Sashe 30
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Safwan ya yi masu jagora har katafaren gidanshi Baffah sai hamdala ya ke yi ga Ubangiji tare da jinjinawa hikimar Inna Gambo da ta fahimtar da hakan tun kafin ya zo ya ganewa idonshi.
Abokan tafiyarshi ma da matan sai jinjina kai suke yi suna fad'in
"ALLAH mai hikima yanzu wannan shi ne gidan Dije uwar tsiwa to ALLAh ya bada hak'urin zaman"
Safwan ya yi masu sha tara ta arzik'i sannan suka yi sallama da juna ya dawo gida su kuma Direba ya kwaahesu suka miki hanyar komawa gida.
Sauka lafiya😅
Akafta😊
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Masha ALLAH Mutanen Dije sannunku da k'ok'arin comments all musamman wad'annan groups d'in:*
*Ina farin cikin tayaki murnar cenye gasar da kika yi Ƙanwata waton Balkisu Muhammad Garkuwa (Ummi) ALLAH ya ƙara basira da ɗaukaka kuma ya ƙara dafa maki ga dukkan al'amurranki na yau da kullum tare da mu gaba ɗaya🤲🏻*
*Lamba ta 31*
Mai motar har ƙofar gidan Maigarin ya ajiyesu, kowane zuciyarshi cike da farin cikin nasarar dawowa gida lafiyar da suka yi, kafin kace me ƙofar gidan ta cika maƙil da yara da manya tare da wasu sauran matasan garin da suka rako motar tun daga farkon shigowa har zuwa ƙofar gidan Maigarin, sai kuwwa ake yi ana ta yi masu sannu da zuwa saboda uwar tafiyar da suka shawo.
Ba ƙaramin daɗi Maigarin ya ji ba saboda ganin karamcin da Safwan ya yi masu, don saƙonshi daban na musamman Safwan ya bada akawo mashi, don manyan riguna ne na alfarma waɗanda suka sha aiki tun daga sama har ƙasa kala biyu ya bada akawo mashi tare da turaruka masu kyau.
Shiyasa mai motar bai bar garin ba har sai da aka ciyar da shi da abinci yaci ya ƙoshi sannan ya kama hanyar komawa gida, Baffah da sauran waɗanda suka tafi kowa ya nufi gida zuciyarshi cike da farin cikin wannan tafiyar arziƙi da suka yi.
Inna Hasiya zaune ta yi ta tasa saƙon da Hajiya Mama ta bada akawo mata a gaba tana kallo, zuciyarta cike fal! da farin cikin ganin Dijenta ta yi sa'ar aure har ma da dace da suruka tagari da tayi, ba tare da ta tantance ba sai jin ta yi hawayen farin ciki suna sauka a kan fuskarta, cikin farin ciki Baffah ya ce
"Ba kuka zaki yi ba godiya ya kamata ki yi don kam tabbas Dije ta yi sa'ar aure, don ina tabbatar maki da cewa kaf faɗin garin nan namu ba wanda ya isa ya nunawa Dijeta Miji ke har ma da mutanen birnin duka, saboda ALLAH cikin hikimar ya jefo muna yaran nan don kawai su haska rayuwar Dijenmu, na yarda da maganar Inna Gambo da tace shi bawa bai san ta inda alkhairinshi yake ba, fatanmu kawai yanzu ALLAH Ubangiji ya basu zaman lafiya kuma ya ƙara masu haƙurin zama da Dijen"
Inna ta saka gefen zane ta share hawayenta cikin sanyin jiki tace,. ,"Ameen Malam amman ina jin tsoron Dije ta je ta yi abunda zai janyo girmanmu ya zube a idanunsu ka fa san halinta sarai, ko mu ya muka ƙare da ita balai Mutanen da basu san halinta ba?"
Baffah ya maka mata wata ƙatuwar harara ya ce,. "Idan kin san bakinki ba zai faɗi alkhairi akanta ba to ki yi haƙuri bana son maganar don ALLAH"
Inna ta miƙe tsaye tana ƙoƙarin kwashe kayan tace
"ALLAH ya baka haƙuri ita kuma ya sa ta canza ta zama dai dai da yanda ake son kowace macen kirki ta kasance gidan Mijinta"
Ya yi saurin sakin fuskarshi yace, "Ameen ko ke fa? Haka ya dace ki ce tun farko, ba ki wai ki zauna kina ta janyo maganganun da idan aka aunasu dai dai suke da muguwar fata ba"
Inna za ta yi magana kenan sai ga Usmanu ya shigo bakinshi har kunne ya ƙaraso wurinsu yana faɗin , "Sannu da zuwa Baffah ya hanya?"
Baffah ya washe baki yace, "Alhamdulillahi Usmanu ALLAH ya nufa mun dawo lafiya tare da abun alkhairin da aka cikomu da su"
Inna ta ajiye ledar da ke hannunta tana murmushin jin daɗi, Usman sai duba kayan yake yi yana faɗin
"Kai! Kai! Kai! Lalle Baffah Dijenka ta zama hamshaƙiya waɗannan kaya haka?"
Baffah ya janyo wata ledar ya fiddo shadda da turare yace,. "Kai ma ga naka sai ka ji daɗin yi wa ƴar uwarka addu'ar zaman lafiya gidan aurenta"
Usmanu cike da jin daɗi ya karɓa tare da rufe Bakinshi ya ce, "cabɗi ashe muma za mu shana? to ALLAH ya ba su zaman lafiya Baffah, kuma ya sa ta rage rashin jin nata don kar ta je ta janyo muna abun magana"
Baffah ya tsuke fuska yace,. "Alkhairi zaku gani daga kai har Uwarka, tunda ta bar maku filin gidan ai sai ku wataya yanzu"
Yana ƙare faɗar maganar ya miƙe ya nufi waje saboda sallamar da ya jiyo ana yi masa a ƙofar gida.
Inna da Usmanu suka bishi da kallo cikin sanyin jiki Inna tace, "Ni na rasa gano inda Malam ya nufa da mu da kullum yake ganin kamar mu bama son Dijen"
Usmanu ya yi saurin faɗin , "ya san sarai duk muna sonta Inna kawai dai don tana ƴar gaban goshinshi ne yake ƙin son a faɗi aibinta, bayan kuma mu gaskiya ce muke kai kuma ita muke faɗa, saboda gudun a barta ba kwaɓa ba hantara ta ƙara sangarcewa aje a shiga uku, yanzu dai tunda komi ya wuce fatan da za mu yi mata shine ALLAH yasa wannan auren ya zamo silar shiryuwarta, don kin ga mu fa in mun juri halinta WALLAHI su cen ba jura za su yi ba"
Inna ta sauke ajiyar zuciya tace, "ALLAH dai ya sa ta gyara mu ma ai farin cikinmu ne Usmanu"
Muryar Baffah da suka ji yo a bayansu yana faɗin "Ameen" shi yasa duk suka miƙe kowa ya nufi sabgoginshi, Baffah ya yi guntun murmushi yace
"Kuna nan zaune kuna gulmar Dije zaku ganinta ta zamo Babbar Hajiya ba tare da kun tantance ba"
Usman ya ƙumshe dariyarshi ya shige ɗakinshi zuciyarshi wasai saboda ganin bakinsu zai huta da bari barin Dije.
Kafin ka ce me gari ya ɗauka Dije ta auri ɗan gidan masu kuɗi a birni mutane sai shigowa yiwa Inna da Baffah sam barka ake yi,su Jummala da Lanti sun ji ina ma ace su ne suka sami wannan damar, don ko Balan Duduwa ma da ya ji labarin abun alkhairin da aka yi wasu Baffah kai tsaye ya nufi ɗakin Duduwa Bakinshi a washe yana faɗin
"Kin gani ko Duduwa ke da ke yi man faɗa kan abunda na yi yanzu ga shi ko Mahaifinta ya ji daɗin abun har wasu ma sun sheda"
Inna Duduwa ta maka masa wata ƙatuwar harara ta ce
"Kai tafi cen sakaran banza ashe daman cen son da kace kana yiwa Dijen na ƙarya ne tunda har ka karɓi kuɗi a matsayin fansar son da kake yi mata"
Balan ya turo baki irin na sangarta yace,. Haba Duduwa yanzu don ALLAH duk wannan tsiren da nake siyo maki kullum baki gode ba?, Yanzu ga shi naci riba biyu ga Matata kuma ga kuɗina ina mora, Ni dai WALLAHI kam banyi nadama ba don ni da ma zai sake ganin Ladiyo ya ce in bar masa ita ya biyani wasu kuɗin tsaf zan bar masa ita, ai da arziƙi gidan wasu gara gidanmu WALLAHI cab! Ai ni....."
Sai jin ya yi muryar Ladiyo a bayanshi da ke ƙoƙarin shigowa tana faɗin, "ai ni ma WALLAHI da ashe zai ganni ya ce yana so da sai nafi kowa murna, ko da zan huta da tusoshin da kake buga mani duk daren ALLAH kafin safiya ta waye ka yi ashirin"
Bala ya zabura ya ce,
"Don Ubanki ba tare da ke muke cin ƙuli ƙulin tsiren ba? Ko ba ke ma kina tusar ba? Shikenan ni na haƙura banyi ƙorafi ba ke zaki zo kina tona man asiri gaban Duduwa, to ba zaki sake cin tsiren da ƙulin ba baƙar munafuka"
Ladiyo ta riƙe ƙugu tana maka masa harara sama da ƙasa tana murguɗar masa baki, Duduwa ta yi sakato tana kallonsu cike da takaici tace,. "Kun dai ji haushi ku kam! Amman ko da yake kai ne babban mai laifin ba ita ba, ALLAH ya shiryeka da baƙin halin da ka tsirowa kanka daga jin ɗimin kuɗi a hannunka ka rikice saboda zalama, to tsiren ma idan ka sake kawo man sai na ci mutuncinka sakaran banza"
Tana ƙare faɗar maganar ta ɗauki zanenta ta yafa ta bar masu gidan tana tafe tana faɗa har gidan Inna Gambo, kasancewar ƙawarta ce ta ƙud da ƙud tun ƙurciya har yanzu da suka manyanta.
Sai dai faɗanta ya tsaya ne saboda ganin Gambo rungume da atamfofi biyu tana murna bakinta yaƙi rufuwa sai zubawa Dije ruwan addu'a take yi, Duduwa ta janyo kujera ƴar zuƙunno ta zauna tana faɗin
"Gambo wannan farin cikin daga ina haka?"
Gambo ta ɗaga Atamfofin sama tana kallonsu ido cikin ido tace,. "Daga hannun Jikata Dijen Sanda saƙo ne tun daga gidan mijinta ta çe akawo mani in saka in ji daɗin yi mata addu'ar nasarar zaman lafiya da Mijinta"
Gambo ta yi shiru sannan ta ce "Ah lalle dole ki yi farin ciki sosai to ALLAH ya haɗa hankulansu kafin nan da shekaru mu ga ƴan dugadugai suna yawo a tsakiyar gidan nan naki"
Gambo ta yi saurin faɗin, "Allahumma Ameen Duduwa karɓi goro ki tamna don mu ji daɗin yin firar"
Duwawa ta karɓi goron ta kai bakinta ta ramtsa tace, "Lalle wani hani ga ALLAH baiwa ne ya hanata Bala ya baiwa ɗanbirni, to ALLAH ya basu zaman lafiya daga ita har Balan tare da Matarshi Ladiyo"
Inna Gambo tace "Ameen ya rabbil'alamina Aminiyata"
Dije kam............😛
Ku yi manage insha ALLAHu maybe anjima ku jini matuƙar na samu yanda nike so😁
Akafta🤗
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
Abokan tafiyarshi ma da matan sai jinjina kai suke yi suna fad'in
"ALLAH mai hikima yanzu wannan shi ne gidan Dije uwar tsiwa to ALLAh ya bada hak'urin zaman"
Safwan ya yi masu sha tara ta arzik'i sannan suka yi sallama da juna ya dawo gida su kuma Direba ya kwaahesu suka miki hanyar komawa gida.
Sauka lafiya😅
Akafta😊
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Masha ALLAH Mutanen Dije sannunku da k'ok'arin comments all musamman wad'annan groups d'in:*
*Ina farin cikin tayaki murnar cenye gasar da kika yi Ƙanwata waton Balkisu Muhammad Garkuwa (Ummi) ALLAH ya ƙara basira da ɗaukaka kuma ya ƙara dafa maki ga dukkan al'amurranki na yau da kullum tare da mu gaba ɗaya🤲🏻*
*Lamba ta 31*
Mai motar har ƙofar gidan Maigarin ya ajiyesu, kowane zuciyarshi cike da farin cikin nasarar dawowa gida lafiyar da suka yi, kafin kace me ƙofar gidan ta cika maƙil da yara da manya tare da wasu sauran matasan garin da suka rako motar tun daga farkon shigowa har zuwa ƙofar gidan Maigarin, sai kuwwa ake yi ana ta yi masu sannu da zuwa saboda uwar tafiyar da suka shawo.
Ba ƙaramin daɗi Maigarin ya ji ba saboda ganin karamcin da Safwan ya yi masu, don saƙonshi daban na musamman Safwan ya bada akawo mashi, don manyan riguna ne na alfarma waɗanda suka sha aiki tun daga sama har ƙasa kala biyu ya bada akawo mashi tare da turaruka masu kyau.
Shiyasa mai motar bai bar garin ba har sai da aka ciyar da shi da abinci yaci ya ƙoshi sannan ya kama hanyar komawa gida, Baffah da sauran waɗanda suka tafi kowa ya nufi gida zuciyarshi cike da farin cikin wannan tafiyar arziƙi da suka yi.
Inna Hasiya zaune ta yi ta tasa saƙon da Hajiya Mama ta bada akawo mata a gaba tana kallo, zuciyarta cike fal! da farin cikin ganin Dijenta ta yi sa'ar aure har ma da dace da suruka tagari da tayi, ba tare da ta tantance ba sai jin ta yi hawayen farin ciki suna sauka a kan fuskarta, cikin farin ciki Baffah ya ce
"Ba kuka zaki yi ba godiya ya kamata ki yi don kam tabbas Dije ta yi sa'ar aure, don ina tabbatar maki da cewa kaf faɗin garin nan namu ba wanda ya isa ya nunawa Dijeta Miji ke har ma da mutanen birnin duka, saboda ALLAH cikin hikimar ya jefo muna yaran nan don kawai su haska rayuwar Dijenmu, na yarda da maganar Inna Gambo da tace shi bawa bai san ta inda alkhairinshi yake ba, fatanmu kawai yanzu ALLAH Ubangiji ya basu zaman lafiya kuma ya ƙara masu haƙurin zama da Dijen"
Inna ta saka gefen zane ta share hawayenta cikin sanyin jiki tace,. ,"Ameen Malam amman ina jin tsoron Dije ta je ta yi abunda zai janyo girmanmu ya zube a idanunsu ka fa san halinta sarai, ko mu ya muka ƙare da ita balai Mutanen da basu san halinta ba?"
Baffah ya maka mata wata ƙatuwar harara ya ce,. "Idan kin san bakinki ba zai faɗi alkhairi akanta ba to ki yi haƙuri bana son maganar don ALLAH"
Inna ta miƙe tsaye tana ƙoƙarin kwashe kayan tace
"ALLAH ya baka haƙuri ita kuma ya sa ta canza ta zama dai dai da yanda ake son kowace macen kirki ta kasance gidan Mijinta"
Ya yi saurin sakin fuskarshi yace, "Ameen ko ke fa? Haka ya dace ki ce tun farko, ba ki wai ki zauna kina ta janyo maganganun da idan aka aunasu dai dai suke da muguwar fata ba"
Inna za ta yi magana kenan sai ga Usmanu ya shigo bakinshi har kunne ya ƙaraso wurinsu yana faɗin , "Sannu da zuwa Baffah ya hanya?"
Baffah ya washe baki yace, "Alhamdulillahi Usmanu ALLAH ya nufa mun dawo lafiya tare da abun alkhairin da aka cikomu da su"
Inna ta ajiye ledar da ke hannunta tana murmushin jin daɗi, Usman sai duba kayan yake yi yana faɗin
"Kai! Kai! Kai! Lalle Baffah Dijenka ta zama hamshaƙiya waɗannan kaya haka?"
Baffah ya janyo wata ledar ya fiddo shadda da turare yace,. "Kai ma ga naka sai ka ji daɗin yi wa ƴar uwarka addu'ar zaman lafiya gidan aurenta"
Usmanu cike da jin daɗi ya karɓa tare da rufe Bakinshi ya ce, "cabɗi ashe muma za mu shana? to ALLAH ya ba su zaman lafiya Baffah, kuma ya sa ta rage rashin jin nata don kar ta je ta janyo muna abun magana"
Baffah ya tsuke fuska yace,. "Alkhairi zaku gani daga kai har Uwarka, tunda ta bar maku filin gidan ai sai ku wataya yanzu"
Yana ƙare faɗar maganar ya miƙe ya nufi waje saboda sallamar da ya jiyo ana yi masa a ƙofar gida.
Inna da Usmanu suka bishi da kallo cikin sanyin jiki Inna tace, "Ni na rasa gano inda Malam ya nufa da mu da kullum yake ganin kamar mu bama son Dijen"
Usmanu ya yi saurin faɗin , "ya san sarai duk muna sonta Inna kawai dai don tana ƴar gaban goshinshi ne yake ƙin son a faɗi aibinta, bayan kuma mu gaskiya ce muke kai kuma ita muke faɗa, saboda gudun a barta ba kwaɓa ba hantara ta ƙara sangarcewa aje a shiga uku, yanzu dai tunda komi ya wuce fatan da za mu yi mata shine ALLAH yasa wannan auren ya zamo silar shiryuwarta, don kin ga mu fa in mun juri halinta WALLAHI su cen ba jura za su yi ba"
Inna ta sauke ajiyar zuciya tace, "ALLAH dai ya sa ta gyara mu ma ai farin cikinmu ne Usmanu"
Muryar Baffah da suka ji yo a bayansu yana faɗin "Ameen" shi yasa duk suka miƙe kowa ya nufi sabgoginshi, Baffah ya yi guntun murmushi yace
"Kuna nan zaune kuna gulmar Dije zaku ganinta ta zamo Babbar Hajiya ba tare da kun tantance ba"
Usman ya ƙumshe dariyarshi ya shige ɗakinshi zuciyarshi wasai saboda ganin bakinsu zai huta da bari barin Dije.
Kafin ka ce me gari ya ɗauka Dije ta auri ɗan gidan masu kuɗi a birni mutane sai shigowa yiwa Inna da Baffah sam barka ake yi,su Jummala da Lanti sun ji ina ma ace su ne suka sami wannan damar, don ko Balan Duduwa ma da ya ji labarin abun alkhairin da aka yi wasu Baffah kai tsaye ya nufi ɗakin Duduwa Bakinshi a washe yana faɗin
"Kin gani ko Duduwa ke da ke yi man faɗa kan abunda na yi yanzu ga shi ko Mahaifinta ya ji daɗin abun har wasu ma sun sheda"
Inna Duduwa ta maka masa wata ƙatuwar harara ta ce
"Kai tafi cen sakaran banza ashe daman cen son da kace kana yiwa Dijen na ƙarya ne tunda har ka karɓi kuɗi a matsayin fansar son da kake yi mata"
Balan ya turo baki irin na sangarta yace,. Haba Duduwa yanzu don ALLAH duk wannan tsiren da nake siyo maki kullum baki gode ba?, Yanzu ga shi naci riba biyu ga Matata kuma ga kuɗina ina mora, Ni dai WALLAHI kam banyi nadama ba don ni da ma zai sake ganin Ladiyo ya ce in bar masa ita ya biyani wasu kuɗin tsaf zan bar masa ita, ai da arziƙi gidan wasu gara gidanmu WALLAHI cab! Ai ni....."
Sai jin ya yi muryar Ladiyo a bayanshi da ke ƙoƙarin shigowa tana faɗin, "ai ni ma WALLAHI da ashe zai ganni ya ce yana so da sai nafi kowa murna, ko da zan huta da tusoshin da kake buga mani duk daren ALLAH kafin safiya ta waye ka yi ashirin"
Bala ya zabura ya ce,
"Don Ubanki ba tare da ke muke cin ƙuli ƙulin tsiren ba? Ko ba ke ma kina tusar ba? Shikenan ni na haƙura banyi ƙorafi ba ke zaki zo kina tona man asiri gaban Duduwa, to ba zaki sake cin tsiren da ƙulin ba baƙar munafuka"
Ladiyo ta riƙe ƙugu tana maka masa harara sama da ƙasa tana murguɗar masa baki, Duduwa ta yi sakato tana kallonsu cike da takaici tace,. "Kun dai ji haushi ku kam! Amman ko da yake kai ne babban mai laifin ba ita ba, ALLAH ya shiryeka da baƙin halin da ka tsirowa kanka daga jin ɗimin kuɗi a hannunka ka rikice saboda zalama, to tsiren ma idan ka sake kawo man sai na ci mutuncinka sakaran banza"
Tana ƙare faɗar maganar ta ɗauki zanenta ta yafa ta bar masu gidan tana tafe tana faɗa har gidan Inna Gambo, kasancewar ƙawarta ce ta ƙud da ƙud tun ƙurciya har yanzu da suka manyanta.
Sai dai faɗanta ya tsaya ne saboda ganin Gambo rungume da atamfofi biyu tana murna bakinta yaƙi rufuwa sai zubawa Dije ruwan addu'a take yi, Duduwa ta janyo kujera ƴar zuƙunno ta zauna tana faɗin
"Gambo wannan farin cikin daga ina haka?"
Gambo ta ɗaga Atamfofin sama tana kallonsu ido cikin ido tace,. "Daga hannun Jikata Dijen Sanda saƙo ne tun daga gidan mijinta ta çe akawo mani in saka in ji daɗin yi mata addu'ar nasarar zaman lafiya da Mijinta"
Gambo ta yi shiru sannan ta ce "Ah lalle dole ki yi farin ciki sosai to ALLAH ya haɗa hankulansu kafin nan da shekaru mu ga ƴan dugadugai suna yawo a tsakiyar gidan nan naki"
Gambo ta yi saurin faɗin, "Allahumma Ameen Duduwa karɓi goro ki tamna don mu ji daɗin yin firar"
Duwawa ta karɓi goron ta kai bakinta ta ramtsa tace, "Lalle wani hani ga ALLAH baiwa ne ya hanata Bala ya baiwa ɗanbirni, to ALLAH ya basu zaman lafiya daga ita har Balan tare da Matarshi Ladiyo"
Inna Gambo tace "Ameen ya rabbil'alamina Aminiyata"
Dije kam............😛
Ku yi manage insha ALLAHu maybe anjima ku jini matuƙar na samu yanda nike so😁
Akafta🤗
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*