← Book details Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 84

Sashe 7

Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dije ganin hawaye ga fuskar Hansai yasa ta d'auki allonta ta lakamo kafad'ar Hansai din tace,. "To Zo muje na yafe maki amman don ALLAH ke baki san wacce ta fad'a ba cikinmu?"

Hansai ta share hawayenta cikin jin dad'in yafe matan da Dije tayi tace,. "WALLAHI bansani ba nikam Dije"

Dije tace,. "To yi shiru shikenan zaki zo Wasa Gidanmu ai anjima ko?"

Tace,. "Eh in Innata ta barni"

Dije tace,. "Zata ma barki ki zo nayi maki d'iyar kare mai shegen kyau"

Tace,. "To"

Sannan suka rankaya har cikin Makarantar inda Suka taradda ta cika fam! Sai karatu ake tayi, Dije taje ta bita karatunta ga Babban malaminsu, sannan ta d'auki bulalarta ta fara koyawa yara karatu, aiko suna ganinta kowa yasha jinin jikinshi sai d'aga murya suke yi suna ta karatu da k'arfin gaske, saboda sun san irin bala'in kashin da take basu wanda abu kad'an ne zai janyo yasa ta ci uban yaro, musamman wad'anda basu gane karatun su Kam ba k'aramar azaba take basu ba.

Don wani zubin ma Kan yaro take hayewa ta taushe masa kai tana muntsilarshi, wani zubin ma har cizo take had'awa mutum da shi in ta kama, don Iyayen yara da yawa sun Sha kawo kararta wurin Malamin musamman idan sunga shatin bulalar ko na muntsilar ko cizon da take yiwa 'ya'yansu, Malamin yana toshe kunnuwanshi ne kawai saboda bala'in k'ok'arin da take da shi gashi kuma yaran suna gane karatunta kuma tana natsar da Makaranta su daina rashin ji in tana wurin, sai dai yayi mata fad'a cikin hikima baya ma nuna mata wai k'ararta aka kawo don tsoron kada ta yi abunda zai fi wanda ta aikata .

Saboda ko baffanta ba'a kwana biyu ba'a Kai masa k'ararta ba akan ta daki wani ko taci zalin wani, iyakaci dai ya bada hak'uri idan ya shiga yayi ta nusar da ita akan ta rage tsaurara horon da take yiwa yaran.

Aiko bayan an tashi Makarantar ne suna tafe su biyar dinsu kamar kullum,har sai da suka kai wani lungu sannan Dije tace

"Yawwa daman Ina son in gano a cikinku wacece taje ta fad'i cewa Wai k'arya ce nake yi ba wata Kura??"

Kowa ya fara rantse rantsen ba shi bane Dije ta kalli Mune da kyau tace,. "Ke nasan duk cikinmu kinfi kowa bak'in surutun tsiya da fad'i ba'a tambayeki ba, don haka kece kika fad'a ai na ganoki yarinya"

Mune ta zaro Ido waje tana muzurai tace,. "WALLAHI Nima banso fad'a ba ai Babanmu naga garin gudu yaji ciyo a k'afa shine fa na fad'a masu gaskiya don su kwantar da hankalinsu"

Dije ta yi wani tsalle ta ciyo kwalar Mune tace,. "Yau ko za'a yi watandarki a bakin tekun zurmukus banbaradusa, ai daman nasan kece kika fad'a to kisani sai na yi kuli kulin rakkiya dake a garin nan yau"

Dije ta mik'awa Hansai allonta ta saki Mune tasha d'amara da gyalenta Mune tana ganin haka ta ce k'afa mi naci ban baki ba, aiko ta zunduma da gudunta Dije ta bita itama sauran kawayen nasu da wasu Yan kallo suka bisu a baya, sai ko gashi Mune taci karo da yayanta tayi saurin yin bayanshi ta b'oye, Dije tana kawowa ta yi tsalle ta dako Mune ta bayanshi, cikin fushi ya rik'e hannun Dijen yace

"Me tayi maki da zaki daketa?"

Dije ta fisge hannunta ta murgud'a masa baki tace,. "Ai Kaima kasan idan bata yi man komi ba haka kawai bazan biyota ba"

Yayan Mune ya kalleta cikin fushi yace,. "Waike me yasa kullum baki rabuwa da fad'a da anjaki da ba'a jaki ba ke duk sai kinyi?"

Dije ta hade fuska tana wani girgizar jiki tace,. "Ni dai ka matsa babu ruwanka kada Kuma in zo in yi maka wani abu aga laifina"

Yayan Munen ya rik'e Baki yace,. "Au ko Nima fasa man Kan zaki yi kamar yanda kika fasawa Bintalo goshi, don Kinga Maigari yace ayi maki hakuri a kyaleki shine kike ganin kamar tsoronki ake yi ko??, To bari kiji ni WALLAHI idan kika yarda kika shiga sabgata sai na lakad'a maki shegen duka a garin nan Inga mai d'aure maki gindi"

Dije ta ja baya da k'arfi ta ce. "He! he! he! daman shi abun dai ai shi abun fad'i yin kanshi yake yi don kuwa kanku aka farashi, ko ka manta duk garin nan kowa yasan cewa Iya Zulai barauniya c......."

Kafin ta k'arasa yayan Mune mai suna Tanbari ya Kai mata wani mahaukacin mari, Dije tace la.la.la. Ni ka mara?"

Cikin tsananin fushi yace,. "An mareki ke d'iyar Gidan Uban w.........."

Kafin ya k'arasa Dije ta duka cikin zafin nama ta debo k'asa ta watsa masa a cikin idanuwa, aiko tambari ya yi saurin kai mata wani uban naushi ta kauce da sauri.

Idonshi cike taf da k'asa ya fara Kaiwa iska naushi iya k'arfinshi yana fad'in,

"Yau sai na kassaraki na kamaki sai na kakkaryaki a garin nan"

Dije ma bakinta bai yi shiru ba sai ramawa take yi, Aiko yana fad'a Yana kaiwa iska naushi ta inda yake jiyo muryarta, har ya Kai wurin wani icce ya bugoshi da k'arfi sai gashi da fasa k'ara don kuwa kanshi yaci karo da iccen ya bugu da k'arfi ga hannunshi da ya naushi iccen, zafi biyu da biyu ya durk'ushe a k'asa yana murkususun wayyo hannunshi.

Akafta🤾🏻‍♂️🏃🏻‍♀️

D/AUTA CE✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*

*NA HADIZA D AUTA*

*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*

*MUTANEN DIJE K'ARANGIYA INA GAIDA KOWA ALL ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MAKU HAR GADON BACCINKU👍🏻*

*Lamba ta 8*

Mune ganin yayanta yana kuwwa yasa ta sake zundumawa da gudu ta yi gida da nufin taje ta fadowa Innarsu, Dije kam karbar Allonta ta yi ta kalli su Hansai tace

"Ku muje in kuma anan zaku tsaya sai in tafiyata"

Yayan Mune sai tsine mata yake yi Dije ta waigo tace,. "Ni bani da lokacinka tunda ALLAH ya saka man akanka, saura kuma idan ka tashi fad'i kace nice na ji maka ciyon a hannu"

Yanata surfa mata zagi tana masa dariya taja kawayenta suka tafi suka barshi anan, kowa idan aka kai gidansu ya shige masu ratsewa su yi hanyar da zata sadasu gidajensu kuma su ratse su tafi, suka bar Dije ita kad'ai tana tafe tana Yar wakarta zuciyarta cike da jin dad'in abunda ta yiwa Tambari, aiko sai gashi ta had'u da Bala wanda tun daga nesa da ya hangota fuskarshi a washe ya k'araso idonshi akanta yace,.

"A'ah su Dije Makaranta aka fito ne??"

Ta Kai kallonta gareshi ta bata fuska tace,. "Eh cen na fito"

Tana maganar tana ci gaba da tafiya abunta, Bala ya biyota a baya yace,. "Dije ki tsaya akwai maganar da nike son muyi Ni da ke"

Dije ta waigo ta rik'e kugunta tana yi masa wani kallon reni tace,. "Magana kuma? Bayan wadda muke yi da Kai yanzu?"

Ya gyara tsayuwarshi yana fesheta da wani arnen murmushi yace,. "Wannan ta musamman ce ai don WALLAHI na dad'e da abun cikin Raina sai dai tsoro yasa na yi ta b'oye abuta a cikin zuciyata"

Dije tana yi masa kallon Ido cikin Ido tace,. "Toh kace abun babba ne Bala? ALLAH yasa dai ba cewa za'a yi nayi wani abun ba kuma?"

Bala ya yi saurin fad'in,. "Ba kiyi komi ba na aibi Dije illah ni da kika sakani shiga damuwa da zullumi kullum safiya"

Dije cikin k'ulle kai da rashin gano inda zantukan Bala Suka nufa tace,. "To ai sai ka fad'a Kai tsaye basai ka tsaya zagaye zagaye ba"

Bala ya kafeta da kallo cikin tsananin kaunarta da ta cika masa zuciya yace,. "WALLAHI Dije sonki dai Nikeyi tun da dad'ewa, ammman na kasa furta maki ina jin tsoro"

Dije ta yi saurin dafe k'irji tace,. "Yanzu Kai Bala duk mutuncin da nake ganinka dashi ashe daman cen dan iska ne Kai ban sani ba??"

Balan ya zaro Ido waje yace,. "Iskanci kamar yaya Dije don nace Ina sonki shine nayi iskancin??"

Dije ta maka masa wata jar harara tace,. "Yo in ba iskanci ba me ya kawo zancen kana Sona? Ko ka d'auka Ni Yar iska ce kamar kai to WALLAHI wurin Duduwa zan kaika in sanar da ita don ta ja maka kunne tun kafin ka janyo Baffahna ya kasheni a garin nan"

Aiko ta juya ta nufi gidansu Bala, Bala ya bita yana magiya akan kar ta Fado ta rufa masa asiri ba zai sake yi mata maganar ba, amman Dije ta Kai wuya shiyasa bata fasa nufar gidan ba cikin fushi kamar wata zakanya, aiko tana shiga ta fara kwallawa Duduwa kira waton Kakar Bala ta wajen Uba da bayan rasuwar Mahaifiyarshi ya dawo hannunta.

Sai ko ga Duduwa ta fito d'aki tana gyara daurin zanenta tace, "lafiya kike kirana? injin dai ba bashinki naci ba?"

Dije ta k'araso ta kantare k'ugu tana wani cije Baki tana murgudashi tace,. "Aiko dole ki ganni tunda har Bala yake so ya maidani Yar iska kamarshi"

Tsohuwa Duduwa ta zaro Ido waje tace, "ke dakata Dije ki fita idona in rufe kada ki kuskura ki yiwa Balana sharri"

Dije ta yi mata wani kallo ta waiga bayanta inda Balan yake shigowa Gidan tace,. "Ai gashinan ki tambayeshi in har zai fadi tsakaninshi da ALLAH me ya fad'a mani yanzu?"

Bala ya k'araso yana dariya yace,. "WALLAHI Duduwa ba fa wani Abu nace da ita mai girma ba, cewa kawai fa nayi da ita Ina sonta shine fa ta ce sai ta kawoni k'ara wurinki"

Duduwa ta kalli Dije ta yi wani mere tace,. "Ke daga ma kin samu yace yana sonki shine zaki biyoshi Gida da kullin sharrinki? To don yace yana sonki miye abun iskanci a ciki?"

Dije ta galla mata harara tace,. "Au yanzu na gano Ashe da had'in bakinki yake so ya lalatani, to WALLAHI sai dai yaje ya bidi Yar iska dai dai shi don ni ba Yar iska bace bale yace yana sona"

Ta k'are maganar tare da murgud'awa Duduwa Baki, Duduwa ta zaro Ido tace

"Yo in dai har haka kawai don yace da ke yana sonki shine iskancin to Innarki Hasiya da Baffanki sun dad'e da iskancewa"
Chapter 7 · 0% Book details