Sashe 13
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
SAFWAN kam cikin Bacci ya fara jin abu yana hawa jikinshi, wani jarumin beran ma cikin k'warewa da mugunta ya cafko masa farcen k'afa da k'arfi sai ga Malam Safwan a zabure tare da kwallah k'ara, idonshi suna kaiwa kan berayen ya fasa wata arniyar k'ara ya nufi k'ofar fita, sai dai mamakinshi rufe take gam gam ba alamun zata iya budewa, SAFWAN kam ya fara tsalle yana ihu Berayen suka firgice suma su ka dinga gudu suna neman maboya, wurin gudun ne wasu Suka yo kanshi aka yi sa'a wani zai hau sama ya kuskure sai gashi ya fado jikinshi, cikin firgici ya fasa wata arniyar k'ara tare da yin tsalle sai ga bera ya shige cikin rigarshi, Safwan ya ci gaba da ihu yanata tsalle har ya samu ya fito rigar da k'yar, amman duk da hakan bai daina zuba ihun ba don kafin kace me k'ofar d'akin nasu ta cika fam da dan Adam, don kuwwar da yake yi iya karfinshi ta janyo hankulan Mutane da yawa ciki kuwa har da Lawi da ke dawowa daga wajen kiran wayar da yayi da mutanen gidansu, kai tsaye aka fara k'ok'arin buge kwadon don a samu k'ofar d'akin ta bud'e, sai dai kafin ma a sami sa'ar budewa tuni Malam Safwan ya some saboda tsabar tashin hankali da firgici da tsoron da ya kamashi, don daman cen shi babu abunda yake tsoro a duniya face b'eraye, akan bera guda d'aya sai ya hargitsa d'aki kaf wajen nemanshi don kuwa muddin akwai bera a d'aki to kam sam shi bashi ba bacci a ranar har sai ya kasheshi sannan ne hankalinshi ke kwanci, to gashi yanzu ya janyo Dije ta yi masa gudunmuwa da manyan zaratan lukutayen kosashin Berayen kauyensu.
Aikuwa ko da aka samu sa'ar bud'e d'akin kwance yake a sheme tsakiyar d'akin tsilla tsillan berayen sai hawa suke yi kanshi suna ta wasa, ganin Berayen yasa Lawi firgicewa saboda yasan yanda Abokinshi yake tsananin tsoronsu, cikin zafin nama ya dauko ruwa ya kandama masa, sai gashi da sauke k'atuwar ajiyar zuciya ya mike a zabure ya fito d'akin yana ihun kiran wayyo a taimakeshi beraye zasu kasheshi.
Mutane kam sai kumshe dariyarsu suke yi ganin wai shi duk akan bera ne yake wannan firgici da tashin hankali har da su suma, Lawi kam sanin wanene abokin nashi da beran ya nufi wajenshi yana ta bashi Baki, sai dai ganin babban farcenshi na k'afa yana zubar jini yasa ya gano ba k'aramar barna Berayen suka yi masa ba, uwa uba fuskarshi da wuyanshi da ya yi jawur ga sawun yagar beran nan ya fito a jikinshi kasancewarshi farin mutum wurin yayi jawur, da kyar ya ciyo kanshi ya daina haukar da yake yi ya samu natsuwa ta ziyartoshi, ya jashi ya kaishi gindin iccen da ke k'ofar gidan Maigarin ya zaunar dashi, maigarin da sauran mutanen kowa sai yi masa sannu suke yi.
Maigarin yasa aka fito da Berayen d'aya bayan d'aya anata kashesu, amman duk da hakan Safwan kafewa yayi akan shi ba zai sake shiga d'akin ba, don ko wunin ranar ma duk a waje yayi komi saboda tsoron shiga d'akin da yake yi, lokacin da dare yayi ma Dole sai d'akin wasu samarin yaran Maigarin aka kai shi ya yi bacci, amman duk da hakan motsi kad'an zai sa ya zabura haka ya kwana zuciya ba natsuwa.
Ko da safiya ta waye tun da sassafe ya nufi Makarantarsu Dije don ko karyawa bai jira ya yi ba saboda gaba d'aya zama gidan ya gundureshi, aka yi dace itama Dijen ta yi sammakon fitowa don kusan ma itace ta biyu ko uku da zuwa Makarantar duka, tana hangoshi saman baranda kanshi duke yanata tunani ta fara kumshe dariyarta, ta yi k'ok'arin saita kanta ta isa wurinshi ta tsaya gabanshi cikin jarumta tace
"Toch me toch fire live me live dengerous your cross the bala'i kaddara your business for nown you tunani in kwakwalwarka"
Tana kare maganar ta gyara zaman Jakar fatar da ke rataye a kafad'arta ta yi masa wani kallo ta wuce fuuu abinta zuwa class dinsu, don tsoron ya sake yi mata irin dukan da yayi mata ranar, Safwan kam binta yayi da wani kallon tafi cen sakarai yana wani mere sai cen Kuma ya tuntsure da wata arniyar dariya, don a iya zamanshi garin ko Murmushi bai tab'a yi ba amman sai gashi yau da kyakyatawa kuma duk a sanadin abokiyar fadan nashi Dije, yarinyar da yake jin tsanarta har cikin zuciyarshi tsana irin wadda bai tab'a yiwa kowa irinta ba.
Yabi bayanta da kallo yana dariyar takaici yace, "crazy girl"
Dije kam murna kawai take yi shima yau ta wankeshi da turanci don ya gano cewa ita d'in ba jahila bace kamar yanda yake kallonta, taji matuk'ar dad'in samun aron littafin da Lawi ya bata don kuwa dashi ta ke kwana a saman kanta tana hardar kalamai tana had'a wannan da wancen ta yi magana cikin turancin duk da ba dai dai take yi ba amman ba laifi tana kamo hanya.
Har aka tashi school Safwan bai da wata natsuwa Dije kam sai jinta take yi cikin nishadi, don tasa a ranta duk ya kuskura ya sake yi mata wani abun abunda zata yi masa a gaba sai yafi wanda ta yi masa a yanzu.
Safwan kam kalamanta sun saka ya zargi cewa ko itace ta yi masa wannan horon da Berayen?, Sai dai ya sa a ranshi zai binciki kawarta d'aya idan har da gaske ita din ce to shi ko sai ta yabawa aya zakinta, aiko safiya tana wayewa ya yi sammako kamar yanda ya yi jiyan sai gashi ko Mune da su jummalo sun zo zasu wuce ya kira mune ta k'araso wurinshi cikin ladabi ta gayar dashi, sannan ya yi mata tambayar cewa
"Kawarki ta gaya maku cewa ta saka man beraye a d'aki ko?"
Mune ta fara waige waige tace, "A'a ba Ni ta fad'awa ba su Jummala ne ta fad'awa"
Safwan ya had'e fuska yace,. "Au da gaske kenan itace ta saka man?"
Mune ta rufe bakinta da sauri tace,. "Ni ma ban sani ba na dai ji tana fad'awa su jummalar don ni yanzu ko magana na yi mata bata amsa man gaba take yi dani"
Ta k'are maganar cikin taruwar kwallah a idonta, Safwan ya bita da kallon mamakin ashe zarginshi ya zama gaskiya ita din ce amman Lawi ya tsaya Kai da fata yanata kareta tare da wanketa tas da soso da sabulu, cikin k'ara tsuke fuska yace
"Me ya had'aku da har take gaba da ke?"
Mune tana shirin bashi amsa ne ta hango Dije tafe tana tsallen jin dad'i tana yan wakokinta, ta yi saurin dafe k'irjinta tace
"Na shiga Uku don ALLAH kar kace Ni na fad'a maka WALLAHI dukana zata yi in taji"
Cikin rawar jiki Mune ta bar wajen da sauri har da su gudunta ta shige ajinsu, Dije Kam duk da ta hangosu amman ko kallo bai isheta ba ta dage kanta sama ta shige aji, sai ko gashi ya shigo class d'in yayi masu karatu saboda takaicin Dijen ko tambaya d'aya bai tambayeta ba, don ko ta d'aga hannu da nufin bada wata amsar sai ya basar da ita ya zab'i wata, haka yayi ta yi tun Dije bata damu ba har ta zo wuya itama ta daina d'aga hannun.
Ko da aka tashi ya sakata kamun kunne cikin rana tsoron ya daketa yasa ta kama kunnen, tun tana juriya har ta kai ta fara kuka tana fad'in jininta zai dawo ta kai zubowa zai yi k'asa idan taci gaba, ya ce ta koma yin kneel down ta d'aga kanta sama ta kalli rana hannuwanta duka biyu ya d'ora mata duwatsu masu dan girma yace kuma ta yarda suka fad'i jikinta ya gaya mata.
Dije tsawon minti sha biyar tana kallon ranar da taji azaba ta Kai mata karo ta fad'i sheme alamun aljanun sun zo, Safwan ya dauko bulala zai daketa ta yi saurin tashi tana fad'in
"Don girman ALLAH Malam ka yi hakuri yunwa nike ji ka bari in je gida"
Yace da ita suna nan har marece sai ta fad'i uban da yasa ta saka masa beraye a d'aki, Dije ta fara rantsuwar ba ita bace Mune ce amman duk da hakan sai da yayi mata bulala goma tare da gargadin ko kallonshi ta sake yi sai ya nakasata bale har ta sake shirya masa wata mugunta.
Dije ta dawo gida sai kumbure kumburen fuska take yi sai dai taki fad'in abunda yayi mata don kada Baffah yace bazata sake zuwa Makarantar ba.
Marece sakaliya ta tanadi kuka da toshshi ta k'ulle a leda, tana ta harkokinta har zuwa dare sannan ta sassada ta debi garwashin wuta cikin wani mataccen kwano ta rufe ta fita, Kai tsaye Gidan Maigarin ta nufa tamkar wacce aka aika tana shiga sashen d'akinsu Safwan d'in, ta ajiye kwanon ta fiddo tosshi da kukar da ta makale jikinta ta leka d'akin ta hangoshi yanata danne dannen wayarshi, ta dawo ta watsa tosshin da kukar ta yi saurin zuwa ta ajiye masa a bakin k'ofar ta janyo d'akin da sauri ta sake rufewa da wani k'aton iccen katako ta dantseshi ta tafiyarta"
Safwan kam ko da ya ji sautin rufe d'akin yayi saurin Kai kallonshi ga k'ofar, abun mamaki sai ga hayaki ya hango yana fitowa cikin kwanon mikewar da zai yi bala'in azabar da ke cikin hayakin ta fara kaiwa idonshi da hancinshi ziyara, aiko nan take ya fara atishaya ya yi ta dukan k'ofar akan a bud'e masa ba kowa wajen don Lawi ma yana wurin Maigarin sunata firarsu, aiko tun yana iya gane gabanshi har hayakin ya turnuke d'akin ko hannunshi baya gani ga kuma tsananin azabar da ke cikin hayakin, ko da Lawi da sauran Yan Gidan suka zo kawo masa agaji tuni Safwan ya galabaita sai sauke numfashin yake yi a wahalce yana nishi sama sama.
Aikuwa ko da aka samu sa'ar bud'e d'akin kwance yake a sheme tsakiyar d'akin tsilla tsillan berayen sai hawa suke yi kanshi suna ta wasa, ganin Berayen yasa Lawi firgicewa saboda yasan yanda Abokinshi yake tsananin tsoronsu, cikin zafin nama ya dauko ruwa ya kandama masa, sai gashi da sauke k'atuwar ajiyar zuciya ya mike a zabure ya fito d'akin yana ihun kiran wayyo a taimakeshi beraye zasu kasheshi.
Mutane kam sai kumshe dariyarsu suke yi ganin wai shi duk akan bera ne yake wannan firgici da tashin hankali har da su suma, Lawi kam sanin wanene abokin nashi da beran ya nufi wajenshi yana ta bashi Baki, sai dai ganin babban farcenshi na k'afa yana zubar jini yasa ya gano ba k'aramar barna Berayen suka yi masa ba, uwa uba fuskarshi da wuyanshi da ya yi jawur ga sawun yagar beran nan ya fito a jikinshi kasancewarshi farin mutum wurin yayi jawur, da kyar ya ciyo kanshi ya daina haukar da yake yi ya samu natsuwa ta ziyartoshi, ya jashi ya kaishi gindin iccen da ke k'ofar gidan Maigarin ya zaunar dashi, maigarin da sauran mutanen kowa sai yi masa sannu suke yi.
Maigarin yasa aka fito da Berayen d'aya bayan d'aya anata kashesu, amman duk da hakan Safwan kafewa yayi akan shi ba zai sake shiga d'akin ba, don ko wunin ranar ma duk a waje yayi komi saboda tsoron shiga d'akin da yake yi, lokacin da dare yayi ma Dole sai d'akin wasu samarin yaran Maigarin aka kai shi ya yi bacci, amman duk da hakan motsi kad'an zai sa ya zabura haka ya kwana zuciya ba natsuwa.
Ko da safiya ta waye tun da sassafe ya nufi Makarantarsu Dije don ko karyawa bai jira ya yi ba saboda gaba d'aya zama gidan ya gundureshi, aka yi dace itama Dijen ta yi sammakon fitowa don kusan ma itace ta biyu ko uku da zuwa Makarantar duka, tana hangoshi saman baranda kanshi duke yanata tunani ta fara kumshe dariyarta, ta yi k'ok'arin saita kanta ta isa wurinshi ta tsaya gabanshi cikin jarumta tace
"Toch me toch fire live me live dengerous your cross the bala'i kaddara your business for nown you tunani in kwakwalwarka"
Tana kare maganar ta gyara zaman Jakar fatar da ke rataye a kafad'arta ta yi masa wani kallo ta wuce fuuu abinta zuwa class dinsu, don tsoron ya sake yi mata irin dukan da yayi mata ranar, Safwan kam binta yayi da wani kallon tafi cen sakarai yana wani mere sai cen Kuma ya tuntsure da wata arniyar dariya, don a iya zamanshi garin ko Murmushi bai tab'a yi ba amman sai gashi yau da kyakyatawa kuma duk a sanadin abokiyar fadan nashi Dije, yarinyar da yake jin tsanarta har cikin zuciyarshi tsana irin wadda bai tab'a yiwa kowa irinta ba.
Yabi bayanta da kallo yana dariyar takaici yace, "crazy girl"
Dije kam murna kawai take yi shima yau ta wankeshi da turanci don ya gano cewa ita d'in ba jahila bace kamar yanda yake kallonta, taji matuk'ar dad'in samun aron littafin da Lawi ya bata don kuwa dashi ta ke kwana a saman kanta tana hardar kalamai tana had'a wannan da wancen ta yi magana cikin turancin duk da ba dai dai take yi ba amman ba laifi tana kamo hanya.
Har aka tashi school Safwan bai da wata natsuwa Dije kam sai jinta take yi cikin nishadi, don tasa a ranta duk ya kuskura ya sake yi mata wani abun abunda zata yi masa a gaba sai yafi wanda ta yi masa a yanzu.
Safwan kam kalamanta sun saka ya zargi cewa ko itace ta yi masa wannan horon da Berayen?, Sai dai ya sa a ranshi zai binciki kawarta d'aya idan har da gaske ita din ce to shi ko sai ta yabawa aya zakinta, aiko safiya tana wayewa ya yi sammako kamar yanda ya yi jiyan sai gashi ko Mune da su jummalo sun zo zasu wuce ya kira mune ta k'araso wurinshi cikin ladabi ta gayar dashi, sannan ya yi mata tambayar cewa
"Kawarki ta gaya maku cewa ta saka man beraye a d'aki ko?"
Mune ta fara waige waige tace, "A'a ba Ni ta fad'awa ba su Jummala ne ta fad'awa"
Safwan ya had'e fuska yace,. "Au da gaske kenan itace ta saka man?"
Mune ta rufe bakinta da sauri tace,. "Ni ma ban sani ba na dai ji tana fad'awa su jummalar don ni yanzu ko magana na yi mata bata amsa man gaba take yi dani"
Ta k'are maganar cikin taruwar kwallah a idonta, Safwan ya bita da kallon mamakin ashe zarginshi ya zama gaskiya ita din ce amman Lawi ya tsaya Kai da fata yanata kareta tare da wanketa tas da soso da sabulu, cikin k'ara tsuke fuska yace
"Me ya had'aku da har take gaba da ke?"
Mune tana shirin bashi amsa ne ta hango Dije tafe tana tsallen jin dad'i tana yan wakokinta, ta yi saurin dafe k'irjinta tace
"Na shiga Uku don ALLAH kar kace Ni na fad'a maka WALLAHI dukana zata yi in taji"
Cikin rawar jiki Mune ta bar wajen da sauri har da su gudunta ta shige ajinsu, Dije Kam duk da ta hangosu amman ko kallo bai isheta ba ta dage kanta sama ta shige aji, sai ko gashi ya shigo class d'in yayi masu karatu saboda takaicin Dijen ko tambaya d'aya bai tambayeta ba, don ko ta d'aga hannu da nufin bada wata amsar sai ya basar da ita ya zab'i wata, haka yayi ta yi tun Dije bata damu ba har ta zo wuya itama ta daina d'aga hannun.
Ko da aka tashi ya sakata kamun kunne cikin rana tsoron ya daketa yasa ta kama kunnen, tun tana juriya har ta kai ta fara kuka tana fad'in jininta zai dawo ta kai zubowa zai yi k'asa idan taci gaba, ya ce ta koma yin kneel down ta d'aga kanta sama ta kalli rana hannuwanta duka biyu ya d'ora mata duwatsu masu dan girma yace kuma ta yarda suka fad'i jikinta ya gaya mata.
Dije tsawon minti sha biyar tana kallon ranar da taji azaba ta Kai mata karo ta fad'i sheme alamun aljanun sun zo, Safwan ya dauko bulala zai daketa ta yi saurin tashi tana fad'in
"Don girman ALLAH Malam ka yi hakuri yunwa nike ji ka bari in je gida"
Yace da ita suna nan har marece sai ta fad'i uban da yasa ta saka masa beraye a d'aki, Dije ta fara rantsuwar ba ita bace Mune ce amman duk da hakan sai da yayi mata bulala goma tare da gargadin ko kallonshi ta sake yi sai ya nakasata bale har ta sake shirya masa wata mugunta.
Dije ta dawo gida sai kumbure kumburen fuska take yi sai dai taki fad'in abunda yayi mata don kada Baffah yace bazata sake zuwa Makarantar ba.
Marece sakaliya ta tanadi kuka da toshshi ta k'ulle a leda, tana ta harkokinta har zuwa dare sannan ta sassada ta debi garwashin wuta cikin wani mataccen kwano ta rufe ta fita, Kai tsaye Gidan Maigarin ta nufa tamkar wacce aka aika tana shiga sashen d'akinsu Safwan d'in, ta ajiye kwanon ta fiddo tosshi da kukar da ta makale jikinta ta leka d'akin ta hangoshi yanata danne dannen wayarshi, ta dawo ta watsa tosshin da kukar ta yi saurin zuwa ta ajiye masa a bakin k'ofar ta janyo d'akin da sauri ta sake rufewa da wani k'aton iccen katako ta dantseshi ta tafiyarta"
Safwan kam ko da ya ji sautin rufe d'akin yayi saurin Kai kallonshi ga k'ofar, abun mamaki sai ga hayaki ya hango yana fitowa cikin kwanon mikewar da zai yi bala'in azabar da ke cikin hayakin ta fara kaiwa idonshi da hancinshi ziyara, aiko nan take ya fara atishaya ya yi ta dukan k'ofar akan a bud'e masa ba kowa wajen don Lawi ma yana wurin Maigarin sunata firarsu, aiko tun yana iya gane gabanshi har hayakin ya turnuke d'akin ko hannunshi baya gani ga kuma tsananin azabar da ke cikin hayakin, ko da Lawi da sauran Yan Gidan suka zo kawo masa agaji tuni Safwan ya galabaita sai sauke numfashin yake yi a wahalce yana nishi sama sama.