Sashe 83
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Baffah ya yi murmushi mai cike da jin daɗi ya ce "daman ita addu'ar a kullum mutum ya yi bata faɗuwa ƙasa banza, don haka muka roƙa kuma ga shi ALLAH ya cika muna gurunmu fiye da yanda muka yi tsammani, da ina da iko da na tara mutane na sanar da su cewa kada su gaji da yiwa ƴaƴansu addu'a, duk halin da suke a kullum su ci gaba da yi masu addu'ar shiriya saɓanin faɗin aibinsu a bakinsu, saboda addu'ar iyaye bata da shamaki wajen Ubangiji, da sunyi take tafiya sai dai ayi jinkiri wajen ganin sakamakon addu'ar, yanzu ga ki kamar ba ke ba kin natsu kin ajiye shirme da tsokana, kin ajiye jan faɗa da abun maganar da kike ta janyo muna a cen baya, ga shi Sakamakon haƙurin da muka yi ALLAH ya mayar muna da alkhairin da bamu zato ba bale tsammani"
Dije ta ce "hakane Baffah ALLAH ya ƙara shirya maka Ni"
Ameenn 🙏🏻
Akafta🤪
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*ALHAMDULILLAH!!!! ALHMDLLH!!! ALHMDLLH!! GIDAN AURE shine sunan book ɗina da zanyi a gaba, wadda take buƙata zata biya kuɗinta 300 kacal ta hanyar transfer ta wannan account ɗin HADIZA D AUTA 1230094555 access Bank, idan kuma kati ne zaki turo aritel ko mtn na ɗari uku to za'a turo ta wannan numbar 09032685442*
*Ƴargata Maman Sultan Ubangiji ya baki lafiya yasa kaffara, Mrs Naseer ina miƙo gaisuwata zuwa gareki akan namijin ƙoƙarinki ga book ɗina, my Ambash ALLAH ya saukeki lafiya mu zo mu ci rangyem, Asma'u Umar ki yi haƙuri na goge laifina🤗*
*Lamba 72 last page*
🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚
Baffah yana murmushin jin daɗi ya ce "Ameen Dijengalata amman fa ko haka aka tsaya Alhamdulillahi, don ba abunda za mu ce wa ALLAH sai godiya ALLAH ya sawa aurenmki albarka ya baku zaman lafiya ke da Mijinki da abokiyar zamanki duka, kuma ya baki ƴaƴa nagari masu albarka waɗanda zasu yi maki fiye da abunda kinka yi muna na alkhairi"
Dije sai "Ameen Ameen" take faɗi zuciyarta cike da jin daɗin samun iyaye nagari, sai da suka ɗan taɓa fira sannan ta dawo falon Inna suna cin abincin ana ci gaba da fira cikin raha da barkwanci.
Kwanansu Zee ɗaya direba ya kwashesu suka suka koma suka bar su Inna da kewarsu tare da jinjina lamarin Ubangiji, ganin yanda dukansu daga Zee har ita Fiddon sun saki jiki da su kamar cewa daman cen ƴan'uwan juna ne.
Bayan su Inna sun dawo daga rakiyarsu ne Hansai ta goye Sayyid ta yi ɓangarenta, Dije ta faɗa kujera tace
"Wash ALLAHna WALLAHI Inna gaba ɗaya jikina ciyo yake yi"
Inna ta zauna tana ƴar dariya ta ce "sai kin yi haƙuri kam don yanzu jikinki yake haɗewa daga ɗaukar ciki da haifuwar da kika yi, wani zubin ma har zazzaɓi wasu su ke yi a wannan lokacin"
Dije ta dafe goshinta ta ce "ai kam dai nima ina jin abinda nike ji a jikina"
Inna ta kalleta da kyau sannan ta ce
"Naji daɗin yanda yarinyar nan ta sauko kuka fahimci juna ga shi yanzu zamanku gwanin burgewa"
Dije ta yunƙura ta ta shi zaune sannan ta kalli Inna ta ce "kin dai gani Inna ga shi yanzu kamar ba'a yi ba ashe da kirkinta sharrin sheɗan ne da kuma mugun kishin Abban Sayyid da take yi"
Inna ta sauke ajiyar zuciya ta ce "duk macen duniya dole zata yi kishin mijinta, ke ba mijinta kawai ba duk abunda kake so a rayuwa dole ka yi kishin ganin wani ya raɓeshi, sai dai na wani ya fi wani don kowa da kalar dauriyarshi, shiyasa kika ji na ce da ke duk runtsi ki sa ya dawo da ita a matsayin matarshi, saboda ko da ta fita dole ne ya auri wata, kuma ita zata iya shigowa gidan da shirinta ƙarshe ma ta janye maki Mijin ya koma gareta a barki da cizon yatsa, amman in ita ce sanadiyyar wannan abun da ta aikata zai dakushe mata karsashi akan ko ma aikata wani mummunan abu saboda ganin igiya ɗaya ce ta rage a tsakaninsu, saɓanin wacce zai auro ba ita, don ba lalle bane ba ace ku fahimci juna, bale kuma ta barki ki ji daɗin zama gidan aurenki ko zama da Mijinki lafiya, don wata mace sharrinta ko sheɗan ya sarawa bala'in da ke tattare da ita, amman yanzu kin ga komi ya zama tarihi kuna zaman lafiyarku Masha Allah, wanda hakan da kuke shi zai ƙara farantawa mijinku rai ya ji daɗin kyautata maku"
Dije ta cire tagumin da ta yi ta ce "Lalle Inna na yarda da aka ce abunda babba ya hango yaro ko da ya hau sama bazai iya hangowa, kuma naji daɗin biyayyar da na yi wajen sakashi dawo da ita, yanzu ga shi abun Ni ma ya zamo mani alkhairi don baki ga yanda ta ke son Sayyid ba, bata bari ya zauna hannuna matukar ba abincinshi zai sha ba, kuma ina bashi take sake karɓeshi su tafi, shi kanshi Abbanshi sanadin wannan halin kirkin da take yi ne yasa ya sake mata sosai suna ɗasawa, sai dai wani lokacin ina jin ba daɗi idan naga yana kulata Inna, Amman idan na tuno da cewa itama fa Matarshi ce kamar Ni sai in baiwa zuciyata haƙuri don bana son ta fahimci ina jin zafinta"
Inna ta yi shiru sannan ta ce "hakan da kike yi ya yi kuma shine abunda ya dace ki yi, don yanda kike ji haka itama take ji amman ta ke haƙura saboda neman zaman lafiyarku, ALLAH ya baku haƙurin zama da junanku itama kuma ya bata nata rabo"
Dije ƙirjinta ya buga amman ta daure ta ce "Ameen inna Bari in je in kwanta Wallahi wani bacci nike ji a idona"
Inna ta bita da kallo cike da jin daɗin ganin yanda hankali ya shige Dijenta, sannan ta ce
"Duk baccin da ki ke son yi ai wannan baturen baya barinki sai dai in bai rikice ba"
Daga cen cikin ɗakin Dije ta ce "WALLAhi sai in tafiyata gidan Gambo in sha baccina in barku da shi ku yi ta fama"
Inna tana dariya ta ce
"Ai duk inda zaki je ki ɓoye sai an kai maki shi acen tunda mu bamu da abunda zamu ba shi"
Dije ta yi saurin faɗin
"Gaskiya Inna uwaye suna shan wahalar renon ƴaƴa a rayuwa"
Inna ta fashe da dariya ta ce
"Kamar yanda aka sha taki ba ai duk uwar da kika gani da ɗanta to ita kaɗai tasan wahalar da ta sha da abunta lokacin da yana ƙarami har girmanshi, ALLAH dai ya jiƙan iyayenmu da rahamomi Wallahi"
Dije ta ce "Ameen" sannan ta yi kwanciyarta aranta tana jinjina irin yanda iyaye mata suke shan wahalar reno musamman farkon haifuwa, wanda ita sai yanzu ta gano cewa ashe ba ƙaramin haƙuri Inna ta yi da ita ba, cikin zuciyarta sai addu'a take zubawa Innar saboda tuno irin abun maganar da ta yi ta janyo masu a baya, tana cikin tunanin ne wani ta yi dariya wani ta ɓata fuska har bacci ya yi awon gaba da ita.
****
Rayuwa mai daɗi Dije ta yi a gidansu saboda komi yi mata ake yi aikinta bacci da cin abinci sai kuma baiwa Sayyid nono, sannan da baiwa Malaminta dama wajen ƙara macewa kanta, don kuwa suna maƙale a waya ko wane lokaci yana nuna mata irin kewarta da ya yi, tare da sanar da ita da ta cika wata ɗaya a garin zai zo ya kwashesu su koma, cikin dubara take ta hilatarshi har ya bar zancen don bata son ya gano bata son komawar a lokacin, kada ya ga kamar ita bata yi kewarshi ba kamar yanda kullum yake sanar da ita irin damuwar da yake ciki, don Zee ta so binshi acen Abujar ya ce ta jira anan Yolar zai dinga zuwa akai akai wurinta, dole ta haƙura amman ba don ranta ya so ba sai don samun zaman lafiyar da ko kaɗan bata son abunda zai janyo wata fitina a tsakaninsu.
Satin Dije Uku a garin ta yi ɓul ɓul daga ita har yaronta gwani sha'awa saboda kulawar da suke samu wurin Inna da dattijuwar matar, a gefe ɗaya kuma Gambo da bata gajiya da dafa mata abubuwa tana shanyewa, don wani zubin acen ma take kwanciyarta daga ita yaronta da dattijuwar, ga Yan garin na su kowa sai nan nan ake yi da ita da kuma yaronta, don ma Gambo bata son ana yawan fita da shi don ƙa'ida ne kullum sai ta tofeshi da addu'o'in tsari, sannan ta ce dole itama Dijen sai ta tosheshi da addu'o'in saboda kariya daga sharrin mutum ko aljan da wasu masu kambun baki, saboda farin yaron da yanda yake kyakkyawa ga shi ɓul ɓul dole ne mutane su yi shaawarshi, sannan uwa uba ga shi fes fes kullum cikin shiga ta alfarma kuma irinta wayayyun ƴan birni.
****
Wasa wasa Dijen Baffah sai da ta yi wata biyu a garinsu sannan Angonta ya garzayo ya kwashi Matarshi da yaronshi suka koma Yola, suka bar su Inna da Baffah da mutanen garin da kewar Dijen da ɗan baturen yaronta mai kama da indiyawa samfurin larabawa kalar yan Ethiopia.
Hajiya Mama ba ƙaramin daɗi ta ji ba da ta ga yanda yaron da mamarshi suka yi sharr abunsu, cike da tsananin farin ciki ta karɓe shi tana ta yi masa wasa yana wasar baki, Fiddo ta karɓeshi tana faɗin
"Coming to your mama my beautiful boy"
Hajiya Mama ta kalleta tana dariya ta ce "in dai ɗanku ne ga shi nan don ma na yi maku kara na ɗauka?"
Fiddo tana dariya ta ce "WALLAhi Hajiyarmu son yaron nan Nike yi, don ALLAH ki ce da Yayanmu su tafi da Ni Abuja don bana son a rabani da shi ALLAH"
Hajiyar tana dariya ta ce "ki jira idan kunyi jarabawar ƙarshe sai ki tattara inaki inaki ki koma cen duka tunda ke baki fatar ki je naki gidan mijin sai taya wasu zaman aure"
Dije dai dariya kawai ta ke yi cikin dariyar ta ce "ai Insha ALLAHu acen ma zamu yi mata aure don bama fatar a raba uwa da ɗanta"
Dije ta ce "hakane Baffah ALLAH ya ƙara shirya maka Ni"
Ameenn 🙏🏻
Akafta🤪
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*ALHAMDULILLAH!!!! ALHMDLLH!!! ALHMDLLH!! GIDAN AURE shine sunan book ɗina da zanyi a gaba, wadda take buƙata zata biya kuɗinta 300 kacal ta hanyar transfer ta wannan account ɗin HADIZA D AUTA 1230094555 access Bank, idan kuma kati ne zaki turo aritel ko mtn na ɗari uku to za'a turo ta wannan numbar 09032685442*
*Ƴargata Maman Sultan Ubangiji ya baki lafiya yasa kaffara, Mrs Naseer ina miƙo gaisuwata zuwa gareki akan namijin ƙoƙarinki ga book ɗina, my Ambash ALLAH ya saukeki lafiya mu zo mu ci rangyem, Asma'u Umar ki yi haƙuri na goge laifina🤗*
*Lamba 72 last page*
🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚
Baffah yana murmushin jin daɗi ya ce "Ameen Dijengalata amman fa ko haka aka tsaya Alhamdulillahi, don ba abunda za mu ce wa ALLAH sai godiya ALLAH ya sawa aurenmki albarka ya baku zaman lafiya ke da Mijinki da abokiyar zamanki duka, kuma ya baki ƴaƴa nagari masu albarka waɗanda zasu yi maki fiye da abunda kinka yi muna na alkhairi"
Dije sai "Ameen Ameen" take faɗi zuciyarta cike da jin daɗin samun iyaye nagari, sai da suka ɗan taɓa fira sannan ta dawo falon Inna suna cin abincin ana ci gaba da fira cikin raha da barkwanci.
Kwanansu Zee ɗaya direba ya kwashesu suka suka koma suka bar su Inna da kewarsu tare da jinjina lamarin Ubangiji, ganin yanda dukansu daga Zee har ita Fiddon sun saki jiki da su kamar cewa daman cen ƴan'uwan juna ne.
Bayan su Inna sun dawo daga rakiyarsu ne Hansai ta goye Sayyid ta yi ɓangarenta, Dije ta faɗa kujera tace
"Wash ALLAHna WALLAHI Inna gaba ɗaya jikina ciyo yake yi"
Inna ta zauna tana ƴar dariya ta ce "sai kin yi haƙuri kam don yanzu jikinki yake haɗewa daga ɗaukar ciki da haifuwar da kika yi, wani zubin ma har zazzaɓi wasu su ke yi a wannan lokacin"
Dije ta dafe goshinta ta ce "ai kam dai nima ina jin abinda nike ji a jikina"
Inna ta kalleta da kyau sannan ta ce
"Naji daɗin yanda yarinyar nan ta sauko kuka fahimci juna ga shi yanzu zamanku gwanin burgewa"
Dije ta yunƙura ta ta shi zaune sannan ta kalli Inna ta ce "kin dai gani Inna ga shi yanzu kamar ba'a yi ba ashe da kirkinta sharrin sheɗan ne da kuma mugun kishin Abban Sayyid da take yi"
Inna ta sauke ajiyar zuciya ta ce "duk macen duniya dole zata yi kishin mijinta, ke ba mijinta kawai ba duk abunda kake so a rayuwa dole ka yi kishin ganin wani ya raɓeshi, sai dai na wani ya fi wani don kowa da kalar dauriyarshi, shiyasa kika ji na ce da ke duk runtsi ki sa ya dawo da ita a matsayin matarshi, saboda ko da ta fita dole ne ya auri wata, kuma ita zata iya shigowa gidan da shirinta ƙarshe ma ta janye maki Mijin ya koma gareta a barki da cizon yatsa, amman in ita ce sanadiyyar wannan abun da ta aikata zai dakushe mata karsashi akan ko ma aikata wani mummunan abu saboda ganin igiya ɗaya ce ta rage a tsakaninsu, saɓanin wacce zai auro ba ita, don ba lalle bane ba ace ku fahimci juna, bale kuma ta barki ki ji daɗin zama gidan aurenki ko zama da Mijinki lafiya, don wata mace sharrinta ko sheɗan ya sarawa bala'in da ke tattare da ita, amman yanzu kin ga komi ya zama tarihi kuna zaman lafiyarku Masha Allah, wanda hakan da kuke shi zai ƙara farantawa mijinku rai ya ji daɗin kyautata maku"
Dije ta cire tagumin da ta yi ta ce "Lalle Inna na yarda da aka ce abunda babba ya hango yaro ko da ya hau sama bazai iya hangowa, kuma naji daɗin biyayyar da na yi wajen sakashi dawo da ita, yanzu ga shi abun Ni ma ya zamo mani alkhairi don baki ga yanda ta ke son Sayyid ba, bata bari ya zauna hannuna matukar ba abincinshi zai sha ba, kuma ina bashi take sake karɓeshi su tafi, shi kanshi Abbanshi sanadin wannan halin kirkin da take yi ne yasa ya sake mata sosai suna ɗasawa, sai dai wani lokacin ina jin ba daɗi idan naga yana kulata Inna, Amman idan na tuno da cewa itama fa Matarshi ce kamar Ni sai in baiwa zuciyata haƙuri don bana son ta fahimci ina jin zafinta"
Inna ta yi shiru sannan ta ce "hakan da kike yi ya yi kuma shine abunda ya dace ki yi, don yanda kike ji haka itama take ji amman ta ke haƙura saboda neman zaman lafiyarku, ALLAH ya baku haƙurin zama da junanku itama kuma ya bata nata rabo"
Dije ƙirjinta ya buga amman ta daure ta ce "Ameen inna Bari in je in kwanta Wallahi wani bacci nike ji a idona"
Inna ta bita da kallo cike da jin daɗin ganin yanda hankali ya shige Dijenta, sannan ta ce
"Duk baccin da ki ke son yi ai wannan baturen baya barinki sai dai in bai rikice ba"
Daga cen cikin ɗakin Dije ta ce "WALLAhi sai in tafiyata gidan Gambo in sha baccina in barku da shi ku yi ta fama"
Inna tana dariya ta ce
"Ai duk inda zaki je ki ɓoye sai an kai maki shi acen tunda mu bamu da abunda zamu ba shi"
Dije ta yi saurin faɗin
"Gaskiya Inna uwaye suna shan wahalar renon ƴaƴa a rayuwa"
Inna ta fashe da dariya ta ce
"Kamar yanda aka sha taki ba ai duk uwar da kika gani da ɗanta to ita kaɗai tasan wahalar da ta sha da abunta lokacin da yana ƙarami har girmanshi, ALLAH dai ya jiƙan iyayenmu da rahamomi Wallahi"
Dije ta ce "Ameen" sannan ta yi kwanciyarta aranta tana jinjina irin yanda iyaye mata suke shan wahalar reno musamman farkon haifuwa, wanda ita sai yanzu ta gano cewa ashe ba ƙaramin haƙuri Inna ta yi da ita ba, cikin zuciyarta sai addu'a take zubawa Innar saboda tuno irin abun maganar da ta yi ta janyo masu a baya, tana cikin tunanin ne wani ta yi dariya wani ta ɓata fuska har bacci ya yi awon gaba da ita.
****
Rayuwa mai daɗi Dije ta yi a gidansu saboda komi yi mata ake yi aikinta bacci da cin abinci sai kuma baiwa Sayyid nono, sannan da baiwa Malaminta dama wajen ƙara macewa kanta, don kuwa suna maƙale a waya ko wane lokaci yana nuna mata irin kewarta da ya yi, tare da sanar da ita da ta cika wata ɗaya a garin zai zo ya kwashesu su koma, cikin dubara take ta hilatarshi har ya bar zancen don bata son ya gano bata son komawar a lokacin, kada ya ga kamar ita bata yi kewarshi ba kamar yanda kullum yake sanar da ita irin damuwar da yake ciki, don Zee ta so binshi acen Abujar ya ce ta jira anan Yolar zai dinga zuwa akai akai wurinta, dole ta haƙura amman ba don ranta ya so ba sai don samun zaman lafiyar da ko kaɗan bata son abunda zai janyo wata fitina a tsakaninsu.
Satin Dije Uku a garin ta yi ɓul ɓul daga ita har yaronta gwani sha'awa saboda kulawar da suke samu wurin Inna da dattijuwar matar, a gefe ɗaya kuma Gambo da bata gajiya da dafa mata abubuwa tana shanyewa, don wani zubin acen ma take kwanciyarta daga ita yaronta da dattijuwar, ga Yan garin na su kowa sai nan nan ake yi da ita da kuma yaronta, don ma Gambo bata son ana yawan fita da shi don ƙa'ida ne kullum sai ta tofeshi da addu'o'in tsari, sannan ta ce dole itama Dijen sai ta tosheshi da addu'o'in saboda kariya daga sharrin mutum ko aljan da wasu masu kambun baki, saboda farin yaron da yanda yake kyakkyawa ga shi ɓul ɓul dole ne mutane su yi shaawarshi, sannan uwa uba ga shi fes fes kullum cikin shiga ta alfarma kuma irinta wayayyun ƴan birni.
****
Wasa wasa Dijen Baffah sai da ta yi wata biyu a garinsu sannan Angonta ya garzayo ya kwashi Matarshi da yaronshi suka koma Yola, suka bar su Inna da Baffah da mutanen garin da kewar Dijen da ɗan baturen yaronta mai kama da indiyawa samfurin larabawa kalar yan Ethiopia.
Hajiya Mama ba ƙaramin daɗi ta ji ba da ta ga yanda yaron da mamarshi suka yi sharr abunsu, cike da tsananin farin ciki ta karɓe shi tana ta yi masa wasa yana wasar baki, Fiddo ta karɓeshi tana faɗin
"Coming to your mama my beautiful boy"
Hajiya Mama ta kalleta tana dariya ta ce "in dai ɗanku ne ga shi nan don ma na yi maku kara na ɗauka?"
Fiddo tana dariya ta ce "WALLAhi Hajiyarmu son yaron nan Nike yi, don ALLAH ki ce da Yayanmu su tafi da Ni Abuja don bana son a rabani da shi ALLAH"
Hajiyar tana dariya ta ce "ki jira idan kunyi jarabawar ƙarshe sai ki tattara inaki inaki ki koma cen duka tunda ke baki fatar ki je naki gidan mijin sai taya wasu zaman aure"
Dije dai dariya kawai ta ke yi cikin dariyar ta ce "ai Insha ALLAHu acen ma zamu yi mata aure don bama fatar a raba uwa da ɗanta"