Sashe 24
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gambo ta yi mere tace, "yaro man kaza ke dai ki rik'e abunda na yi ta fad'a maki saboda aure yana da dad'i amman Kuma yana da wahala, don haka ba za'a ci ribarshi ba har sai an had'a da hak'uri, kiji ki ki sauraro ki gani ki yi Kamar baki gani ba, ki rufe kunnuwanki ruf ki raba idanuwanki da ganin abunda bai shafeki ba"
Haka Inna Gambo ta dauki lokacin tana ta baiwa Dije shawarwarin da ita sam bata san ma'anarsu ba.
Ko da dare ya yi Maigarin ya zo da kanshi ya yiwa Baffah bayanin abunda ake ciki, ba jayayya ya amince amman yace k'afarshi kafarsu sai yaga inda za'a kai masa Dijenshi.
Inna da Baffah'n kwana suka yi sunata ja mata kunne tare da nasihohin da Suka sakata jin bata son tafiya ta barsu, Baffah ya k'arfafa mata gwiwa akan cewa ai tare za su, sannan hankalinta ya kwanta.
Aiko Asubar farin ta nufi gidan Gambo ta d'auko ajiyarta tare da yi mata sallama, haka ta bi gidan kawayenta duk tana yi masu bankwana kamar ba Amarya ba, alhali cen gidan sai nemanta ake yi akan ta shirya kar su makara a tafiyar tasu kasancewar tafiya ce sosai a gabansu.
Tare da rakiyarsu Hansai da su Jummala da Lanti har da Mune ta dawo gidan zuciyarta cike da tunanin jin wai Bala ya auri Ladiyo kawarta.
Bayan sun shirya ne Safwan da Iyayenshi suka zo sake gaisawa da Baffah, ba k'aramin dad'i Suka ji ba da ganin sauyin da aka samu, don har cikin Gidan Baffah ya yi masu jagora Safwan ya gayar da Inna bayan sun gaisa da Iyayen nashi, sannan suka yi masu alkhairi mai tsoka don har gidan Gambo aka kaisu suka gaisa itama suka yi mata alkhairin.
Inna Kam cikin sanyin jiki ta jinjina maganganun da Inna Gambo tayi, saboda ganin Safwan da Iyayenshi yasa ta gano ba k'aramar baiwace Allah ya yiwa Dijensu ba, mutanen unguwa da abokan arzik'i suka cika k'ofar gidan dank'am ana yi masu sallama, bayan duk wad'anda aka zab'a za'a je da su kowa ya shiga motane amman ba'a ga Dije ta fito gidan ba, ana k'ok'arin a shiga a fito da ita ne sai gata ta fito janye da akuyarta tana fad'in
"Zo muje ke ma ba zan ci amanarki ba don zan zama Likita, don haka dole ne kema in kin fara zawo in yi maki allura"
Cike da mamaki kowa ya saki baki yana kallonta, Safwan kam mere ya yi ya d'auke Kai yana k'umshe dariyarshi, Inna ce ta karb'e akuyar tana cewa da ita ta bari idan ta sake dawowa ta tafi da ita, Dije Kam ta fashe da kuka cikin fushi Usman ya fisgo hannunta ya sakata motar Safwan a seat d'in gaba ya zaunar da ita sannan ya rufe k'ofar.
Haka Suka bar k'ofar gidan sai bye bye ake yi masu tare da yi masu addu'ar ALLAH ya tsare hanya.
Maza bisa Kan Yan birni😝
Akafta🤣
D/AUTA CE🤝🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*GA KIRA DA BABBAR MURYA BAN YARDA BA KUMA BAN AMINCE BA BAN LAMUNTA BA DA A SAKE CANZA KO A SAKE SARRAFA MANI LITTAFAINA BA TA KOWACE SIGA*
*TARTSATSI.*
*RUWA DA. KANKARA.*
*DIJE K'ARANGIYA*
*NI HADIZA D/AUTA BAN LAMUNTA BA AKAN KOWA DA YA SAKE SARRAFA MANI LITTAFAINA BA TA KO WACE HANYA DA KO WANE YANAYI BA TARE DA IZININA BA AKASIN HAKAN KUWA WALLAHIL'AZIM ZAMU GAURAYA DA KOMA WACEE DON SAI NA JA HAKKINA AKAN KOMA WA YE A BI DOKA A ZAUNA LAFIYA🤝🏻*
BAN AMINTA BA!
BAN AMINTA BA!
KAR A SAKE!
KAR A SAKE!
*Lamba ta 25*
DIJE kam duk Wanda ta sani sai ta tashi tsaye ta fito da kanta tana d'agawa mutane hannu, tun Safwan yana jin takaicin abun a ranshi har sai da ya kai ya katsa mata wata arniyar tsawa yace
"Wai ke wace irin bak'auya ce ke? Wannan abu da kike yi tamkar wata zararra fa?"
Dije kam bata daina gaisawa da mutanen k'auyensu ba, cike da jin haushin abin ya ciyo kugunta ya janyo zanenta da k'arfi ta dawo dab'as ta zauna, kanta ya bugu da bayan seat d'in tace
"Wash! ALLAH kaina"
Cikin masifa yace,. ,"Ya dad'e bai cire ba shi kan naki tunda ke ba kya ji WALLAHI ba zan lamunci hakan ba"
Dije ta makure ta sha jinin jikinta tana yi masa hararar gefe tana mui mui, mata biyu yan rakiyar Dijen da suke tare da su cikin motar suka had'a baki wajen fad'in cewa
"Don ALLAH ka yi hak'uri k'urciya ce"
Safwan ya yi banza da su tamkar ma bai ji su ba, ba shiri su ma suka yi gum motar ta yi shiru na d'an lokaci aikuwa cen Dije ta hango wata 'yar Makarantarsu ta Allo ta yi saurin yin wani zillo tamkar biranya ta dale saman seat d'in da kafafunta ta tashi tsaye ta fito da jikinta suka tana fad'in
"Ladidi kin ganni nan cikin mota anyi mani aure birni zan je, me kike so idan zan dawo in kawo maki?"
Ladidin ta washe Baki tace,. "Burodi nike so Dije don ALLAH fa kar ki mance kinji??"
Dije tace, "bazan mance ba Ladidi Sha kuruminki kinji ai kud'i zan yi idan naje, ke karatun Likitancin fa zan yo a cen fa ki ce da Malam Mainasara ya ci gaba da yi man addu'a sai na dawo"
Haka Dije ta yi ta zuba shirmenta da Ladidi har suka daina ganin juna, sannan ta dawo ta zauna tana washe Baki tace
"ALLAH sarki garinmu shikenan zan barka kar ka yi kuka ka ji sai na dawo"
Safwan dai zuciyarshi ta kai wuya ya k'ufula sosai Shiyasa bai biyeta ba don matuk'ar ya kulata ba k'aramar jibga zai yi mata ba, gashi tare yake da Baffah'nta da yan uwanta yasan dole ne sai sunji ba dad'i, shiyasa ya yi kwafa kawai ya yi sannan ya ci gaba da tuk'inshi sannu a hankali har suka shiga babban birnin k'auyen su Dijen, aiko tana hango wani mai shayi da biredi motar tana gudu ta fara yunkurin tsallakewa ta tagar da nufin ta fita, Safwan ya yi nisa da tunani sai gashi ya dawo hankalinshi ba shiri saboda fahimtar abunda take so ta yi, aiko ba shiri ya fisgota ta dawo ciki tare da yin sauri ya zuge glass d'in ya rufe ruf, ta yi saurin kallonshi tace
"Don girman ALLAH ka barni in sha shayi da burodin cen WALLAHI raina ya biya sosai, ka ga yawuna ma har sun tsinke gaba d'aya WALLAHI"
Ta k'are maganar tare da had'iye wasu yawun suka wuce a makoshinta kutt! Safwan ya yi banza da ita, Dije ta tashi ta fara dukan gilas d'in tana fad'in
"Wayyo ALLAH ga wani kifi cen za'a gasa daga ganinshi zai yi dad'i WALLAHI"
Cen kuma ta sake cewa "ji matar cen tana soya kosai gaskiya daga ji zai yi dad'i WALLAHI, har da wani Abu gashi cen ina ma zan samu in ci shi inji?"
Ta k'are maganar cikin marairecewa Safwan ya yi k'ok'arin yin parking a gefen titin ya fito ranshi a b'ace ya nufi wurin mai suyar k'osan, mintuna a tsakani sai gashi ya dawo da ledodi himili guda sai ga motar bayansu ta Iyayen Safwan, wadda Baffahn Dije yake ciki suma sun tsaya suka ce da shi lafiya?, Kai tsaye ya sanar da su cewa Dije ya yiwa siyayyar abun kari tace bata karya ba, cike da jin dad'in hakan Baffahn ya washe Baki ganin himilin ledodin, sannan ya ce da su su tafi abunsu kawai shi zai biyosu daga baya, Baffahn ganin Dijen da Mata biyu yan garinsu yasa bai ji komi ba ya koma motar suka tafi, shi ko ya bud'e murfin gefen Dijen ya zuba mata ledodin a cinya duka ya karb'i wata da wani yaro ya rik'o masa itama duk ya tula mata a jiki sannan ya rufe k'ofar garam! Da k'arfi ya zagaya ya shiga ya tada motar suka bar wajen.
Sai ga Dije da kwallah k'ara tana fad'in wayyo ALLAH zafi kunama tana cizona a cinya WALLAHI"
Ya yi banza da ita cikin sauri ta ture ledodin da ke saman cinyarta sai ga Ledar ruwan zafin shayin da yasa aka k'ullo mata ta fado k'afarta har sun zuba kad'an ta yi saurin d'age k'afar tana fad'in
"Wayyo ALLAH zafi"
Ta saka hannu ta shafo k'afar ganin abu fari yasa ta lasa aikuwa ta yi saurin dukawa ta d'auko ledar tana wash! zafi tana lasar bayan ledar inda shayin ya zubo ya b'ata bayan ledar.
Sannan ta ajiye ledar gefen sitarin motar ta duka ta d'auko wata ledar sai ga kosai yana tiririn zafi, ta yi saurin budewa ta d'auko guda ta kai baki sai gata da yin saurin fad'in
"Wayyo!"
Ta fara hura bakin da hannu tana fad'in,. "Wai wai gaskiya wannan yafi na garinmu dad'i"
Sai da taci sosai sannan ta waigo ta mikowa su Inna Kandala rabi tace
"Ku ci kuma ku ji yafi na garinmu dad'i"
Sai da taci kosan sosai sannan ta bud'a wata ledar sai ga soyayyar doya da kwai ta yi saurin zaro ido tace,. "WALLAHI shine na hango kai honi Dije yau ina ta shan dad'ina WALLAHI cabd'i"
Ta sake rabawa biyu ta mik'awa na baya ta fara cin doyar tana fad'in,. "Shi Kuma wannan abun ko da mi ake had'ashi shi kuma? Kai Yan birni suna jin dad'insu WALLAHi"
Haka ta tasa doyar a gaba ta ci mai isarta sannan ta fara sauke nishi tana fad'in,. "Cikina zai fashe yasin"
Sannan ta ajiye ledar doyar itama ta bud'e wata ledar sai ga waina da miya k'ulle a leda sai kamshin manshanu ke tashi, Dije ta zaro Ido tace
"Kai kai ho! ni Dije ho! Ni Dije gashi na koshi bansan ya zanyi da wainar nan ba?"
Safwan ya yi saurin fad'in,. "Ki zubar kawai a wuce wajen"
Ta k'ara damke ledar tace,. "Cabd'i ai WALLAHI Ni kam sai na cita inji ya take itama, don nasan dole ma ta yi dad'i don ba zata yi kamshin banza ba"
Haka Inna Gambo ta dauki lokacin tana ta baiwa Dije shawarwarin da ita sam bata san ma'anarsu ba.
Ko da dare ya yi Maigarin ya zo da kanshi ya yiwa Baffah bayanin abunda ake ciki, ba jayayya ya amince amman yace k'afarshi kafarsu sai yaga inda za'a kai masa Dijenshi.
Inna da Baffah'n kwana suka yi sunata ja mata kunne tare da nasihohin da Suka sakata jin bata son tafiya ta barsu, Baffah ya k'arfafa mata gwiwa akan cewa ai tare za su, sannan hankalinta ya kwanta.
Aiko Asubar farin ta nufi gidan Gambo ta d'auko ajiyarta tare da yi mata sallama, haka ta bi gidan kawayenta duk tana yi masu bankwana kamar ba Amarya ba, alhali cen gidan sai nemanta ake yi akan ta shirya kar su makara a tafiyar tasu kasancewar tafiya ce sosai a gabansu.
Tare da rakiyarsu Hansai da su Jummala da Lanti har da Mune ta dawo gidan zuciyarta cike da tunanin jin wai Bala ya auri Ladiyo kawarta.
Bayan sun shirya ne Safwan da Iyayenshi suka zo sake gaisawa da Baffah, ba k'aramin dad'i Suka ji ba da ganin sauyin da aka samu, don har cikin Gidan Baffah ya yi masu jagora Safwan ya gayar da Inna bayan sun gaisa da Iyayen nashi, sannan suka yi masu alkhairi mai tsoka don har gidan Gambo aka kaisu suka gaisa itama suka yi mata alkhairin.
Inna Kam cikin sanyin jiki ta jinjina maganganun da Inna Gambo tayi, saboda ganin Safwan da Iyayenshi yasa ta gano ba k'aramar baiwace Allah ya yiwa Dijensu ba, mutanen unguwa da abokan arzik'i suka cika k'ofar gidan dank'am ana yi masu sallama, bayan duk wad'anda aka zab'a za'a je da su kowa ya shiga motane amman ba'a ga Dije ta fito gidan ba, ana k'ok'arin a shiga a fito da ita ne sai gata ta fito janye da akuyarta tana fad'in
"Zo muje ke ma ba zan ci amanarki ba don zan zama Likita, don haka dole ne kema in kin fara zawo in yi maki allura"
Cike da mamaki kowa ya saki baki yana kallonta, Safwan kam mere ya yi ya d'auke Kai yana k'umshe dariyarshi, Inna ce ta karb'e akuyar tana cewa da ita ta bari idan ta sake dawowa ta tafi da ita, Dije Kam ta fashe da kuka cikin fushi Usman ya fisgo hannunta ya sakata motar Safwan a seat d'in gaba ya zaunar da ita sannan ya rufe k'ofar.
Haka Suka bar k'ofar gidan sai bye bye ake yi masu tare da yi masu addu'ar ALLAH ya tsare hanya.
Maza bisa Kan Yan birni😝
Akafta🤣
D/AUTA CE🤝🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*GA KIRA DA BABBAR MURYA BAN YARDA BA KUMA BAN AMINCE BA BAN LAMUNTA BA DA A SAKE CANZA KO A SAKE SARRAFA MANI LITTAFAINA BA TA KOWACE SIGA*
*TARTSATSI.*
*RUWA DA. KANKARA.*
*DIJE K'ARANGIYA*
*NI HADIZA D/AUTA BAN LAMUNTA BA AKAN KOWA DA YA SAKE SARRAFA MANI LITTAFAINA BA TA KO WACE HANYA DA KO WANE YANAYI BA TARE DA IZININA BA AKASIN HAKAN KUWA WALLAHIL'AZIM ZAMU GAURAYA DA KOMA WACEE DON SAI NA JA HAKKINA AKAN KOMA WA YE A BI DOKA A ZAUNA LAFIYA🤝🏻*
BAN AMINTA BA!
BAN AMINTA BA!
KAR A SAKE!
KAR A SAKE!
*Lamba ta 25*
DIJE kam duk Wanda ta sani sai ta tashi tsaye ta fito da kanta tana d'agawa mutane hannu, tun Safwan yana jin takaicin abun a ranshi har sai da ya kai ya katsa mata wata arniyar tsawa yace
"Wai ke wace irin bak'auya ce ke? Wannan abu da kike yi tamkar wata zararra fa?"
Dije kam bata daina gaisawa da mutanen k'auyensu ba, cike da jin haushin abin ya ciyo kugunta ya janyo zanenta da k'arfi ta dawo dab'as ta zauna, kanta ya bugu da bayan seat d'in tace
"Wash! ALLAH kaina"
Cikin masifa yace,. ,"Ya dad'e bai cire ba shi kan naki tunda ke ba kya ji WALLAHI ba zan lamunci hakan ba"
Dije ta makure ta sha jinin jikinta tana yi masa hararar gefe tana mui mui, mata biyu yan rakiyar Dijen da suke tare da su cikin motar suka had'a baki wajen fad'in cewa
"Don ALLAH ka yi hak'uri k'urciya ce"
Safwan ya yi banza da su tamkar ma bai ji su ba, ba shiri su ma suka yi gum motar ta yi shiru na d'an lokaci aikuwa cen Dije ta hango wata 'yar Makarantarsu ta Allo ta yi saurin yin wani zillo tamkar biranya ta dale saman seat d'in da kafafunta ta tashi tsaye ta fito da jikinta suka tana fad'in
"Ladidi kin ganni nan cikin mota anyi mani aure birni zan je, me kike so idan zan dawo in kawo maki?"
Ladidin ta washe Baki tace,. "Burodi nike so Dije don ALLAH fa kar ki mance kinji??"
Dije tace, "bazan mance ba Ladidi Sha kuruminki kinji ai kud'i zan yi idan naje, ke karatun Likitancin fa zan yo a cen fa ki ce da Malam Mainasara ya ci gaba da yi man addu'a sai na dawo"
Haka Dije ta yi ta zuba shirmenta da Ladidi har suka daina ganin juna, sannan ta dawo ta zauna tana washe Baki tace
"ALLAH sarki garinmu shikenan zan barka kar ka yi kuka ka ji sai na dawo"
Safwan dai zuciyarshi ta kai wuya ya k'ufula sosai Shiyasa bai biyeta ba don matuk'ar ya kulata ba k'aramar jibga zai yi mata ba, gashi tare yake da Baffah'nta da yan uwanta yasan dole ne sai sunji ba dad'i, shiyasa ya yi kwafa kawai ya yi sannan ya ci gaba da tuk'inshi sannu a hankali har suka shiga babban birnin k'auyen su Dijen, aiko tana hango wani mai shayi da biredi motar tana gudu ta fara yunkurin tsallakewa ta tagar da nufin ta fita, Safwan ya yi nisa da tunani sai gashi ya dawo hankalinshi ba shiri saboda fahimtar abunda take so ta yi, aiko ba shiri ya fisgota ta dawo ciki tare da yin sauri ya zuge glass d'in ya rufe ruf, ta yi saurin kallonshi tace
"Don girman ALLAH ka barni in sha shayi da burodin cen WALLAHI raina ya biya sosai, ka ga yawuna ma har sun tsinke gaba d'aya WALLAHI"
Ta k'are maganar tare da had'iye wasu yawun suka wuce a makoshinta kutt! Safwan ya yi banza da ita, Dije ta tashi ta fara dukan gilas d'in tana fad'in
"Wayyo ALLAH ga wani kifi cen za'a gasa daga ganinshi zai yi dad'i WALLAHI"
Cen kuma ta sake cewa "ji matar cen tana soya kosai gaskiya daga ji zai yi dad'i WALLAHI, har da wani Abu gashi cen ina ma zan samu in ci shi inji?"
Ta k'are maganar cikin marairecewa Safwan ya yi k'ok'arin yin parking a gefen titin ya fito ranshi a b'ace ya nufi wurin mai suyar k'osan, mintuna a tsakani sai gashi ya dawo da ledodi himili guda sai ga motar bayansu ta Iyayen Safwan, wadda Baffahn Dije yake ciki suma sun tsaya suka ce da shi lafiya?, Kai tsaye ya sanar da su cewa Dije ya yiwa siyayyar abun kari tace bata karya ba, cike da jin dad'in hakan Baffahn ya washe Baki ganin himilin ledodin, sannan ya ce da su su tafi abunsu kawai shi zai biyosu daga baya, Baffahn ganin Dijen da Mata biyu yan garinsu yasa bai ji komi ba ya koma motar suka tafi, shi ko ya bud'e murfin gefen Dijen ya zuba mata ledodin a cinya duka ya karb'i wata da wani yaro ya rik'o masa itama duk ya tula mata a jiki sannan ya rufe k'ofar garam! Da k'arfi ya zagaya ya shiga ya tada motar suka bar wajen.
Sai ga Dije da kwallah k'ara tana fad'in wayyo ALLAH zafi kunama tana cizona a cinya WALLAHI"
Ya yi banza da ita cikin sauri ta ture ledodin da ke saman cinyarta sai ga Ledar ruwan zafin shayin da yasa aka k'ullo mata ta fado k'afarta har sun zuba kad'an ta yi saurin d'age k'afar tana fad'in
"Wayyo ALLAH zafi"
Ta saka hannu ta shafo k'afar ganin abu fari yasa ta lasa aikuwa ta yi saurin dukawa ta d'auko ledar tana wash! zafi tana lasar bayan ledar inda shayin ya zubo ya b'ata bayan ledar.
Sannan ta ajiye ledar gefen sitarin motar ta duka ta d'auko wata ledar sai ga kosai yana tiririn zafi, ta yi saurin budewa ta d'auko guda ta kai baki sai gata da yin saurin fad'in
"Wayyo!"
Ta fara hura bakin da hannu tana fad'in,. "Wai wai gaskiya wannan yafi na garinmu dad'i"
Sai da taci sosai sannan ta waigo ta mikowa su Inna Kandala rabi tace
"Ku ci kuma ku ji yafi na garinmu dad'i"
Sai da taci kosan sosai sannan ta bud'a wata ledar sai ga soyayyar doya da kwai ta yi saurin zaro ido tace,. "WALLAHI shine na hango kai honi Dije yau ina ta shan dad'ina WALLAHI cabd'i"
Ta sake rabawa biyu ta mik'awa na baya ta fara cin doyar tana fad'in,. "Shi Kuma wannan abun ko da mi ake had'ashi shi kuma? Kai Yan birni suna jin dad'insu WALLAHi"
Haka ta tasa doyar a gaba ta ci mai isarta sannan ta fara sauke nishi tana fad'in,. "Cikina zai fashe yasin"
Sannan ta ajiye ledar doyar itama ta bud'e wata ledar sai ga waina da miya k'ulle a leda sai kamshin manshanu ke tashi, Dije ta zaro Ido tace
"Kai kai ho! ni Dije ho! Ni Dije gashi na koshi bansan ya zanyi da wainar nan ba?"
Safwan ya yi saurin fad'in,. "Ki zubar kawai a wuce wajen"
Ta k'ara damke ledar tace,. "Cabd'i ai WALLAHI Ni kam sai na cita inji ya take itama, don nasan dole ma ta yi dad'i don ba zata yi kamshin banza ba"