Sashe 21
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dije kam ranar kwana ta yi tana sharbar hawayenta saboda sam sam ita bata son auren kacakam ballantana auren Balan, idan son damunta ne ace ta yi karatu mai zurfi ta zamo abar alfakhari cikin kauyensu, amman ina kash tasan gurint sam bazai tab'a cika ba muddin ta auri Bala, don dama ace Lawi ne da zata sakawa ranta cewa gurinta zai cika komi daren dad'ewa.
Ko da Safiya ta waye da d'ar d'ar ta shirya don ta zaci Baffah'n ya hanata zuwa Makaranta, amman sai gashi bai hanata ba har da yi mata ALLAH ya kiyaye, saboda yasan Shirin da yake yi akan auradda ita d'in cikin kankanin lokaci.
Dije sukuku ta zo Makarantar Lawi ya so ya yi mata magana amman tuno irin gargadin da Maigarin ya yi masa akanta yasa ya yi k'ok'arin kawar da kanshi gareta, don ko da aka tashi ma sai da kowa ya watse Makarantar sannan shi ya nufo masaukinsu, don gaba d'aya ma shi zaman garin ya gundureshi jin yake yi kamar a saman kaya yake, Alla Alla yake yi su kammala service dinsu su bar Garin, don akan hakan ma har abokin nashi ma sun fara zaman doya da manja dashi, gashi shi ma Maigarin yace ya zame hannunshi idan shi zai iya ga fili ga mai doki.
**
Cikin wata d'aya aka kammala neman auren Bala da Dije inda aka kawo komi na auren Rana kawai ake jira ta zo a sha shagali, izuwa lokacin Dije ta saduda dolenta saboda ba tirjiyar da bata yi ba akan auren amman Baffah'n kam ya kafe ba gudu ba ja da baya, don ita kanta Innar ganin akan auren Dije zasu samu matsala da Baffah'n shiyasa ta zubar da makamanta ta fara shirye shiryen auren Dijenta.
Ana saura sati d'aya bikin Dije suka zana jarabawar kammala primary, kowa sai murna yake yi inda shi Kuma Lawi yake cike da bak'in cikin rasa Dijen da yayi, Safwan kam ko kad'an bazaka gano yanayin da yake ciki ba, asali ma shi hankalinshi kwance yake ta d'aukar photuna da su Dije da sauran yaran Makarantar, Dijen ma ba wata walwala akan fuskarta don kuwa a kallo d'aya zaka gano sauyawar da ta yi, don kuwa gaba d'aya ra zabge sai Ido da karan hanci don izuwa lokacin har wata natsuwar dole ta ziyartota, duk nacin da Lawi ya yi akan yana so ya yi sallama da Dije bai sami wannan damar ba, saboda ganin yanda Safwan ya keta hidimar d'aukar pic's d'inshi da su Dijen.
Sai da aka gama ne ya samu ya yi wa Dije sallama tare da mika mata wata envelope idonshi jawur tamkar ya yi kuka, don shi ya kuduri aniyar ba zai jira ayi auren Dijen da shi ba, da nufin tun da sassafe ya had'a inashi inashi ya bar garin, don shi Safwan ya ce ba ranar zai tafi ba ya yi gaba shi zai biyoshi ta baya.
Dije tana kuka suka yi sallama da Lawi ta tura envelope d'in da ya bata a jaka ta nufi gida,. Kai tsaye ta shige toilet ta bud'a envelope d'in saboda ta matsu taga me ke ciki gashi bata son Inna ta gani.
Aiko sai gashi tana budawa taga wasu Yan hannu da zobe masu bala'in kyau sannan da bandur d'in kud'i sababbi kal yan d'ari bibbiyu, Dije ta zaro ido tare da goge hawayenta cikin sauri ta rungume kud'in da sauran kayan ta fashe da kuka gwanin ban tausayi, sai dai ita bata san duk abunda take yi Inna tana hankalce da ita, shiyasa lokacin da taga ta dad'e bayin ta biyo sawunta sai ko gashi ta ganta durk'ushe kasan bayin tana ta kuka, cikin tausayawa ta isa wurinta ta tadata Dije ta yi saurin yunkurin b'oye kud'in sai ga takardar kud'in ta yage kud'in sun zubo shaaaa! A k'asa.
Ku yi hakuri da kuskuren da kuka gani yau ban yi editing ba🤦🏻♀️
Akafta😉
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*MUTANEN DIJE K'ARANGIYA INA GAIDA KOWA ALL ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MAKU HAR GADON BACCINKU👍🏻*
*Lamba ta 22*
Daga Inna har Dijen gaba d'aya zaro Ido suka yi suna kallon kud'in, cikin firgici inna ta yi saurin fad'in
"Dije me nake Shirin gani yau Ni Hasiya?"
Dije ta yi saurin duk'atawa tana ta tattara kud'in har ta kammala sannan ta mik'awa Inna tace,. "Karb'i kyauta ce aka bani"
Inna ta tak'i karb'ar kud'in ta tsuke fuska tace,. "Gaya man duk fad'in garin nan waye mai arzik'in da har zai iya baki wad'annan mak'udan kud'in sababbi k'al da su haka?"
Dije ta saka hannu ta share hawayen da har lokacin basu daina zubo mata ba tace,. "Malaminmu D'anbirni ne ya bani wai tashi gudunmuwa ce yace ko Daddawa a siya man"
Inna ta maka mata wata jar harara tace,. "To WALLAHI Ni ba ruwana in har Baffah'nki ya ji wannan magana,sawunki a likkafa ki tattara kayanshi da kud'inshi ki je ki Kai masa salun alun ba wanda ya ji ba wanda ya gani"
Dije ta sake fashewa da wani sabon kuka tace,. "Ni dai Inna ina son awarwaron da zoben, don ALLAH ki bari in mayar masa da kud'in kawai don ALLAH Inna"
Ta k'are maganar cikin marairecewa gwanin ban tausayi, Inna ta karbe kud'in da awarwaron da zoben ta janyo hannunta suka fito tana janye da hannun Dijen har d'akinta, sannan ta samo wata leda baka ta zuba kud'in da kayan ta k'ulle jabau! Ta mika mata tare da had'e fuska alamun ba wasa tace,. "Karb'i kije ki mayar masa da kayanshi yanzun ba sai anjima ba"
Dije ta karb'a har ta fito ta dawo tace,. "To Inna ki bari in cire kayan Makarantar in saka na Gida"
Inna ta taso mata kamar zata daketa tace,. "Bazan bari ba nace ba za'a bari ba zaki je ko sai na sab'a maki ne yanzu Nan??"
Dije ta fice tana tafe tana gunguni har ta kai wani lungu ta bud'e ledar ta cire awarwaron da zoben ta k'ulle ledar ta nufi gidan Inna Gambo, sai da ta samu wani waje cikin dabara ta b'oyesu d'akin Gambon sannan ta fito ta nufi gidan Maigarin, sai dai rashin sa'ar da ta taka tun kafin ta isa daga nesa Maigarin da ya hangota ya bada umurnin a hanata zuwa wurinshi, saboda yaci alwashin daga Dijen har Baffah'n ba zai sake shiga cikin shirginsu ba, sai dai ita kam ta nace akan ita bazata koma ba don wurin Malaminsu ta zo ba wurinshi ba, Maigari kam ganin rigima zata b'alle ne a tsakanin Dijen da wani yaronshi yasa yace a kyaleta, kai tsaye ta nufi k'ofar d'akinsu Safwan ta fara rafka sallama sai dai ta yi har ta gaji ko sau d'aya bata ji an amsa mata ba, cike da k'unar rai ta fad'a d'akin da k'arfinta sai dai wayam ba kowa d'akin, tana k'ok'arin fitowa ne ta ji ta yi karo da mutum da sauri ta ja baya tana sosa goshinta da kan Safwan ya buge, Cikin tsoro ta rab'a ta gefenshi ta fito jikinta yana rawa ta fara fad'in
"Don ALLAH ka yi hak'uri wajen Malam na zo na yita sallama banji an amsa ba shiyasa na shigo in ga ko lafiya"
Safwan ya maka mata wata Uwar harara sannan ya rungume hannu a K'irji ya ce,. "Lafiya kike nemansa? ba naga kunyi sallama ba ko Mahaifin naki ne ya amince zai bashi aurenki ne shiyasa kika zo yi masa albishir? "
Dije yanayin fuskarshi da tambayoyinshi sun sakata daburcewa, cikin rawar murya tace
"Kyautar da ya bani ce na zo kawo masa kayanshi sabida gidanmu ance bazan karb'a ba"
SAFWAN ya yi wani mere yace,. "Sai Kuma aka yi rashin sa'a shi ya bar garin gaba d'aya ya koma gida, cen zaki bishi garinsu ki kai masa ko yaya?"
Dije ta zaro ido tace,. "WALLAHI na koma da su sai sun janyo man gagarumar matsala, don ALLAH ka karb'a ka ajiye masa idan ka koma sai ka bashi abunshi kace na gode sosai ALLAH ya had'a fuskokinmu a aljannah, kuma ka yi masa albishir insha ALLAHu nice Matarshi a Lahira idan munje cen"
SAFWAN ya galla mata wata jar harara da jajayen idonshi da suka rine lokaci d'aya yace,. "Zaki bar wajen nan ko sai kin janyo na karairayaki a kaiwa kwad'ayayyen angonki sauran k'asusuwan???"
Dije ta yi saurin ja da baya tace,. "Don girman ALLAH ka karb'a WALLAHI dukana za'a yi gidanmu idan na koma da su"
Safwan ya buga mata wani uban tsaki ya shige d'akinsu tare da fad'in,.
"Idiot!!!"
Dije kam sanin idan ta koma da su gida akwai matsala ta lallaba ta jefa ledar kud'in cikin d'akin ta zank'ara da gudun tsiya, Maigarin da mutanenshi suna ganin fitowarta da gudu suka bita da kallo, Maigari ya mike tsaye jikinshi yana rawa yace
"Bari in je in dubo yaron Mutane kada ta kasheshi mu shiga uku, tunda shi har yanzu bai tashi barin garin ba duk da kyamar garin da yake yi"
Sauran mutanen su ka biyoshi baya har zuwa d'akin sai dai ganinshi da suka yi kwance yana latsar waya ne yasa hankalinsu ya kwanta, sannan suka koma suna ci gaba da yi da Dije da Baffah'nta, inda wasu suke ganin laifinshi akan abunda ya yi wa Maigarin yayin da wasu suke ganin hakan da ya yi shine dai dai.
Bikin yana saura kwana Uku aka gyarewa Dije d'akinta ram! gidan Inna Duduwa,Wanda Balan ya ci gado ga Mahaifinshi da ya mutu, don asalima d'akin Mahaifiyarshi ne da ta yi zama ciki lokacin da Mahaifinshi yana raye, don yanzu haka tana wani k'auye tana aurenta da yaranta biyar bayan Balan.
Biki sai kankama yake yi Bala da abokanshi da kawayen Dije Su Jummala sai shagalin bikinsu suke ta yi, don ana saura kwana biyu ne aka shirya wani bikin tauri a k'ofar gidansu Balan, inda yan tauri suka baje sai nuna k'warewarsu suke yi, sun burge iya burgewa in da bikin wasar taurin ya d'auki lokaci har cikin dare anata fafatawa da zaratan jaruman Yan taurin.
Ko da Safiya ta waye da d'ar d'ar ta shirya don ta zaci Baffah'n ya hanata zuwa Makaranta, amman sai gashi bai hanata ba har da yi mata ALLAH ya kiyaye, saboda yasan Shirin da yake yi akan auradda ita d'in cikin kankanin lokaci.
Dije sukuku ta zo Makarantar Lawi ya so ya yi mata magana amman tuno irin gargadin da Maigarin ya yi masa akanta yasa ya yi k'ok'arin kawar da kanshi gareta, don ko da aka tashi ma sai da kowa ya watse Makarantar sannan shi ya nufo masaukinsu, don gaba d'aya ma shi zaman garin ya gundureshi jin yake yi kamar a saman kaya yake, Alla Alla yake yi su kammala service dinsu su bar Garin, don akan hakan ma har abokin nashi ma sun fara zaman doya da manja dashi, gashi shi ma Maigarin yace ya zame hannunshi idan shi zai iya ga fili ga mai doki.
**
Cikin wata d'aya aka kammala neman auren Bala da Dije inda aka kawo komi na auren Rana kawai ake jira ta zo a sha shagali, izuwa lokacin Dije ta saduda dolenta saboda ba tirjiyar da bata yi ba akan auren amman Baffah'n kam ya kafe ba gudu ba ja da baya, don ita kanta Innar ganin akan auren Dije zasu samu matsala da Baffah'n shiyasa ta zubar da makamanta ta fara shirye shiryen auren Dijenta.
Ana saura sati d'aya bikin Dije suka zana jarabawar kammala primary, kowa sai murna yake yi inda shi Kuma Lawi yake cike da bak'in cikin rasa Dijen da yayi, Safwan kam ko kad'an bazaka gano yanayin da yake ciki ba, asali ma shi hankalinshi kwance yake ta d'aukar photuna da su Dije da sauran yaran Makarantar, Dijen ma ba wata walwala akan fuskarta don kuwa a kallo d'aya zaka gano sauyawar da ta yi, don kuwa gaba d'aya ra zabge sai Ido da karan hanci don izuwa lokacin har wata natsuwar dole ta ziyartota, duk nacin da Lawi ya yi akan yana so ya yi sallama da Dije bai sami wannan damar ba, saboda ganin yanda Safwan ya keta hidimar d'aukar pic's d'inshi da su Dijen.
Sai da aka gama ne ya samu ya yi wa Dije sallama tare da mika mata wata envelope idonshi jawur tamkar ya yi kuka, don shi ya kuduri aniyar ba zai jira ayi auren Dijen da shi ba, da nufin tun da sassafe ya had'a inashi inashi ya bar garin, don shi Safwan ya ce ba ranar zai tafi ba ya yi gaba shi zai biyoshi ta baya.
Dije tana kuka suka yi sallama da Lawi ta tura envelope d'in da ya bata a jaka ta nufi gida,. Kai tsaye ta shige toilet ta bud'a envelope d'in saboda ta matsu taga me ke ciki gashi bata son Inna ta gani.
Aiko sai gashi tana budawa taga wasu Yan hannu da zobe masu bala'in kyau sannan da bandur d'in kud'i sababbi kal yan d'ari bibbiyu, Dije ta zaro ido tare da goge hawayenta cikin sauri ta rungume kud'in da sauran kayan ta fashe da kuka gwanin ban tausayi, sai dai ita bata san duk abunda take yi Inna tana hankalce da ita, shiyasa lokacin da taga ta dad'e bayin ta biyo sawunta sai ko gashi ta ganta durk'ushe kasan bayin tana ta kuka, cikin tausayawa ta isa wurinta ta tadata Dije ta yi saurin yunkurin b'oye kud'in sai ga takardar kud'in ta yage kud'in sun zubo shaaaa! A k'asa.
Ku yi hakuri da kuskuren da kuka gani yau ban yi editing ba🤦🏻♀️
Akafta😉
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*MUTANEN DIJE K'ARANGIYA INA GAIDA KOWA ALL ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MAKU HAR GADON BACCINKU👍🏻*
*Lamba ta 22*
Daga Inna har Dijen gaba d'aya zaro Ido suka yi suna kallon kud'in, cikin firgici inna ta yi saurin fad'in
"Dije me nake Shirin gani yau Ni Hasiya?"
Dije ta yi saurin duk'atawa tana ta tattara kud'in har ta kammala sannan ta mik'awa Inna tace,. "Karb'i kyauta ce aka bani"
Inna ta tak'i karb'ar kud'in ta tsuke fuska tace,. "Gaya man duk fad'in garin nan waye mai arzik'in da har zai iya baki wad'annan mak'udan kud'in sababbi k'al da su haka?"
Dije ta saka hannu ta share hawayen da har lokacin basu daina zubo mata ba tace,. "Malaminmu D'anbirni ne ya bani wai tashi gudunmuwa ce yace ko Daddawa a siya man"
Inna ta maka mata wata jar harara tace,. "To WALLAHI Ni ba ruwana in har Baffah'nki ya ji wannan magana,sawunki a likkafa ki tattara kayanshi da kud'inshi ki je ki Kai masa salun alun ba wanda ya ji ba wanda ya gani"
Dije ta sake fashewa da wani sabon kuka tace,. "Ni dai Inna ina son awarwaron da zoben, don ALLAH ki bari in mayar masa da kud'in kawai don ALLAH Inna"
Ta k'are maganar cikin marairecewa gwanin ban tausayi, Inna ta karbe kud'in da awarwaron da zoben ta janyo hannunta suka fito tana janye da hannun Dijen har d'akinta, sannan ta samo wata leda baka ta zuba kud'in da kayan ta k'ulle jabau! Ta mika mata tare da had'e fuska alamun ba wasa tace,. "Karb'i kije ki mayar masa da kayanshi yanzun ba sai anjima ba"
Dije ta karb'a har ta fito ta dawo tace,. "To Inna ki bari in cire kayan Makarantar in saka na Gida"
Inna ta taso mata kamar zata daketa tace,. "Bazan bari ba nace ba za'a bari ba zaki je ko sai na sab'a maki ne yanzu Nan??"
Dije ta fice tana tafe tana gunguni har ta kai wani lungu ta bud'e ledar ta cire awarwaron da zoben ta k'ulle ledar ta nufi gidan Inna Gambo, sai da ta samu wani waje cikin dabara ta b'oyesu d'akin Gambon sannan ta fito ta nufi gidan Maigarin, sai dai rashin sa'ar da ta taka tun kafin ta isa daga nesa Maigarin da ya hangota ya bada umurnin a hanata zuwa wurinshi, saboda yaci alwashin daga Dijen har Baffah'n ba zai sake shiga cikin shirginsu ba, sai dai ita kam ta nace akan ita bazata koma ba don wurin Malaminsu ta zo ba wurinshi ba, Maigari kam ganin rigima zata b'alle ne a tsakanin Dijen da wani yaronshi yasa yace a kyaleta, kai tsaye ta nufi k'ofar d'akinsu Safwan ta fara rafka sallama sai dai ta yi har ta gaji ko sau d'aya bata ji an amsa mata ba, cike da k'unar rai ta fad'a d'akin da k'arfinta sai dai wayam ba kowa d'akin, tana k'ok'arin fitowa ne ta ji ta yi karo da mutum da sauri ta ja baya tana sosa goshinta da kan Safwan ya buge, Cikin tsoro ta rab'a ta gefenshi ta fito jikinta yana rawa ta fara fad'in
"Don ALLAH ka yi hak'uri wajen Malam na zo na yita sallama banji an amsa ba shiyasa na shigo in ga ko lafiya"
Safwan ya maka mata wata Uwar harara sannan ya rungume hannu a K'irji ya ce,. "Lafiya kike nemansa? ba naga kunyi sallama ba ko Mahaifin naki ne ya amince zai bashi aurenki ne shiyasa kika zo yi masa albishir? "
Dije yanayin fuskarshi da tambayoyinshi sun sakata daburcewa, cikin rawar murya tace
"Kyautar da ya bani ce na zo kawo masa kayanshi sabida gidanmu ance bazan karb'a ba"
SAFWAN ya yi wani mere yace,. "Sai Kuma aka yi rashin sa'a shi ya bar garin gaba d'aya ya koma gida, cen zaki bishi garinsu ki kai masa ko yaya?"
Dije ta zaro ido tace,. "WALLAHI na koma da su sai sun janyo man gagarumar matsala, don ALLAH ka karb'a ka ajiye masa idan ka koma sai ka bashi abunshi kace na gode sosai ALLAH ya had'a fuskokinmu a aljannah, kuma ka yi masa albishir insha ALLAHu nice Matarshi a Lahira idan munje cen"
SAFWAN ya galla mata wata jar harara da jajayen idonshi da suka rine lokaci d'aya yace,. "Zaki bar wajen nan ko sai kin janyo na karairayaki a kaiwa kwad'ayayyen angonki sauran k'asusuwan???"
Dije ta yi saurin ja da baya tace,. "Don girman ALLAH ka karb'a WALLAHI dukana za'a yi gidanmu idan na koma da su"
Safwan ya buga mata wani uban tsaki ya shige d'akinsu tare da fad'in,.
"Idiot!!!"
Dije kam sanin idan ta koma da su gida akwai matsala ta lallaba ta jefa ledar kud'in cikin d'akin ta zank'ara da gudun tsiya, Maigarin da mutanenshi suna ganin fitowarta da gudu suka bita da kallo, Maigari ya mike tsaye jikinshi yana rawa yace
"Bari in je in dubo yaron Mutane kada ta kasheshi mu shiga uku, tunda shi har yanzu bai tashi barin garin ba duk da kyamar garin da yake yi"
Sauran mutanen su ka biyoshi baya har zuwa d'akin sai dai ganinshi da suka yi kwance yana latsar waya ne yasa hankalinsu ya kwanta, sannan suka koma suna ci gaba da yi da Dije da Baffah'nta, inda wasu suke ganin laifinshi akan abunda ya yi wa Maigarin yayin da wasu suke ganin hakan da ya yi shine dai dai.
Bikin yana saura kwana Uku aka gyarewa Dije d'akinta ram! gidan Inna Duduwa,Wanda Balan ya ci gado ga Mahaifinshi da ya mutu, don asalima d'akin Mahaifiyarshi ne da ta yi zama ciki lokacin da Mahaifinshi yana raye, don yanzu haka tana wani k'auye tana aurenta da yaranta biyar bayan Balan.
Biki sai kankama yake yi Bala da abokanshi da kawayen Dije Su Jummala sai shagalin bikinsu suke ta yi, don ana saura kwana biyu ne aka shirya wani bikin tauri a k'ofar gidansu Balan, inda yan tauri suka baje sai nuna k'warewarsu suke yi, sun burge iya burgewa in da bikin wasar taurin ya d'auki lokaci har cikin dare anata fafatawa da zaratan jaruman Yan taurin.