonta ta rik'e k'ugu tace,. "To wa ya fad'a??"
Hansai hawayen da take makalewa suka zubo tace,. "WALLAHI in har nice na fad'a ALLAH kada ya dagar dani anan wurin"
Dije jikinta ya d'auki rawar tsoro ta makure gefe ta dunkule waje d'aya tana addua, Inna ta maka mata wata hararar ta rab'a gefenta ta yi kwanciyarta hankalinta a kwance don ta gano cewa duk iya shegen Dije ne ba wasu aljanu.
Akafta🤾🏻♂️
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*BAK'ON YANAYI BOOK NE MAI ZAFI HAR KUNA YAKE YI A HANNU SABODA TSABAR TSANANIN ZAK'INSHI BOOK D'IN BAK'ON YANAYI SALONSHI DABAN NE DA KOWANE BOOK DA KA TAB'A KARANTAWA A DUNIYAR LITTAFAI, ZAKU SAMESHI A ARHA DA FARASHIN NERA D'ARI UKU KACAL KUMA ZAKU SAMESHI A COMPLETE DINSHI CIKAKKE MAI B'UKATA TA NEMENI TA WANNAN NUMBER 09032685442 SAYEN NA GARI MAYAR DA KUD'I GIDA SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI👍🏻 DOMIN KUWA BAK'ON YANAYI DAUKE YAKE DA NASHI KALAR SALO KALA KALA KUMA MABANBANTA MASU BURGE MAI KARATU DA SAKASHI SHIGA CIKIN SHAUKI YAYIN KARANTAWA💃🏻*
*Lamba ta 7*
Aiko Dije har safe ko motsin kirki bata sake yi ba saboda ta tsorata da jan kunnen da Inna ta yi mata, don hasali ma har mafalki ta yi wai gasunan sun bayyana da siffarsu sun zo wurinta zasu kasheta, cikin firgici ta falka a zabure tana fad'in
"Don ALLAH kuyi hakuri bazan sake ba na tuba nabi ALLAH da manzonshi, amman in har kunga na sake to ku d'auki mataki"
Inna da ke shigowa d'akin ta d'auro arwallar sallahr Asuba da nufin ta tada ita sai gashi ta taradda ita zaune tsakiyar gado tana sambatu, Inna ta kalleta da kyau tace
"Lafiyarki tun da safe kike yiwa mutane soki burutsun zance?"
Dije ta waiga gefe da gefenta sannan ta fara saukowa gadon tace,. 'ba komi"
INNA ta bita da kallo har ta fice d'akin ta girgiza kai sannan ta shimfida wata sabuwar tabarmar kaba da suke sallah akai ta tada sallahrta.
Dije kam har ta k'are arwallar ta dawo d'akin tunanin mafalkin take yi, jikinta a sanyaye ta yi sallah ta gayar da Inna sannan ta fara bitar karatunta na allo, Inna cikin jin dad'in ganin sauyin Dije ta bita da addu'ar ALLAH yasa abun ya dore a haka, don dai ita jikinta yana bata ko dai da gaske Dijen akwai wasu k'wank'wammai akanta masu sakata jidali da yawan fad'ace fad'ace kullum?, Ta fice zuciyarta cike da jin dad'i ta yi madafi domin ta d'ind'ima masu tuwon da zasu karyawa dashi.
Dije Kam tana k'are bitar karatunta ta jingine allonta ta nufi d'akin Baffah domin ta yi mashi Ina kwana, aiko sai gashi sunyi kicib'is da Usman ta ja baya ya shige d'akin sannan ta bi bayanshi da harara ta shige d'akin itama, Baffah yana kishingide da carbi a hannunshi yana ja yana gyangyadi, jin sallamar Usman yasa ya yi saurin tashi zaune yana amsa masa sallamar fuska a d'aure, ganin Dije a bayanshi yasa ya saki fuskarshi da fara'a tana shirin zama nesa dashi yayi saurin fad'in,. "Matso nan kusa da ni Dijengalata ya jikin naki?"
Dije ta zunburo Baki tace,. "Naji sauk'i sai dai dukan da Yaya Usman yayi mani ashe duk ya farfasa man jikina kallo ka gani Baffah"
Ta k'are maganar tare da zubowar wasu kwallah tana nuna masa tsintsiyar hannunta inda shatin bulalar ya fito rad'am.
Baffah ranshi ya K'ara b'aci cikin d'aure fuska yace da Usman da ke k'ok'arin gayar dashi yace,. "Ajiye gaisuwarka bana so tunda har baka ji kunyar saka bulala ka yiwa Dije irin wannan dukan ba, don tsabar rashin imani Innarku ta daketa da dare ace wai kaima ka bita tsakar dare da dukan kawo wuk'a, to bari kaji muddin ka sake yi mata irin wannan dukan WALLAHI sai na sab'a maka, don nafi son Ni in illataka da hannuna da dai ace Yariman Aljanu ya kawo maka farmaki, don ko Hasiya ALLAH ne ya tsareta da yau bata tashi da idanuwanta ba, duk kuma akan dukan da tayiwa Dijen, Kai ma ka kiyayi kanka da tsokano fushin d'an Gidan mai martaba"
Usman yayi saurin toshe dariyarshi yace,. "WALLAHI Baffah k'arya take yi ba wasu aljanu don da idona na ganta jiya tana rera waka tana dukan rufin madafinmu"
Baffah ya galla masa wata jar harara yace,. "To ka godewa ALLAH da har siffarta ka gani a jiki ba siffarsu ba, to bari kaji Kai kanka zasu iya yin siffarka suje inda suke so bale ta Dijen"
Usman ya yunkura zai tashi yace,. "Ni zan tafi gona Baffah kafin ka shigo" Saboda ganin da yayi idan ya tsaya musu ne zasu ci gaba da yi da shi don gano da Baffah Kam yayi amanna da karyar aljanun Dije.
Baffah ya ce "ba zaka bari ka ci tuwo ba?"
Usman zai yi magana Inna ta shigo da kwanon abincin Baffah ta ajiye, ta kalli Dije dake rakub'e kusa da Baffah'n tace,. "Tashi ki d'auki abincin yayanki ki kai masa dakinshi, kema ki d'auki naki kici ki tafi Makaranta"
Dije ta yunkura ta tashi ranta a bace tana fitowa ta bi hanyar d'akin Usman da kallo ta yi kwafa, saboda d'akin ya nufa ya shige abunshi ko waigota bai yi ba, ta nufi madafin ta bud'a kwanon abincinshi da kullum dashi ake zuba masa abinci ciki, ta bud'a langar ta damko gishiri cike da hannunta ta nutse dashi cikin miyar, ta maida murfin ta rufe ta d'auko tana tafe tana had'e fuska har ta kai dakinshi ta yi sallama ciki ciki ta ajiye kwanon bakin k'ofar shiga d'akin zata wuce, ya yi saurin fad'in
"Ki kawoshi nan a gabana ki ajiye"
Ta fisgi kwanon ta je gabanshi ta ajiye tana wani cin magani har ta zo fita yace,. "Ki kawo man ruwan sha to"
Dije ta fice ko waigoshi bata yi ba sai ko gata da ruwa cike da kofi kamar arzik'i ta ajiye cikin ladabi sannan ta fita da sauri jikinta yana rawa ta nufi wurin Baffah da ke cin tuwonshi har lokacin, ta wani marairecewa tace
"Don Allah Baffah ka rantsewa Yaya Usman akan kada ya sake dukana, don yanzu haka hararata kawai yake yi nasan k'iris yake jira ya kamani yayi ta jibga kamar jaka"
"Baffah yace kyaleshi je kici abincinki ki tafi Makaranta kar kiyi latti yaran da kike karantarwa su yi ta jira"
Dije tuno irin cin zalin d'in da take yiwa yaran makatantar yasa ta kyalkyale da dariya tace,. "Bari in d'auko tuwon nan inci Baffah a gabanka"
Ta nufi madafin da saurinta don tsoron Usman ya cafketa aiko fitowarta ke da wuya taji ya shako wuyanta, Aiko ta fasa k'ara tare da kiran sunan Baffah akan ya kawo mata agaji, sai ko gashi ya fito Usman yana d'aga hannu da nufin ya saukeshi a fuskarta Baffah ya rik'e hannunshi cikin fushi Yace
"Wai kai shikenan ita bazaka barta ta sakata ta wala ba cikin gidan nan? To WALLAHI wannan karon ko kallon banza naga ka sake yi mata sai na rama mata"
Ya fisge hannun Dije daga rikon da Usman yayi mata suka shige dakinshi, Usman ranshi a b'ace ya kalli Inna yace
"Gishiri fa ta saka man a tuwon da kikace ta kai mani, ruwa ma da nace ta debo man duk sai da ta zuba gishirin ciki ina kurbawa ba shiri na furzar saboda bala'in zartsinsu, amman Kinga Baffah laifina ya gani to WALLAHI idan ta cikani sai na karyata cikin Gidan nan"
Baffah ya lek'o kanshi Usman yana gaf da fita yace, "Wanda ya fasa karyata ban gode masa ba, Kai ko ka zuba ido ka ga irin kalar hukuncin da zan dauka kanka"
INNA dai ranta a b'ace tace ,. "Haba Malam ka dubi abun nan fa da idon basira, gishiri fa ta zabga masa a abinci da ruwan sha ina ko Dije taga gaskiya anan?"
Baffah ya yi mata wani kallo yace,. "Anji bata da gaskiyar ku had'u ke da shi ku kasheta"
INNA tace,. "ALLAH ya baka hak'uri ni dai fadar gaskiya ce tawa"
Baffah cikin d'aga murya yace,. "To ba'a so ki rik'e gaskiyarki ku bar Yarinya ta sarara"
Dije dai sai guma lomomin tuwonta take yi tana kammalawa ta wanke hannunta ta ja allonta ta fice, tana tafe tana wakarta har ta kusa kaiwa Makarantar ta hango Hansai da itama tun daga nesa da ta hangota tafe ta k'ara d'aga kafafuwanta da sauri don bata son Dije ta cimmata, aiko Dijen tana hangota ta kwalla mata kira ganin taki tsayawa yasa ta d'aga murya tace,. "WALLAHI in baki tsaya ba na kamaki sai na canza maki kamannu"
Hansai ta tsaya jikinta yana rawa tace,. "Aikena aka yi akace in yi sauri in dawo"
Dije ta k'araso hannunta rik'e da k'ugu tana yiwa Hansai wani kallo tace, "Aikenki aka yi Kuma na ganki da Allo?"
Hansai ta Kai kallonta ga allon cikin rawar Baki tace,. "Allon zan ajiye sai in tafi aiken"
Dije ta dungure mata Kai tace,. "Ke dai kinji haushi WALLAHI bak'ar makaryaciya, na ganoki ai don kinsan kin tonani ne shiyasa kike tsoron mu had'u, amman kinsan kina tsorona Ubanwa yace kije ki sanarwa Maigari Wai k'arya nake yi ba wata Kura?"
Hansai ta zaro Ido tace,. "Ni d'in WALLAHI Ni k'arya ake yi man bani na fad'a ba"
Dije ta ajiye allonta ta rik'e k'ugu tace,. "To wa ya fad'a??"
Hansai hawayen da take makalewa suka zubo tace,. "WALLAHI in har nice na fad'a ALLAH kada ya dagar dani anan wurin"