Sashe 26
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta janyo hannunta tare da yiwa 'yan rakiyar Dije maraba da Baffah'nta da yake ta kallon k'aton gidan yana jinjina girmamshi a ranshi, har suka shiga ciki inda su Baffanta da sauran mutum biyu da suka rakoshi aka kaisu babban sit room d'in Gidan tare da Iyayen Safwan d'in biyu da suke tare.
Dije kam cikin Gidan Hajiya Mama ta ja ta K'annen Safwan biyu suna biye da su suna k'umshe dariya, musamman dai d'aya k'anwar tashi da har dafe ciki take yi saboda waige waigen da Dijen da 'yan rakiyarta suke ta yi, don suna ta kalle kallensu har suka shiga ciki, in da aka yiwa matan biyu masauki a wani d'aki Dije kam kai tsaye ta nufi d'akinta da ita ta zaunar da ita falonta, su Sury da ke biye da su suna shigowa ta korasu suka fita saboda ganin yanda su ke ta faman yi wa Dijen dariya.
Sannan ta kira wata 'yar aikinsu ta kawowa Dijen Abinci da wad'ancen matan sannan ta yi k'uryar d'akinta zuciyarta cike da tunane tunane, Dije kam ba wani jin nauyi ko jin kunya ta saki jiki ta kwashi abincinta tana santi har da su lashe filet d'in tas da halshenta, sannan da ta k'oshi ma ta saka hannunta cikin miyar ta dinga tsamo tsokokin naman tana cinyewa tana fad'in
"Wannan Abinci sai kace a aljannah?? Cabd'i jam, ai Ni kam gaba ta yi da ni wai zak'wai yasin ai Ni kam ba mai fiddani cikin gidan nan"
Surayya da fiddo kam da suke lab'e jikin k'ofar d'akin sunata turereniyar lek'enta, sai uwar dariya suke ci har sai da Hajiya Mama ta fito ta gansu suka yi saurin barin wajen tare da k'umshe dariyar da take son kashesu, saboda ganin duk felek'en Yaya Safwan d'in ace wai wannan Bagidajiyar ce Matarshi.
Hajiya Mama ta yi zaune tana kallon Dijen yanda bakinta ya nashe da maik'o gashi sai faman lashe hannunta take yi tana fad'in,. "Hannuna Kai ma yau ka san ka shigo gidan Yan gayu munci dad'i abunmu ALLAH yasa in mutu a gidan nan Ni kam, dole in koma in zo da Innata da Gambo su ma su sha dad'insu, ta sake d'auko wani k'aton k'ashi tace wohoho ina ma Gambo ta sami wannan k'ashin nasan da hak'oranta da suka zube duka sai sun dawo"
A cen gefen su Baffah kuwa an tarbesu da manyan kulolin abinci na alfarma, sannan aka nuna masu toilet da komi suka fara gabatar da sallolinsu sannan suka ci abinci suka yi k'at! Sannan aka had'u duka akan a tattauna muhimmiyar maganar da ta had'asu dukansu..
Akafta
D/AUTA CE😅
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*BAN LAMUNTA BA AKAN KOWA YA SARRAFA MANI LITTAFAINA BA BA TARE DA IZININA BA AKASIN HAKA KUWA WALLAHIL'AZIM ZAMU GAURAYA DA KOMA WACE DON SAI NA JA HAKKINA AKAN KOMA WA YE A BI DOKA A ZAUNA LAFIYA🤝🏻*
*Kukan Kurciya......😉*
*Lamba ta 27*
Safwan kam ko da ya je sanarwa da Hajiya Mama ya taradda ita zaune falonta ta yi tagumi tana nazarin abunda ya ja Safwan ga Dije har ya zab'eta a matsayin matar aurenshi, saboda saninshi da ta yi ciki da bayanshi akan mugun k'yank'yami tare da wofintar da sha'anin Mata, cikin sanyin jiki ya isa wurinta saboda yanayinta ya nuna k'arara damuwar da take ciki, ya sami d'aya daga cikin kujerun ya zauna sannan yace
"Maaah!"
Ta d'ago kanta da sauri tana murmushin yak'e tace,. "Ya dai? Sun kammala cin abincin ne?"
Ya sosa kanshi ya ce "Eh ina ita yarinyar?"
Hajiya Mama ta yi masa nuni da k'uryar d'akinta tace,. "Tana ciki tana SALLAH"
Sannan ya ce "Ok to ki je su Baba Ali suna so su tafi gida shine aka ce ki zo ku yi sallama"
Hajiya Mama ta mike ta janyo hijabinta ta saka tace,. "Ok to mu je"
Ya sosa kanshi yace,. "Itama ta zo ai zaman har da ita ne"
Hajiya Mama tace,. "Ok to ku sameni a cen d'in"
Ta fice zuciyarta bata daina mamakin Safwan ba, Safwan kam kai tsaye d'akin ya nufa in da ya taradda ita tsaye a gaban standing mirror tana kallon kanta tana wasar Baki, tana yi tana rufe fuskarta cen ta bud'e tana dariya saboda ganin kanta jikin k'aton madubin yasata jinta cikin wani nishad'i.
A hankali ya ja ya tsaya bayanta tare da rungume hannu a K'irji yana kallonta, cikin Madubin Dije ta hangoshi tsaye ta yi saurin waigawa sai ko gashi yana yi mata wani kallon reni yace
"Ke Wai shikenan ba zaki yi hankali ba?"
Dije ta sha jinin jikinta tace,. "Ai kasan cewa Ni ba mahaukaciya ba ce ba ko?"
Ta k'are maganar tare da murgud'a masa Baki, ya tako a hankali ya tsaya gaf da ita tare da rik'e mata kunne ya jawo cikin sigar k'eta Dije ta yage baki tace
"Wayyo! Baffahna"
Safwan ya yi saurin sakinta ya ce " ke fa wata b'aro ce to ki zo muje ana nemanki kuma saura idan kika je don ALLAH ki zuba shirmenki da kika saba, WALLAHI in saki jiki in jibegeki a banza kin ga nan ba k'auyenku bane bale har ki sami damar yi man turaren mayu ko ki saka man b'eraye"
Yana k'are maganar ya nufi k'ofar fita yace,. "Ki zo mu je na ce"
Dije ta sha jinin jikinta sosai saboda tuno abunda ta yi masa sannan ta bishi a baya tana fad'in
"Don Allah Ni dai ai ba wani laifi nayi ba kuma yanzu ko? Don Ni dai WALLAHI ALLAH bana son a ce in bar gidan nan, ashe haka kuke cin dad'inku ku kam? Cab! Gaskiya Wallahi kun zo duniyar a sa'a ashe ku ma kuna cikin mutanen da na ji Malaminmu ya fad'a muna ana baiwa Aljannah tun nan duniya ku canye mu Kuma sai a bamu ta Lahira"
Ya yi banza da ita yana gaba tana biyarshi tana zuba masa surutu har suka kai Babban falon Gidan, in da su Fiddo su ke zaune suna kallo suna labarin shirmen Dije suna dariya, suna hangoshi suka yi muk'us dukansu saboda bala'in tsoronshi da suke ji kamar me, ya wuce abinshi ba tare da ko kallonsu ya yi ba, Dije kam tana k'arasowa tana kalle kallenta ta hango t.v ana wani wrestling, dai dai in da wani k'aton mutum ya d'aga wani sama ya jefoshi k'asa ya bishi ya danne ana kidanyar d'aya biyu uku, Dije ta yi wani tsalle tace
"Tashi ka rama WALLAHI kada ka yarda cabd'i jam haka kawai ka zuba masa Ido ya jibgi banza?"
Sai Kuma gashi Kuma wanda ya danne d'in ya hanashi ci ta hanyar yin wani zillo cikin jin haushin hakan mai son ya ci d'in ya saki kwanji ya yi ta kaiwa na k'asan naushi, Dije ta zabura ta gyara tsayuwar dambe ta sha fili tace
"Ai billahillazi kar ka yarda tashi ka rama nace ko baka jini ba? kutuma lalle Kai yanzu zaune zaka yi yanata jibgarka a banza lalle ma kai wawan banza ne kai cabd'i!"
Surry da Fiddo ko me za su yi ba dariya ba don kuwa daina kallon suka yi suka koma kallonta suna cin uban dariya, Safwan kam jin kamar bata biyarshi yasa ya waiga ganin bai ganta ba ya dawo sai dai tsayin da ya ga ta yi ne shi ma kanshi ya so ya bashi dariya, amman ya mazge ya katsa mata wata uwar tsawa yace
"Ke Uban mi kike yi a wurin ba za ki zo mu tafi ba??"
Dije ta yi saurin waigawa sannan ta b'ata fuska tace, "wani abun takaici na gani yanzu wai wani k'atoton banza ne ya yi kwance anata jibgarshi a wofi WALLAHI ya ji haushi shi kam"
Safwan hararar da ya danna mata ce tasa ta yi muk'us ba shiri ta nufo wajen tare da rab'awa ta gefenshi ta wuce, su Surry kansu tuni suka yi gum! har sai da suka ga ya wuce sannan suka sake fashewa da wata sabuwar dariya saboda abinda Dijen ta yi ba k'aramin dariya ya basu ba.
Bayan sun bar wajen ne Safwan d'in ya fisgota da k'arfi ya had'ata da gini tare da d'aga hannu kamar zai daketa cikin b'acin rai ya nunata da yatsa yace
"WALLAHI kada ki kuskura ki janyo in karairayaki cikin Gidan nan, ke shikenan ba zaki natsu ba sai abu kike yi tamkar wata mahaukaciya to bari kiji na sake ganin kin sake irin wannan shirmen jikinki ne zai gaya maki wawuyar banza,, matsa daga nan kina wani kallona da wasu idanuwanki guru guru tamkar idanuwan mota"
Dije ta zunb'uro baki Kai tsaye ya fisgo hannunta cike da jin haushin kwafsawar da take yi masa suka nufi d'akin, sannan ya saketa da sauri suka shiga tare da sallama a bakunansu.
Dije kam sage da hannu ta shiga ta Sami gefe ta rakub'e tana yarfa hannunta,a zuciyarta tana fad'in
_"Shi Kam wannan mugun mutumen har ciki nawa ya ke so ya yi man ne? "_
Tunaninta ya katse ne saboda jin muryar wani d'aya daga cikin Iyayen Safwan d'in da ta jii yana cewa,. "Matso daga ciki ki zauna kinji 'yata"
Dije ta mik'e ta dawo ciki kad'an ta zauna k'asan carpet kamar yanda taga Safwan d'in ya yi, duk da wata zuciyar ta so ace ta hau Kan kujerar ko don ta ji ya laushinta ya ke, don tunda ta k'yalla Ido ta hangosu tasan ba k'aramin dad'in zama za su yi ba, amman firgicin cikin da Safwan ya sake yi mata yasa ta ji duniyar gaba d'aya ma ta fice mata a Rai.
Baba Ali ya sake cewa
Dije kam cikin Gidan Hajiya Mama ta ja ta K'annen Safwan biyu suna biye da su suna k'umshe dariya, musamman dai d'aya k'anwar tashi da har dafe ciki take yi saboda waige waigen da Dijen da 'yan rakiyarta suke ta yi, don suna ta kalle kallensu har suka shiga ciki, in da aka yiwa matan biyu masauki a wani d'aki Dije kam kai tsaye ta nufi d'akinta da ita ta zaunar da ita falonta, su Sury da ke biye da su suna shigowa ta korasu suka fita saboda ganin yanda su ke ta faman yi wa Dijen dariya.
Sannan ta kira wata 'yar aikinsu ta kawowa Dijen Abinci da wad'ancen matan sannan ta yi k'uryar d'akinta zuciyarta cike da tunane tunane, Dije kam ba wani jin nauyi ko jin kunya ta saki jiki ta kwashi abincinta tana santi har da su lashe filet d'in tas da halshenta, sannan da ta k'oshi ma ta saka hannunta cikin miyar ta dinga tsamo tsokokin naman tana cinyewa tana fad'in
"Wannan Abinci sai kace a aljannah?? Cabd'i jam, ai Ni kam gaba ta yi da ni wai zak'wai yasin ai Ni kam ba mai fiddani cikin gidan nan"
Surayya da fiddo kam da suke lab'e jikin k'ofar d'akin sunata turereniyar lek'enta, sai uwar dariya suke ci har sai da Hajiya Mama ta fito ta gansu suka yi saurin barin wajen tare da k'umshe dariyar da take son kashesu, saboda ganin duk felek'en Yaya Safwan d'in ace wai wannan Bagidajiyar ce Matarshi.
Hajiya Mama ta yi zaune tana kallon Dijen yanda bakinta ya nashe da maik'o gashi sai faman lashe hannunta take yi tana fad'in,. "Hannuna Kai ma yau ka san ka shigo gidan Yan gayu munci dad'i abunmu ALLAH yasa in mutu a gidan nan Ni kam, dole in koma in zo da Innata da Gambo su ma su sha dad'insu, ta sake d'auko wani k'aton k'ashi tace wohoho ina ma Gambo ta sami wannan k'ashin nasan da hak'oranta da suka zube duka sai sun dawo"
A cen gefen su Baffah kuwa an tarbesu da manyan kulolin abinci na alfarma, sannan aka nuna masu toilet da komi suka fara gabatar da sallolinsu sannan suka ci abinci suka yi k'at! Sannan aka had'u duka akan a tattauna muhimmiyar maganar da ta had'asu dukansu..
Akafta
D/AUTA CE😅
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*BAN LAMUNTA BA AKAN KOWA YA SARRAFA MANI LITTAFAINA BA BA TARE DA IZININA BA AKASIN HAKA KUWA WALLAHIL'AZIM ZAMU GAURAYA DA KOMA WACE DON SAI NA JA HAKKINA AKAN KOMA WA YE A BI DOKA A ZAUNA LAFIYA🤝🏻*
*Kukan Kurciya......😉*
*Lamba ta 27*
Safwan kam ko da ya je sanarwa da Hajiya Mama ya taradda ita zaune falonta ta yi tagumi tana nazarin abunda ya ja Safwan ga Dije har ya zab'eta a matsayin matar aurenshi, saboda saninshi da ta yi ciki da bayanshi akan mugun k'yank'yami tare da wofintar da sha'anin Mata, cikin sanyin jiki ya isa wurinta saboda yanayinta ya nuna k'arara damuwar da take ciki, ya sami d'aya daga cikin kujerun ya zauna sannan yace
"Maaah!"
Ta d'ago kanta da sauri tana murmushin yak'e tace,. "Ya dai? Sun kammala cin abincin ne?"
Ya sosa kanshi ya ce "Eh ina ita yarinyar?"
Hajiya Mama ta yi masa nuni da k'uryar d'akinta tace,. "Tana ciki tana SALLAH"
Sannan ya ce "Ok to ki je su Baba Ali suna so su tafi gida shine aka ce ki zo ku yi sallama"
Hajiya Mama ta mike ta janyo hijabinta ta saka tace,. "Ok to mu je"
Ya sosa kanshi yace,. "Itama ta zo ai zaman har da ita ne"
Hajiya Mama tace,. "Ok to ku sameni a cen d'in"
Ta fice zuciyarta bata daina mamakin Safwan ba, Safwan kam kai tsaye d'akin ya nufa in da ya taradda ita tsaye a gaban standing mirror tana kallon kanta tana wasar Baki, tana yi tana rufe fuskarta cen ta bud'e tana dariya saboda ganin kanta jikin k'aton madubin yasata jinta cikin wani nishad'i.
A hankali ya ja ya tsaya bayanta tare da rungume hannu a K'irji yana kallonta, cikin Madubin Dije ta hangoshi tsaye ta yi saurin waigawa sai ko gashi yana yi mata wani kallon reni yace
"Ke Wai shikenan ba zaki yi hankali ba?"
Dije ta sha jinin jikinta tace,. "Ai kasan cewa Ni ba mahaukaciya ba ce ba ko?"
Ta k'are maganar tare da murgud'a masa Baki, ya tako a hankali ya tsaya gaf da ita tare da rik'e mata kunne ya jawo cikin sigar k'eta Dije ta yage baki tace
"Wayyo! Baffahna"
Safwan ya yi saurin sakinta ya ce " ke fa wata b'aro ce to ki zo muje ana nemanki kuma saura idan kika je don ALLAH ki zuba shirmenki da kika saba, WALLAHI in saki jiki in jibegeki a banza kin ga nan ba k'auyenku bane bale har ki sami damar yi man turaren mayu ko ki saka man b'eraye"
Yana k'are maganar ya nufi k'ofar fita yace,. "Ki zo mu je na ce"
Dije ta sha jinin jikinta sosai saboda tuno abunda ta yi masa sannan ta bishi a baya tana fad'in
"Don Allah Ni dai ai ba wani laifi nayi ba kuma yanzu ko? Don Ni dai WALLAHI ALLAH bana son a ce in bar gidan nan, ashe haka kuke cin dad'inku ku kam? Cab! Gaskiya Wallahi kun zo duniyar a sa'a ashe ku ma kuna cikin mutanen da na ji Malaminmu ya fad'a muna ana baiwa Aljannah tun nan duniya ku canye mu Kuma sai a bamu ta Lahira"
Ya yi banza da ita yana gaba tana biyarshi tana zuba masa surutu har suka kai Babban falon Gidan, in da su Fiddo su ke zaune suna kallo suna labarin shirmen Dije suna dariya, suna hangoshi suka yi muk'us dukansu saboda bala'in tsoronshi da suke ji kamar me, ya wuce abinshi ba tare da ko kallonsu ya yi ba, Dije kam tana k'arasowa tana kalle kallenta ta hango t.v ana wani wrestling, dai dai in da wani k'aton mutum ya d'aga wani sama ya jefoshi k'asa ya bishi ya danne ana kidanyar d'aya biyu uku, Dije ta yi wani tsalle tace
"Tashi ka rama WALLAHI kada ka yarda cabd'i jam haka kawai ka zuba masa Ido ya jibgi banza?"
Sai Kuma gashi Kuma wanda ya danne d'in ya hanashi ci ta hanyar yin wani zillo cikin jin haushin hakan mai son ya ci d'in ya saki kwanji ya yi ta kaiwa na k'asan naushi, Dije ta zabura ta gyara tsayuwar dambe ta sha fili tace
"Ai billahillazi kar ka yarda tashi ka rama nace ko baka jini ba? kutuma lalle Kai yanzu zaune zaka yi yanata jibgarka a banza lalle ma kai wawan banza ne kai cabd'i!"
Surry da Fiddo ko me za su yi ba dariya ba don kuwa daina kallon suka yi suka koma kallonta suna cin uban dariya, Safwan kam jin kamar bata biyarshi yasa ya waiga ganin bai ganta ba ya dawo sai dai tsayin da ya ga ta yi ne shi ma kanshi ya so ya bashi dariya, amman ya mazge ya katsa mata wata uwar tsawa yace
"Ke Uban mi kike yi a wurin ba za ki zo mu tafi ba??"
Dije ta yi saurin waigawa sannan ta b'ata fuska tace, "wani abun takaici na gani yanzu wai wani k'atoton banza ne ya yi kwance anata jibgarshi a wofi WALLAHI ya ji haushi shi kam"
Safwan hararar da ya danna mata ce tasa ta yi muk'us ba shiri ta nufo wajen tare da rab'awa ta gefenshi ta wuce, su Surry kansu tuni suka yi gum! har sai da suka ga ya wuce sannan suka sake fashewa da wata sabuwar dariya saboda abinda Dijen ta yi ba k'aramin dariya ya basu ba.
Bayan sun bar wajen ne Safwan d'in ya fisgota da k'arfi ya had'ata da gini tare da d'aga hannu kamar zai daketa cikin b'acin rai ya nunata da yatsa yace
"WALLAHI kada ki kuskura ki janyo in karairayaki cikin Gidan nan, ke shikenan ba zaki natsu ba sai abu kike yi tamkar wata mahaukaciya to bari kiji na sake ganin kin sake irin wannan shirmen jikinki ne zai gaya maki wawuyar banza,, matsa daga nan kina wani kallona da wasu idanuwanki guru guru tamkar idanuwan mota"
Dije ta zunb'uro baki Kai tsaye ya fisgo hannunta cike da jin haushin kwafsawar da take yi masa suka nufi d'akin, sannan ya saketa da sauri suka shiga tare da sallama a bakunansu.
Dije kam sage da hannu ta shiga ta Sami gefe ta rakub'e tana yarfa hannunta,a zuciyarta tana fad'in
_"Shi Kam wannan mugun mutumen har ciki nawa ya ke so ya yi man ne? "_
Tunaninta ya katse ne saboda jin muryar wani d'aya daga cikin Iyayen Safwan d'in da ta jii yana cewa,. "Matso daga ciki ki zauna kinji 'yata"
Dije ta mik'e ta dawo ciki kad'an ta zauna k'asan carpet kamar yanda taga Safwan d'in ya yi, duk da wata zuciyar ta so ace ta hau Kan kujerar ko don ta ji ya laushinta ya ke, don tunda ta k'yalla Ido ta hangosu tasan ba k'aramin dad'in zama za su yi ba, amman firgicin cikin da Safwan ya sake yi mata yasa ta ji duniyar gaba d'aya ma ta fice mata a Rai.
Baba Ali ya sake cewa