Sashe 37
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana ƙare maganar ya miƙe tsaye ya karɓi butar da Inna take miƙo masa ya fice ƙofar gida zuciyarshi cike fal da farin ciki.
Bayan fitarshi ne Inna ta jawo hannunta da sauri suka yi ɗaki, ta maka mata wata uwar harara tace
"Na sake jin kin faɗi sirrin dake tsakaninki da Mijinki ko na gidan aurenki ga kowa sai na saɓa maki, ko da ko Baffah'n ne naji kin sake tona wata magana ba mai daɗi ba to ni kaɗai nasan abunda zan yi maki, tunda har na gano ke har yanzu baki da wayo, in kuma har kina son ya hanaki komawa ki daina makarantar da kike son zama likitan shikenan, kije ki yi ta faɗa har ya ji zafi ya ce ba zaki ci gaba da karatun ba"
Inna tana gama faɗar maganganun cike da jin haushi ta fice, Dije ta biyota tace "na Bari Inna ni yanzu ma ko da wani ya tambayeni cewa zan yi ina jin daɗin zama da shi har ma da ƙanwarshi Fiddausi, ai ya yi haka ko Inna?"
Innar ta juyo tace,. "Da kin taimaki kanki don muddin kika sake faɗar wani aibin da ya shafi aurenki to tsaf zai ce ba zaki koma birnin ba, shikenan sai ki dawo nan ki ci gaba da zaman tunda haka kike so"
Dije ta rufe bakinta tace,. "Laa! Kin ko ga sai yanzu na tuno Inna itama da Hajiyar sai da tace da ni kar in faɗa maku yana cin zalina"
Inna tace ",kinji ba tunda kin janyo ta fahimci baƙin surutunki naki ko?, To yanzu dai ki ko yi ɓoye sirrin Mijinki da na gidan aurenki ga kowa ma, ke har ni kaina nan bance ki faɗa man ba"
Dije ta toshe dariyar da ta zo mata tace,. "Har da ke Inna to ke wani zaki je ki faɗawa ne halan?"
Inna ta fice ɗakin tana faɗin "Maba zan baiwa kuɗi ya yi ta sanarwa yana shela ko'ina a garin nan sai kowa ma ya sani"
Dije ta tuntsure da dariya tace,. ,"ALLAH ya bar man ke Innata"
Inna ta ɗauki butarta ta yi bayi tana faɗin "ke kuma ya shirya man ke ba"
Da dare ko da Baffah ya dawo gidan da ledar tsirenshi da ya siyowa Dijen tuni har ta yi bacci, dole ya ajiye mata sai da safe sannan ya bata ta cenye tana yi wa Usmanu dariyar an bashi tsoka biyu.
Bayan ta yi wanka ne tace da Inna zata je gidansu Gambo su ƙara gaisawa, Inna ta ce da ita to ta jira a bata kayan tsarabar da aka kawo masu ta kai mata nata kaso, Baffah ya ce ta raba kayan a kaiwa duk wanda ALLAH yasa da rabonshi a ciki, ta fidda na Gambon Usmanu ya karɓa zai wuce mata da kayan a babur ɗinshi, sannan shi ya wuce birni wajen harkar kasuwancinshi.
Sauran na mutanen garin kuma ya kira yara da kanshi anata lissafa gida gida da wanda za'a kaiwa sabulu da Omon, ita kuma Dijen ya bata na Maigari ya ce ta fara zuwa gidanshi ta kai masa kafin ta je gidan Gambon.
Lanti da Mune sune suka riƙa kayan suka taka mata har gidan Maigarin, cikin natsuwa Dijen ta gayar da shi tare da Matanshi sannan ta karɓi kayan tsarabar ta bashi tare da yi wa uwargidan Maigarin ya jikinta akan kariyar da ta janyo mata lokacin gudun kura, duk da har lokacin bata koma dai-dai ba amman sunji daɗin kular da ta nuna masu, suna saka mata albarka ta fito gidan tare da jinjina yanda Dijen ta fara shiryuwa, saboda ganin yanda ta yi masu komi cikin ladabi ba kamar cen baya ba da ko gidan bata shigowa bale su sami arziƙin ta zo gayar da su.
Suna fitowa Dije tace da su Lanti gidan Gambo nik son in je amman zuciyata tana bani in fara zuwa wurin Jummala in ganota, saboda jiya da tausayinta na kwana Lanti musamman labarin gudowar da kuka ce tana yi, ina son inje inji dalilinta don gaskiya bana son a cutar da rayuwarta WALLAHi"
Mune ta sauke ajiyar zuciya tace,. "Hu'umm to ALLAH yasa Garbatin baya gida"
Suka haɗa baki wajen cewa "Ameen" Dije ta ƙara da cewa "ko ma yana gidan ai sai ya fito ya barmu mun gaisa da ƙawarmu"
Suka rankaya zuwa gidan Jummala sai dai tun kafin su isa suka fara jiyo kururuwar Jummala, cikin sauri suka ƙarasa cikin gidan abun mamaki ɗakin Jummalar a rufe amman sai kuwwa take zubawa tana magiya akan ya yi haƙuri, cikin faɗuwar gaba Dijen ta je bakin ƙofar ɗakin ta fara bubbugawa tana faɗin
"Jummala ki buɗe ɗakin me ya faru da ke ne? Buɗe nice Dije na zo ganinki"
Bubbugar ɗakin da Dijen take yi shi ya dawo da Garbatin daga duniyar ma'aurata da ya lula, cike da tsanani jin haushi ya sauko gadon yana gyara zaman kayanshi ya nufi Kofar ya buɗe, yana ƙarewa Dije kallo da jajayen idanuwanshi da suka so su baiwa Dijen tsoro, cikin dakiya tace
"Matsa daga nan ni ka bani hanya inga Jummalar tun kafin ka kasheta ka raba ganawar tamu"
Garbati ya yi maka mata wata harara tare da riƙe ƙofar yace,. "Sannu uwar Jummala to bari kiji WALLAHI da kin kawo iskanci har ki bar garin nan bazan taɓa barinki ki ga matata ba, don na sanki sarai da baƙin halinki tsaf zaki hure mata kunne ta bijire mani, bayan namijin ƙoƙarin da aka yi akan shawo kan matsalarta, don haka ki sani kika kuskura naji wani abu daga baya to ki sani duk garin nan ba mai hanani yin ƙasa ƙasa da ke idan na tashi gwada maki haukata"
Dije ta riƙe ƙugu tana maka masa wata harara sama da ƙasa tace,. "A tsammaninka share shayen da ka fara zai tsoratani ne?? To ka yi kuskure don kuwa Dijen Baffah tana nan yanda ka santa har ma da ƙarin wani ilimin baƙin halin da na ƙaro, zaka bani hanya in gano Ƙawata ko sai na fara nuna maka kalar baƙaƙen halayen nawa??"
Garbati ba shiri ya tuntsure da wata arniyar dariya yace,. "Ana iya shege a duniya yasin to ke Dije halan ance maki ni lusari ne kamar Tambari da kika renawa hankali?, To ni......"
Fitowar Jummalar ne ya sa shi yin shiru saboda turenshi da tayi da hannu biyu ta fito tana share hawaye ta janyo hannun Dijen suka shiga cikin ɗakin, Garbati ya bita da kallo yace
"Yanzu Jummala ni kika yi wa haka akan Dije?? Lalle kam yau sai kin nemi mai ƙwatarki hannuna"
Dije ta ɗaga murya tace, "ALLAH ya fika Garbati"
Jummala kam juyowa ta yi ta murguɗa masa baki wanda hakan da ta yi ba ƙaramar dariya ta bashi ba, ya sosa kanshi ya fice sannan su Mune suka shigo ɗakin su ma kowane da abunda zuciyarshi take ƙissima mashi.
Dije ta zauna kan gadon Jummala tana ƙare mata kallon mamakin yanda duk ta bi ta firgice ta rame saboda zalamar Garbati, ta riƙo hannunta tace
"Ƙawata baki da lafiya ne halan? Naga duk kin canza ba yanda na sanki ba"
Jummala ta kalli Mune da Lanti ta share hawayenta sannab tace,. "Ba komi"
Dije fahimtar tana son ta sanar da ita amman bata son su Mune su sani yasa ta ce da su Munen, "Don Allah Lanti ku jirani a waje zamu yi magana da Jummala kunji?, Kar fa kuji haushi kunsan komi yana buƙatar sirri"
Lanti kasancewar tasan saboda Mune ne yasa Jummala bata son fayyace sirrinta yasa ta miƙe ta fice, Mune ta taɓe baki ta miƙe ta fice tana gungunin faɗin
"To ALLAH na tuba mu miye ma ne bamu sani ba?"
Suna fita Jummala ta fashe da kuka Dije ta fara lallashinta tana faɗin,. "Ki yi haƙuri Jummala ki sanar dani matsalarki da kaina zan je wajen Maigari in sanar da shi aka maki haƙƙinki"
Jummala ta share hawayenta tace,. "Ai ba abunda za'a iya yi akan matsalata Dije saboda Garbati ya riga da ya sami ɗaurin gindinsu Babana, don asali ma sune suka bashi damar da har ya dinga yi man abunda yake man"
Kan Dije ya ƙulle da zancen Jummala cikin rashin fahimtar inda ta dosa tace,. "Wace dama ce suka bashi halan?? Gaske dai naga yana wata gadara ashe wuri ya samu"
Jummala ta saka gefen ɗankwalinta ta shafe fuskarta ta ce,. "Tun ranar da aka kawoni gidan nan ya fara bijiro mani da wani sabon iskanci, ganin da gaske yake yi yasa na ƙwaci kaina da ƙarfin tsiya na gudu gidanmu, amman tun cikin daren aka dawo masa dani, ke in taƙaice maki labari na jera sati ɗaya ina guduwa cikin dare ana dawo dani, a ranar da na cika kwana takwas a gidan nan ne Baba Ɗanliti ya zo da ƙatuwar igiyar ya ɗaureni kan gadon nan ta ko'ina, yanda ko motsin kirki bana iya yi bayan ya gama dukana yanata zagina, haka ya fice ya ce da Garbati duk abunda yake so ya yi dani kar ya ji tausayina, Garbati ganin wannan damar da ya samu yasa bai ji kunyar ALLAH ba ya yi ta cin zalina, ina kuka ina ihu amman bai ji tausayina ba ko kaɗan asali ma haka na kwana ɗauren, sai da safe ya kwance ni haka kullum dare Baba Ɗanliti yake zuwa yana ɗaureni har tsawon kwana uku sannan aka daina ɗaureni, shi kuma Garbati baya jin kunyar ALLAH baya tsoron aradu ta faɗo masa har yanzu bai fasa abunda ya ke yi ba"
Dije tace
"Ni Jummala har kinsa jikina ya yi sanyi WALLAHi, saboda nasan Baba Ɗanliti mutum ne shi mai kirki banyi tsammanin haka daga wajenshi ba, amman ki yi haƙuri tunda har kika ga anata dawo dake idan kin gudu to ana son ki zauna ne, don haka don Allah ki daina ihun da kike yi kina tonawa Mijinki asiri tunda har baya barin cin zalinki, insha ALLAHu watarana ko ance ya yi ma ba zai yi ba tunda har nasan yana sonki Jummala, ki ɗauka cewa ko yanzu sharrin sheɗan ne da kuma shaye shayen da ya fara"
Jummala ta yi saurin kallonta tace,. "Wa ya gaya maki yana shaye shaye ne?!"
Bayan fitarshi ne Inna ta jawo hannunta da sauri suka yi ɗaki, ta maka mata wata uwar harara tace
"Na sake jin kin faɗi sirrin dake tsakaninki da Mijinki ko na gidan aurenki ga kowa sai na saɓa maki, ko da ko Baffah'n ne naji kin sake tona wata magana ba mai daɗi ba to ni kaɗai nasan abunda zan yi maki, tunda har na gano ke har yanzu baki da wayo, in kuma har kina son ya hanaki komawa ki daina makarantar da kike son zama likitan shikenan, kije ki yi ta faɗa har ya ji zafi ya ce ba zaki ci gaba da karatun ba"
Inna tana gama faɗar maganganun cike da jin haushi ta fice, Dije ta biyota tace "na Bari Inna ni yanzu ma ko da wani ya tambayeni cewa zan yi ina jin daɗin zama da shi har ma da ƙanwarshi Fiddausi, ai ya yi haka ko Inna?"
Innar ta juyo tace,. "Da kin taimaki kanki don muddin kika sake faɗar wani aibin da ya shafi aurenki to tsaf zai ce ba zaki koma birnin ba, shikenan sai ki dawo nan ki ci gaba da zaman tunda haka kike so"
Dije ta rufe bakinta tace,. "Laa! Kin ko ga sai yanzu na tuno Inna itama da Hajiyar sai da tace da ni kar in faɗa maku yana cin zalina"
Inna tace ",kinji ba tunda kin janyo ta fahimci baƙin surutunki naki ko?, To yanzu dai ki ko yi ɓoye sirrin Mijinki da na gidan aurenki ga kowa ma, ke har ni kaina nan bance ki faɗa man ba"
Dije ta toshe dariyar da ta zo mata tace,. "Har da ke Inna to ke wani zaki je ki faɗawa ne halan?"
Inna ta fice ɗakin tana faɗin "Maba zan baiwa kuɗi ya yi ta sanarwa yana shela ko'ina a garin nan sai kowa ma ya sani"
Dije ta tuntsure da dariya tace,. ,"ALLAH ya bar man ke Innata"
Inna ta ɗauki butarta ta yi bayi tana faɗin "ke kuma ya shirya man ke ba"
Da dare ko da Baffah ya dawo gidan da ledar tsirenshi da ya siyowa Dijen tuni har ta yi bacci, dole ya ajiye mata sai da safe sannan ya bata ta cenye tana yi wa Usmanu dariyar an bashi tsoka biyu.
Bayan ta yi wanka ne tace da Inna zata je gidansu Gambo su ƙara gaisawa, Inna ta ce da ita to ta jira a bata kayan tsarabar da aka kawo masu ta kai mata nata kaso, Baffah ya ce ta raba kayan a kaiwa duk wanda ALLAH yasa da rabonshi a ciki, ta fidda na Gambon Usmanu ya karɓa zai wuce mata da kayan a babur ɗinshi, sannan shi ya wuce birni wajen harkar kasuwancinshi.
Sauran na mutanen garin kuma ya kira yara da kanshi anata lissafa gida gida da wanda za'a kaiwa sabulu da Omon, ita kuma Dijen ya bata na Maigari ya ce ta fara zuwa gidanshi ta kai masa kafin ta je gidan Gambon.
Lanti da Mune sune suka riƙa kayan suka taka mata har gidan Maigarin, cikin natsuwa Dijen ta gayar da shi tare da Matanshi sannan ta karɓi kayan tsarabar ta bashi tare da yi wa uwargidan Maigarin ya jikinta akan kariyar da ta janyo mata lokacin gudun kura, duk da har lokacin bata koma dai-dai ba amman sunji daɗin kular da ta nuna masu, suna saka mata albarka ta fito gidan tare da jinjina yanda Dijen ta fara shiryuwa, saboda ganin yanda ta yi masu komi cikin ladabi ba kamar cen baya ba da ko gidan bata shigowa bale su sami arziƙin ta zo gayar da su.
Suna fitowa Dije tace da su Lanti gidan Gambo nik son in je amman zuciyata tana bani in fara zuwa wurin Jummala in ganota, saboda jiya da tausayinta na kwana Lanti musamman labarin gudowar da kuka ce tana yi, ina son inje inji dalilinta don gaskiya bana son a cutar da rayuwarta WALLAHi"
Mune ta sauke ajiyar zuciya tace,. "Hu'umm to ALLAH yasa Garbatin baya gida"
Suka haɗa baki wajen cewa "Ameen" Dije ta ƙara da cewa "ko ma yana gidan ai sai ya fito ya barmu mun gaisa da ƙawarmu"
Suka rankaya zuwa gidan Jummala sai dai tun kafin su isa suka fara jiyo kururuwar Jummala, cikin sauri suka ƙarasa cikin gidan abun mamaki ɗakin Jummalar a rufe amman sai kuwwa take zubawa tana magiya akan ya yi haƙuri, cikin faɗuwar gaba Dijen ta je bakin ƙofar ɗakin ta fara bubbugawa tana faɗin
"Jummala ki buɗe ɗakin me ya faru da ke ne? Buɗe nice Dije na zo ganinki"
Bubbugar ɗakin da Dijen take yi shi ya dawo da Garbatin daga duniyar ma'aurata da ya lula, cike da tsanani jin haushi ya sauko gadon yana gyara zaman kayanshi ya nufi Kofar ya buɗe, yana ƙarewa Dije kallo da jajayen idanuwanshi da suka so su baiwa Dijen tsoro, cikin dakiya tace
"Matsa daga nan ni ka bani hanya inga Jummalar tun kafin ka kasheta ka raba ganawar tamu"
Garbati ya yi maka mata wata harara tare da riƙe ƙofar yace,. "Sannu uwar Jummala to bari kiji WALLAHI da kin kawo iskanci har ki bar garin nan bazan taɓa barinki ki ga matata ba, don na sanki sarai da baƙin halinki tsaf zaki hure mata kunne ta bijire mani, bayan namijin ƙoƙarin da aka yi akan shawo kan matsalarta, don haka ki sani kika kuskura naji wani abu daga baya to ki sani duk garin nan ba mai hanani yin ƙasa ƙasa da ke idan na tashi gwada maki haukata"
Dije ta riƙe ƙugu tana maka masa wata harara sama da ƙasa tace,. "A tsammaninka share shayen da ka fara zai tsoratani ne?? To ka yi kuskure don kuwa Dijen Baffah tana nan yanda ka santa har ma da ƙarin wani ilimin baƙin halin da na ƙaro, zaka bani hanya in gano Ƙawata ko sai na fara nuna maka kalar baƙaƙen halayen nawa??"
Garbati ba shiri ya tuntsure da wata arniyar dariya yace,. "Ana iya shege a duniya yasin to ke Dije halan ance maki ni lusari ne kamar Tambari da kika renawa hankali?, To ni......"
Fitowar Jummalar ne ya sa shi yin shiru saboda turenshi da tayi da hannu biyu ta fito tana share hawaye ta janyo hannun Dijen suka shiga cikin ɗakin, Garbati ya bita da kallo yace
"Yanzu Jummala ni kika yi wa haka akan Dije?? Lalle kam yau sai kin nemi mai ƙwatarki hannuna"
Dije ta ɗaga murya tace, "ALLAH ya fika Garbati"
Jummala kam juyowa ta yi ta murguɗa masa baki wanda hakan da ta yi ba ƙaramar dariya ta bashi ba, ya sosa kanshi ya fice sannan su Mune suka shigo ɗakin su ma kowane da abunda zuciyarshi take ƙissima mashi.
Dije ta zauna kan gadon Jummala tana ƙare mata kallon mamakin yanda duk ta bi ta firgice ta rame saboda zalamar Garbati, ta riƙo hannunta tace
"Ƙawata baki da lafiya ne halan? Naga duk kin canza ba yanda na sanki ba"
Jummala ta kalli Mune da Lanti ta share hawayenta sannab tace,. "Ba komi"
Dije fahimtar tana son ta sanar da ita amman bata son su Mune su sani yasa ta ce da su Munen, "Don Allah Lanti ku jirani a waje zamu yi magana da Jummala kunji?, Kar fa kuji haushi kunsan komi yana buƙatar sirri"
Lanti kasancewar tasan saboda Mune ne yasa Jummala bata son fayyace sirrinta yasa ta miƙe ta fice, Mune ta taɓe baki ta miƙe ta fice tana gungunin faɗin
"To ALLAH na tuba mu miye ma ne bamu sani ba?"
Suna fita Jummala ta fashe da kuka Dije ta fara lallashinta tana faɗin,. "Ki yi haƙuri Jummala ki sanar dani matsalarki da kaina zan je wajen Maigari in sanar da shi aka maki haƙƙinki"
Jummala ta share hawayenta tace,. "Ai ba abunda za'a iya yi akan matsalata Dije saboda Garbati ya riga da ya sami ɗaurin gindinsu Babana, don asali ma sune suka bashi damar da har ya dinga yi man abunda yake man"
Kan Dije ya ƙulle da zancen Jummala cikin rashin fahimtar inda ta dosa tace,. "Wace dama ce suka bashi halan?? Gaske dai naga yana wata gadara ashe wuri ya samu"
Jummala ta saka gefen ɗankwalinta ta shafe fuskarta ta ce,. "Tun ranar da aka kawoni gidan nan ya fara bijiro mani da wani sabon iskanci, ganin da gaske yake yi yasa na ƙwaci kaina da ƙarfin tsiya na gudu gidanmu, amman tun cikin daren aka dawo masa dani, ke in taƙaice maki labari na jera sati ɗaya ina guduwa cikin dare ana dawo dani, a ranar da na cika kwana takwas a gidan nan ne Baba Ɗanliti ya zo da ƙatuwar igiyar ya ɗaureni kan gadon nan ta ko'ina, yanda ko motsin kirki bana iya yi bayan ya gama dukana yanata zagina, haka ya fice ya ce da Garbati duk abunda yake so ya yi dani kar ya ji tausayina, Garbati ganin wannan damar da ya samu yasa bai ji kunyar ALLAH ba ya yi ta cin zalina, ina kuka ina ihu amman bai ji tausayina ba ko kaɗan asali ma haka na kwana ɗauren, sai da safe ya kwance ni haka kullum dare Baba Ɗanliti yake zuwa yana ɗaureni har tsawon kwana uku sannan aka daina ɗaureni, shi kuma Garbati baya jin kunyar ALLAH baya tsoron aradu ta faɗo masa har yanzu bai fasa abunda ya ke yi ba"
Dije tace
"Ni Jummala har kinsa jikina ya yi sanyi WALLAHi, saboda nasan Baba Ɗanliti mutum ne shi mai kirki banyi tsammanin haka daga wajenshi ba, amman ki yi haƙuri tunda har kika ga anata dawo dake idan kin gudu to ana son ki zauna ne, don haka don Allah ki daina ihun da kike yi kina tonawa Mijinki asiri tunda har baya barin cin zalinki, insha ALLAHu watarana ko ance ya yi ma ba zai yi ba tunda har nasan yana sonki Jummala, ki ɗauka cewa ko yanzu sharrin sheɗan ne da kuma shaye shayen da ya fara"
Jummala ta yi saurin kallonta tace,. "Wa ya gaya maki yana shaye shaye ne?!"