Sashe 75
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ai da kin tsaya ki nuna man banbancinki da ƴar aikin, to ai gara su basu shuka tsiyar da kika shuka a gidan mazajensu ba amman ga su a matsayin yan aikin, to ke in Baki yi a hankali ba yan aikin ma sai su fiki daraja a idon duniya, don ko wannan bankaɗa da kika janyo aka yi wa zuri'armu kawai hakkinmu ya isheki ballantana haƙƙin ɗaukar rai da kika so ki yi, in banda ALLAH ya tarfawa garinki nono da yanzu kin janyo muna bala'in da bamu san inda zamu jefa kanmu ba, don haka WALLAhi Ni banu wani ragi tsakanina da ke a gidan nan don yan aikin ma sai sun fiki daraja a wurina"
Har Zee ta ajiye kayan ta fito bata daina sababin faɗa ba, haka ta zaunar da ita tana ta tsara mata abunda zata yi a gidan tun daga safiya har dare, hankalin Zee bai ta shi ba har sai da ta ji wai har da wanki zata dinga yi kullum, wankin ma kuma na samarin ƴaƴanta da suka balaga wasu ma har suna zancen aure amman ace har da su zata dinga yiwa wanki,cike da ƙuncin zuciya ta kwana tare da cin alwashin muddin ta ji za'a kasheta WALLAhi dole ta tsere ta bar mata gidanta, don bazata zura ido aiki ya kassarata ba tunda daman cen ita ko undies ɗinta wanke mata ake yi, ba abunda ta iya in banda dafa indomie ko shi don watarana in an dafo mata tace bata yi mata daɗi ba, Mahaifiyarta tace ba mai sake dafo mata wata in tana so ta je ta dafa da kanta, to da hakan ne ta iya dafata saboda Daddynta ya ajiye mata masu aikin da suke yi mata duk abunda take so, to yanzu ga shi Baabaah Asabe zata sakata shiga uku.
Don kuwa tun da sassafe ta tadota daga baccin da ta koma na bayan asuba, ta fito ta kaita wajen tulin kayan wanke wanke ta ce ta fara idan ta gama ta je ta share gidan lungu da saƙo, cike da fargaba da tsananin tashin hankali ta ke ƙarewa ƙaton gidan kallo, tana nazarin ko rabinshi aka sakata sharewa ai an so kasheta bale duka, sai ga muryarta a saman kanta tana faɗin
"Zaki fara wanke wanken ko sai na fara sauke maki bulalata a jikinki?"
Zee jiki yana rawa ta fara harhaɗa kwanonin Baabaah Asaben ta ce da wata matashiyar ƴar aikinta ta nunnuna mata yanda zata yi, tana tsaye har aka nunawa Zee komi ta fara m wankewa tana hawaye sannan ta bar wajen, ta dawo falo ta zauna zuciyarta cike da jin daɗin yanda ta yi nasarar da Daddyn Zee ɗin ya gano kuskuren da ya tafka akan tarbiyyar ɗiyarshi, tare da jin daɗin amincewar da ya yi akan ta zo da ita hannunta ta zauna don bai san ƙudurinta akan Zee ɗin ba, da wataƙila ba zai yi saurin amincewa ba duk da kuma yasan ba zata yi mata ta daɗi ba, amman bai taba tunanin irin wannan azabtarwa zata yi mata ba.
Zee Kam haka aka yini ana aiki wankin samarin ma sai da ta yi sai dai su ma kansu ba da son ransu ba don dai Mahaifiyarsu ta yi masu jan kunne da kashedi sosai akan duk abunda suka ga ta saka Zee iyakacinsu Ido, Dole Suka zura ido suna kallon yanda take ta yi masu wankin, cikin ƙankanin lokaci hannunta ya yi ja ya saluɓe aiko ta fara yarfa hannu tana kuka, ganin haka yasa aka canza mata wani aikin ko da dare ya yi ta kwanta ko'ina nata ciwo yake yi, da ciwon jiki ta kwana kan tabarma tana haki tana juye juyen wahala.
Sorry Zee😢 Wai ko dai in zo in gudu dake ne🙊 gidan mum Irfaan ko gidan Daughter Rufaida ko wurin ƙanwata Asiya? Ki yi shawarar inda kike son zuwa kafin in dawo🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🤣
Akafta😊
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Don Allah masu neman book ɗin Ƙarangiya daga farko ku yi haƙuri idan an kammala za ku sameshi a complete ɗinshi, plss ku yi haƙuri kunji😢saboda anyi nisa sosai kuma bana son kuna tambaya baku samu ba😆*
*Lamba 68*
Daren ranar Dije da Inna sai hira suke ta zubawa, don ita Hansai tun da ta ji cikinta ya ɗauka ta baje abunta sai sharar baccinta take yi ita da yaronta, ganin dare ya miƙa ne Inna ta ce da Dijen ta tashi ta je wurin Mijinta, Dije tana zumɓuro baki ta ce
"Anan zan kwana Inna mu yi ta firarmu Ni da ke Inna, sabida ALLAH yaushe rabon da mu ga juna an daɗe fa? Ni dai don girman ALLAH Inna ki barni in kwana abuna anan ɗakin"
Ta ƙare maganar tare da zubowar wasu ƙwallah, Inna ta gyara ta yi kwanciyarta tana faɗin
"To Ni dai bacci nike ji idan ke baki gaji da firar ba ki ci gaba ai akwai aljanun dare suna saurarenki zasu tayaki yin firar"
Dije ta zaro ido tuno abunda ya taɓa faruwa a school ta yi saurin kwanciya bayanta ta ƙudundune tana faɗin
"Inna ki yi man addu'a kar su kamani don ALLAH"
Inna ta miƙe zaune cike da mamaki ta ce "zaki ta shi ki je wurin Mijinki ko ko so kike yi ya ɗaukemu waɗanda basu san abunda suke yi ba?"
Dije ta miƙe tana kallon ƙofa tace
"To mu je ki rakani WALLAHI tsoro nike ji"
Inna ta riƙe baki cike da mamaki ta ce
"Tunda kike gidan baki ji tsoro ba sai yanzu da kika ga mun zo ko? To ya yi insha ALLAHu gobe tun da sassafe mu zamu bar maki gidanki tunda so kike yi ya ɗaukemu mutanen banza"
Dije ta miƙe ta fito Inna ta rufo ɗakin zuciyarta cike da nauyin kada Safwan ɗin ya ga sun riƙeta, aikuwa Dije cikin sanɗa ta ke tafiya tana waige sai jin ta yi anyi caraf da ita, ba shiri ta yage baki da nufin fasa ƙara taji bakin Malaminta cikin nata, gano shine yasa ta ƙara ruƙunƙumeshi jikinshi tana faɗin
"Mu je ɗaki tsoro nike ji"
Cike da jin daɗi ya sake manneta jikinshi suka yi ɗakinshi, ganin da gaske tsoron take ji yasa ya fara tambayarta abunda ya tsoratata, cikin murya ƙasa ƙasa ta yi masa bayanin yanda suka yi da Inna, cikin dariya ya ce
"ALLAH ya biya Inna da gidan Aljannah don Ni ta kyauta man, saboda tun ɗazu da na dawo wurinsu Baffah nike ta juye juye Ni kaɗai akan gado, dole na fito falo na zauna ina kallo nan ma na ji ba daɗi na kashe ina tunanin yanda zan yi in ce ki zo, ashe Inna tasan ƙishina shiyasa ta koro man ke waje"
Dije ta tureshi cikin fushi ta ce "tunda haɗe man kai kuke son yi ai ku je ni ma gobe wurin Hajiyarmu zan kwana "
Safwan ya janyota jikinshi ya ce "ai Hajiyarmu ma ba zata so ki bar Mijinki shi kaɗai ba yana kewa ba"
Haka ya hilaceta ya gwangwaje abunshi tare da sassafta murya wurin sambatun da ya saba, don gudun ya tafka abun kunya gaban surukai.
Tun da Sassafe aka kammala masu komi na breakfast ɗinsu tare da taimakon wasu yan aiki biyu da Hajiyar ta ƙaro masu, bayan sun karya ne aka sake wata sabuwar gaisawa sannan Safwan ya kwaahesu zuwa gidansu su gayar da Hajiyar, tarba ta mutumci Hajiya Mama ta yi masu fuska cike da fara'a tamkar cewa da man cen ƴan'uwanta ne, Inna da Baffah suka yi godiya sosai akan yanda take kulawa da Dije tamkar itace ɗiyarta ba Safwan ba, Inna da Hansai da Dijen sun daɗe gidan tare da Hajiya Mama sannan Safwan ya dawo da su Baffah da ya je kaisu yawon ganin gari, marece sakaliya ya ɗaukesu ya kaisu gidan Mijin Surayyy, inda itama ta yi masu tarba mai kyau tamkar kar su rabu saboda kirkin Surry ba ƙaramin burge su Inna yake yi ba, sai gaf da magriba suka dawo gidan inda suka taradda an haɗa masu abincin dare mai rai da lafiya, tuwon farar shinkafa da miyar agusi ta ji zuƙa zuƙan namomi tare da lafiyayye ferfesun kajin turawa masu manyan tsokoki, bayan sun ci abincin ne aka koma yin firar bankwana saboda tun da sassafe zasu juyawa inda suka fito, tun cikin daren Safwan ya tanadar masu duk abunda zai ba su ya basu, Hajiya Mama ma da nata kalar tsarabar Surayya ma da tata, haka suka yi ta godiya kamar ba gobe, don kuwa su kansu sun san ba ƙaramin arziƙi suka yi ba,saboda bancin sutura kuɗi tsabarsu dubu ɗari Safwan ya baiwa Baffah, Inna dubu Hamsin Usmanu da talatin Hansai ashirin yaronta goma, bayan suturar da aka cikasu da ita da turaruka da sabulai kala kala, yaron Hansai kanshi ledar kayanshi daban aka siyo mashi masu ɗan karen kyau.
Tun cikin daren Dukansu suka saka Dije tsakiya suna yi mata nasihohi tare da jan kunne akan ta ninka wa mijinta da Mahaifiyarshi biyayyar da take yi masu, haka ma ƴan'uwaanshi ta riƙesu tamkar yanda zata riƙe nata, in ma da hali su fi natan don kawai ta sami zaman lafiya da kwanciyar hankali a gidan aurenta, anan ne take sanar da su gumurzun da aka yi da Zee akan kashe sun da ta so yi tare da ƙudurinta da ta yanke akan muddin Zee ta dawo to ita zata bar mata gidan, cikin fushi Usmanu ya ce
"WALLAHI kika kuskura kika bar wannan gidan akan baƙin shirmenki sai na saki jiki na lakaɗa maki shegen duka"
Inna tana harararta ta ce "to bari ki ji da kyau muddin kika taka ƙafarki kika bar gidan nan bada izinin Mijinki ba to ki sani ban yafe maki ba"
Baffah ya yafito Dijen ta zo gabanshi ta zauna tana zimɓoro baki yana dariya ya ce
"Shin Ina Dijengalata?? "
Hawaye suka zubo mata ta ce
"Gani Baffah".
Har Zee ta ajiye kayan ta fito bata daina sababin faɗa ba, haka ta zaunar da ita tana ta tsara mata abunda zata yi a gidan tun daga safiya har dare, hankalin Zee bai ta shi ba har sai da ta ji wai har da wanki zata dinga yi kullum, wankin ma kuma na samarin ƴaƴanta da suka balaga wasu ma har suna zancen aure amman ace har da su zata dinga yiwa wanki,cike da ƙuncin zuciya ta kwana tare da cin alwashin muddin ta ji za'a kasheta WALLAhi dole ta tsere ta bar mata gidanta, don bazata zura ido aiki ya kassarata ba tunda daman cen ita ko undies ɗinta wanke mata ake yi, ba abunda ta iya in banda dafa indomie ko shi don watarana in an dafo mata tace bata yi mata daɗi ba, Mahaifiyarta tace ba mai sake dafo mata wata in tana so ta je ta dafa da kanta, to da hakan ne ta iya dafata saboda Daddynta ya ajiye mata masu aikin da suke yi mata duk abunda take so, to yanzu ga shi Baabaah Asabe zata sakata shiga uku.
Don kuwa tun da sassafe ta tadota daga baccin da ta koma na bayan asuba, ta fito ta kaita wajen tulin kayan wanke wanke ta ce ta fara idan ta gama ta je ta share gidan lungu da saƙo, cike da fargaba da tsananin tashin hankali ta ke ƙarewa ƙaton gidan kallo, tana nazarin ko rabinshi aka sakata sharewa ai an so kasheta bale duka, sai ga muryarta a saman kanta tana faɗin
"Zaki fara wanke wanken ko sai na fara sauke maki bulalata a jikinki?"
Zee jiki yana rawa ta fara harhaɗa kwanonin Baabaah Asaben ta ce da wata matashiyar ƴar aikinta ta nunnuna mata yanda zata yi, tana tsaye har aka nunawa Zee komi ta fara m wankewa tana hawaye sannan ta bar wajen, ta dawo falo ta zauna zuciyarta cike da jin daɗin yanda ta yi nasarar da Daddyn Zee ɗin ya gano kuskuren da ya tafka akan tarbiyyar ɗiyarshi, tare da jin daɗin amincewar da ya yi akan ta zo da ita hannunta ta zauna don bai san ƙudurinta akan Zee ɗin ba, da wataƙila ba zai yi saurin amincewa ba duk da kuma yasan ba zata yi mata ta daɗi ba, amman bai taba tunanin irin wannan azabtarwa zata yi mata ba.
Zee Kam haka aka yini ana aiki wankin samarin ma sai da ta yi sai dai su ma kansu ba da son ransu ba don dai Mahaifiyarsu ta yi masu jan kunne da kashedi sosai akan duk abunda suka ga ta saka Zee iyakacinsu Ido, Dole Suka zura ido suna kallon yanda take ta yi masu wankin, cikin ƙankanin lokaci hannunta ya yi ja ya saluɓe aiko ta fara yarfa hannu tana kuka, ganin haka yasa aka canza mata wani aikin ko da dare ya yi ta kwanta ko'ina nata ciwo yake yi, da ciwon jiki ta kwana kan tabarma tana haki tana juye juyen wahala.
Sorry Zee😢 Wai ko dai in zo in gudu dake ne🙊 gidan mum Irfaan ko gidan Daughter Rufaida ko wurin ƙanwata Asiya? Ki yi shawarar inda kike son zuwa kafin in dawo🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🤣
Akafta😊
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Don Allah masu neman book ɗin Ƙarangiya daga farko ku yi haƙuri idan an kammala za ku sameshi a complete ɗinshi, plss ku yi haƙuri kunji😢saboda anyi nisa sosai kuma bana son kuna tambaya baku samu ba😆*
*Lamba 68*
Daren ranar Dije da Inna sai hira suke ta zubawa, don ita Hansai tun da ta ji cikinta ya ɗauka ta baje abunta sai sharar baccinta take yi ita da yaronta, ganin dare ya miƙa ne Inna ta ce da Dijen ta tashi ta je wurin Mijinta, Dije tana zumɓuro baki ta ce
"Anan zan kwana Inna mu yi ta firarmu Ni da ke Inna, sabida ALLAH yaushe rabon da mu ga juna an daɗe fa? Ni dai don girman ALLAH Inna ki barni in kwana abuna anan ɗakin"
Ta ƙare maganar tare da zubowar wasu ƙwallah, Inna ta gyara ta yi kwanciyarta tana faɗin
"To Ni dai bacci nike ji idan ke baki gaji da firar ba ki ci gaba ai akwai aljanun dare suna saurarenki zasu tayaki yin firar"
Dije ta zaro ido tuno abunda ya taɓa faruwa a school ta yi saurin kwanciya bayanta ta ƙudundune tana faɗin
"Inna ki yi man addu'a kar su kamani don ALLAH"
Inna ta miƙe zaune cike da mamaki ta ce "zaki ta shi ki je wurin Mijinki ko ko so kike yi ya ɗaukemu waɗanda basu san abunda suke yi ba?"
Dije ta miƙe tana kallon ƙofa tace
"To mu je ki rakani WALLAHI tsoro nike ji"
Inna ta riƙe baki cike da mamaki ta ce
"Tunda kike gidan baki ji tsoro ba sai yanzu da kika ga mun zo ko? To ya yi insha ALLAHu gobe tun da sassafe mu zamu bar maki gidanki tunda so kike yi ya ɗaukemu mutanen banza"
Dije ta miƙe ta fito Inna ta rufo ɗakin zuciyarta cike da nauyin kada Safwan ɗin ya ga sun riƙeta, aikuwa Dije cikin sanɗa ta ke tafiya tana waige sai jin ta yi anyi caraf da ita, ba shiri ta yage baki da nufin fasa ƙara taji bakin Malaminta cikin nata, gano shine yasa ta ƙara ruƙunƙumeshi jikinshi tana faɗin
"Mu je ɗaki tsoro nike ji"
Cike da jin daɗi ya sake manneta jikinshi suka yi ɗakinshi, ganin da gaske tsoron take ji yasa ya fara tambayarta abunda ya tsoratata, cikin murya ƙasa ƙasa ta yi masa bayanin yanda suka yi da Inna, cikin dariya ya ce
"ALLAH ya biya Inna da gidan Aljannah don Ni ta kyauta man, saboda tun ɗazu da na dawo wurinsu Baffah nike ta juye juye Ni kaɗai akan gado, dole na fito falo na zauna ina kallo nan ma na ji ba daɗi na kashe ina tunanin yanda zan yi in ce ki zo, ashe Inna tasan ƙishina shiyasa ta koro man ke waje"
Dije ta tureshi cikin fushi ta ce "tunda haɗe man kai kuke son yi ai ku je ni ma gobe wurin Hajiyarmu zan kwana "
Safwan ya janyota jikinshi ya ce "ai Hajiyarmu ma ba zata so ki bar Mijinki shi kaɗai ba yana kewa ba"
Haka ya hilaceta ya gwangwaje abunshi tare da sassafta murya wurin sambatun da ya saba, don gudun ya tafka abun kunya gaban surukai.
Tun da Sassafe aka kammala masu komi na breakfast ɗinsu tare da taimakon wasu yan aiki biyu da Hajiyar ta ƙaro masu, bayan sun karya ne aka sake wata sabuwar gaisawa sannan Safwan ya kwaahesu zuwa gidansu su gayar da Hajiyar, tarba ta mutumci Hajiya Mama ta yi masu fuska cike da fara'a tamkar cewa da man cen ƴan'uwanta ne, Inna da Baffah suka yi godiya sosai akan yanda take kulawa da Dije tamkar itace ɗiyarta ba Safwan ba, Inna da Hansai da Dijen sun daɗe gidan tare da Hajiya Mama sannan Safwan ya dawo da su Baffah da ya je kaisu yawon ganin gari, marece sakaliya ya ɗaukesu ya kaisu gidan Mijin Surayyy, inda itama ta yi masu tarba mai kyau tamkar kar su rabu saboda kirkin Surry ba ƙaramin burge su Inna yake yi ba, sai gaf da magriba suka dawo gidan inda suka taradda an haɗa masu abincin dare mai rai da lafiya, tuwon farar shinkafa da miyar agusi ta ji zuƙa zuƙan namomi tare da lafiyayye ferfesun kajin turawa masu manyan tsokoki, bayan sun ci abincin ne aka koma yin firar bankwana saboda tun da sassafe zasu juyawa inda suka fito, tun cikin daren Safwan ya tanadar masu duk abunda zai ba su ya basu, Hajiya Mama ma da nata kalar tsarabar Surayya ma da tata, haka suka yi ta godiya kamar ba gobe, don kuwa su kansu sun san ba ƙaramin arziƙi suka yi ba,saboda bancin sutura kuɗi tsabarsu dubu ɗari Safwan ya baiwa Baffah, Inna dubu Hamsin Usmanu da talatin Hansai ashirin yaronta goma, bayan suturar da aka cikasu da ita da turaruka da sabulai kala kala, yaron Hansai kanshi ledar kayanshi daban aka siyo mashi masu ɗan karen kyau.
Tun cikin daren Dukansu suka saka Dije tsakiya suna yi mata nasihohi tare da jan kunne akan ta ninka wa mijinta da Mahaifiyarshi biyayyar da take yi masu, haka ma ƴan'uwaanshi ta riƙesu tamkar yanda zata riƙe nata, in ma da hali su fi natan don kawai ta sami zaman lafiya da kwanciyar hankali a gidan aurenta, anan ne take sanar da su gumurzun da aka yi da Zee akan kashe sun da ta so yi tare da ƙudurinta da ta yanke akan muddin Zee ta dawo to ita zata bar mata gidan, cikin fushi Usmanu ya ce
"WALLAHI kika kuskura kika bar wannan gidan akan baƙin shirmenki sai na saki jiki na lakaɗa maki shegen duka"
Inna tana harararta ta ce "to bari ki ji da kyau muddin kika taka ƙafarki kika bar gidan nan bada izinin Mijinki ba to ki sani ban yafe maki ba"
Baffah ya yafito Dijen ta zo gabanshi ta zauna tana zimɓoro baki yana dariya ya ce
"Shin Ina Dijengalata?? "
Hawaye suka zubo mata ta ce
"Gani Baffah".