Sashe 82
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Lanti da ta yi tagumi ta ce "ai Ni bance komi ba Dije don WALLAhi har zaucewa na so yi lokacin da Usmanu ya kawo man su har gida ya ce in jiki wai mu ja jari, haka naga abun kamar almara WALLAHI"
Dije cike da mamaki ta kalli Hansai saboda neman ƙarin bayani don ita bata ma san kan zancen ba, kuma bata da masaniyar komi akai, Hansai ta yi dariya ta ce
"Habibynki ne ya turowa wani saƙon ya baiwa Baban yaron nan ya kawo muna ya ce in ji ki abamu mu abokanki"
Dije ta ji wata ƙwallah ta sauko mata cike da jin ƙara ƙaunar mijin nata, saboda ita ko kaɗan bai sanar da ita anyi hakan ba sai yanzu da ta ji a bakunansu, Mune ta sauke ajiyar zuciya ta ce
"Dole ki yi kuka don farin ciki ya yi a rayuwa, ALLAH ya ƙara buɗe maku hanyoyin samu ta ko'ina ko don mu na kusa da ku mu amfana"
Gaba ɗaya aka ce "Ameen"
Dije ta share hawayenta tana dariya ta ce "Mune naga yanzu kin rage surutu mi ye sirrin halan?"
Mune ta yi dariya ta ce
"Hmmmmmmmm ai ke dai in ana SALLAH ba'a magana, don kuwa akan halin har sakina ma Ummaru ya yi na dawo gida, saboda wani faɗa da na haɗa tsakanin matan yayan Ummaru, duk da a zahiri Ni iya gaskiyata ce na faɗi, amman duk wanda ya ji zai ɗauka cewa munafucci ne"
Lanti tana dariya ta ce
"To da gaskiya ta bayyana ai ALLAH ya wankeki ko? Kuma ki godewa ALLAH tunda har hakan ya zamo sanadin shiriyarki kika daina yawan faɗi ba'a tambayeki ba"
Dije ta kalli Jummala ta ce "me ya faru halan"
Ladiyo ta fashe da dariya ta ce "ki tambayi ƴar gidan taki mana sai ta fi iya bada labarin yanda ake so"
Mune ta cire taguminta ta ce "Matan yayan Ummaru ne suke ta faɗan kishi kullum a tsakaninsu, shine ranar na ji ɗaya tana faɗawa wata abokiyarta cewa zata sakawa abokiyar zaman shinkafar ɓera a abinci ta mutu, to shine Ni kuma na ji tsoro na je na sanarwa wadda ake so akashen, aiko ta sanarwa da mijinsu sai ko ga shi wadda ta ci alwashin ta kawo mata abinci ta ce bazata ci ita sai ta ci ta ƙi ci, daman an shirya hakan mijin ma ya kafe akan dole sai taci abincin ta ƙi ci, rigima ta rikice gida ya cika da mutane ƙarshe dai abu har gaban Maigari, aka baiwa kyanwa ta ci bata yi komi ba itama aka tilastata dole sai da ta ci, abun mamaki ba abunda ta yi shine aka fara kuka ta ce daman na ce sai na ƙalla mata sharri, nan mutane suka yi ta tsine mani ana cewa da ni daman cen Ni Munafuka ce, gashi yanzu zan haɗa rigima don kawai na tsani ɗayar, ke a taƙaice dai akan hakan Ummaru ya sakeni na koma gida sai daga baya da gaskiya ta fito aka gano makirci ne ta ƙulla ashe ta ji lokacin da nike faɗawa waccen ɗin, shine ta liƙaman sharri sai cikin ikon ALLAH bayan bana gidan faɗa ya haɗasu ta ɗauko taɓarya ta ce sai ta kashe kishiyar, da komi ya lafa aka gano gaskiya don ta yi iƙirari da bakinta akan cewa itace ta faɗa na ji a lokacin, shine fa ya dawo da ni gidanshi bayan an ja kunnena da faɗi ba'a tambayeka ba, to tun daga haka na kame bakina ba ruwana da faɗin abunda bai shafeni ba, kinji mafarin shiriyata, yanzu ko a gabana aka yi abu WALLAhi ba abunda ya dameni bale in fad'a"
Dije tana dariya ta ce "Alhmdllh ƙawata baki dadi wallahi yanzu ki ce ko a gabanki mu yi kashinmu ba zaki faɗa ba? "
Mune tana dariya ta ce "tabbas Ni ce ma zan sakayaku in yi maku labule don kar a ganku"
Gaba ɗaya aka saka dariya, haka suka yi ta tuno baya suna mayar da zance suna dariya, sun ɗauki lokaci sunata firarsu har dare ya raba sannan suka je suka kwanta.
Tunda sassafe suka yi sallama da kowa suka kama hanyar zuwa inda suka fito, da nufin sati yana zagayowa itama zata bi su ta je wankan gida a garinsu .
Haka ko aka yi Satin yana zuwa Fiddo da Zee da wata dattijuwaar da zata dinga taimakonta suka rakata zuwa garinsu ta jirgin sama da zai rage masu hanya zuwa sannan su ci gaba da motar, saboda kawai Yaron Safwan da ko ƙuda baya son su hau kanshi bale wahalar doguwar tafiya irin wannan.
Ko da Jirgin ya saukesu motar tana jiransu saboda tuni ta taso sannan su daga baya suka biyo hanya, kasancewar an samu ci gaba sosai a babban birninsu Dijen har cikin ƙauyensu, shi yasa basu sha wata wahala ba suka isa ƙauyen ƙiriu garinsu Dijen Baffah.
Mamaki bai kashe Dijen ba har sai da suka isa ƙofar gidan nasu taga kamar ma ba nan ne ba, don kuwa gida ne na alfarma Safwan ya ƙyanƙyara masu saboda kawai ya basu tukuicin faranta masan da ƴarsu take yi a kullum, ga kuma hasken solar ta ko'ina tun daga ƙofar gidan har cikin gidan fes yake masha ALLAH tare da sabon fentiin da ya ƙara fito da kyawon gidan.
Baki sake Dije take kallon gidan don ko kula da masu yi mata sannu da zuwa bata yi ba har suka isa cikin gidan ita da su Zee, Baki bud'e ta ƙura wa inna ido cikin shiga mai kyau ta buɗe wata doguwar freezer tana fito da wasu gorunan ruwa tana saka wasu, bakinta washe ta ke faɗin
"Sannunku da zuwa mutanen Yola sannu da zuwa"
Fiddo kanta mamaki abun ya bata saboda tasan yanda gidan ya ke acen baya, Zee kam wasar bakinta kawai ta ke yi har suka shiga falon Inna da ya ƙawatu da kujeru irin na ƴan gayu, Suka zazzauna Dije kam ƙurya ta shige saboda kukan da ya zo mata kuma ba zata iya danneshi ba, haka ma bata son ta yi shi a gaban Zee ta fahimci wani abu.
Inna ta fara jera masu abinci kala kala da ruwa da lemuka tana faɗin "ku sha ruwa kun kwaso hanya kam"
Fiddo ta karɓi Sayyid hannun Zee ta ce
"Inna ba zan baki yarona ba tunda har baki yi murna da zuwanshi ba"
Inna ta rufe Baki tana dariya ta ce "ku yi ta kaya Ni mai Malam me zan yi da wannan mijin cikin zane komai sai anyi masa?"
ZEE ta ɗauki ruwa tana tsiyayawa a kofi tace "ai dai inna shi sabon miji daban yake tsoho, idan kuma kika bari ya yi fushi ya ce ya fasa kuma shikenan sai mu nemo masa wasu matan"
Shigowar Hansai cikin tsantsar farin ciki yasa Inna Bata Sami damar mayar masu da amsa ba, Hansai ta karɓe yaron tana ihun faɗin
"Wayyo daɗi ɗanmu ya zama ɗan turawa Inna duba ki gani"
Inna ta ƙarɓeshi da bisimillah tana faɗin
"Waɗannan uwayen dai akwai kuri, to ALLAH yasa kafin ku haifu wasu sun rigaku haifuwar"
Ta ƙare maganar tare da zaunawa tana gyara masa hannun rigarshi ta kayan sanyin da ke jikinshi ya sauko ƙasa ya rufe tafinshi, Zee tana dariya ta ce
"Mu dai na mu muka sani Inna don zamu iya bugun ƙirji mu ce namu ya fi na kowa"
Inna tana dariya ta ɗagashi sama tana yin miƙa yana wani botsarewa alamun ya ji daɗin hakan, Inna ta kalli Fiddo ta ce
"Ku ne da yaron amman baku iya renon ba, to ku biya kawai a tayaku renonshi kawai"
Dattijuwaar da suka zo da ita tana dariya ta ce "Mutum da Matarshi har sai an biya? To a biyosu bashi idan ya girma sai ya biya da kanshi"
Sai ga sallamar Baffah ya shigo Dije da ke ƙuryar ɗaki tana kuka Hansai na lallashinta Muryar Baffah ta sa ta fito da saurinta ta taryeshi cike da jin daɗin ganinshi ta durƙusa tana gayar da shi, cike tsantsan farin ciki ya ke amsawa sannan ya tsaya bakin ƙofar falon ya gaisa da su Zee, sannan ya yi masu sannu da zuwa tare da tambayar mutanen gida, bayan sun ƙare gaisawar ne ya yi ɗakinshi Dije ta biyoshi zuciyarta cike tsantsan farin cikin ganin yanda yayi ƙiba hankalinshi a kwance, ta zauna tana wasa da yan yatsunta suka sake gaisawa a tsanake sannan ya kalleta yana ƴar dariya ya ce
"Wa ya taɓa man Dijeta daga zuwanta?"
Dije ta share hawayenta tana dariya ta ce "naga gida ya yi kyau Baffah ashe haka ka gyara gidan?"
Yana dariyarsu ta manya ya ce "na gyara ko aka gyara man? ki yi haƙuri shi ya ce kada a sanar da ke sai in kin zo kin gani da idonki, don yanzu haka bamu fi wata uku da tarewa ba, saboda cikin ƴan watanni aka yi komi aka gama, mutane da yawa sunyi mamakin yanda aka kammala ginin cikin lokaci kaɗan, Alhmdllh kam mun godewa ALLAH da ya had'amu da mutanen kirki masu mutunci da sanin Yakamata, da ace duk sauran mutane haka su ke da ina tabbatar maki mabuƙata ba zasu taɓa yin kuka ba, to matsalar da aka samu irinsu ƙaɗan ne a cikin al'umma"
Dije ta share hawayenta ta ce "Ni ban ma san mi zan ce ba Baffah saboda tun da naga wannan gyaran nasab aikinshi ne, haka fa ya aikowa da su Ladiyo kuɗi Ni banma sani ba ya ce in jini su ja jari"
Dije cike da mamaki ta kalli Hansai saboda neman ƙarin bayani don ita bata ma san kan zancen ba, kuma bata da masaniyar komi akai, Hansai ta yi dariya ta ce
"Habibynki ne ya turowa wani saƙon ya baiwa Baban yaron nan ya kawo muna ya ce in ji ki abamu mu abokanki"
Dije ta ji wata ƙwallah ta sauko mata cike da jin ƙara ƙaunar mijin nata, saboda ita ko kaɗan bai sanar da ita anyi hakan ba sai yanzu da ta ji a bakunansu, Mune ta sauke ajiyar zuciya ta ce
"Dole ki yi kuka don farin ciki ya yi a rayuwa, ALLAH ya ƙara buɗe maku hanyoyin samu ta ko'ina ko don mu na kusa da ku mu amfana"
Gaba ɗaya aka ce "Ameen"
Dije ta share hawayenta tana dariya ta ce "Mune naga yanzu kin rage surutu mi ye sirrin halan?"
Mune ta yi dariya ta ce
"Hmmmmmmmm ai ke dai in ana SALLAH ba'a magana, don kuwa akan halin har sakina ma Ummaru ya yi na dawo gida, saboda wani faɗa da na haɗa tsakanin matan yayan Ummaru, duk da a zahiri Ni iya gaskiyata ce na faɗi, amman duk wanda ya ji zai ɗauka cewa munafucci ne"
Lanti tana dariya ta ce
"To da gaskiya ta bayyana ai ALLAH ya wankeki ko? Kuma ki godewa ALLAH tunda har hakan ya zamo sanadin shiriyarki kika daina yawan faɗi ba'a tambayeki ba"
Dije ta kalli Jummala ta ce "me ya faru halan"
Ladiyo ta fashe da dariya ta ce "ki tambayi ƴar gidan taki mana sai ta fi iya bada labarin yanda ake so"
Mune ta cire taguminta ta ce "Matan yayan Ummaru ne suke ta faɗan kishi kullum a tsakaninsu, shine ranar na ji ɗaya tana faɗawa wata abokiyarta cewa zata sakawa abokiyar zaman shinkafar ɓera a abinci ta mutu, to shine Ni kuma na ji tsoro na je na sanarwa wadda ake so akashen, aiko ta sanarwa da mijinsu sai ko ga shi wadda ta ci alwashin ta kawo mata abinci ta ce bazata ci ita sai ta ci ta ƙi ci, daman an shirya hakan mijin ma ya kafe akan dole sai taci abincin ta ƙi ci, rigima ta rikice gida ya cika da mutane ƙarshe dai abu har gaban Maigari, aka baiwa kyanwa ta ci bata yi komi ba itama aka tilastata dole sai da ta ci, abun mamaki ba abunda ta yi shine aka fara kuka ta ce daman na ce sai na ƙalla mata sharri, nan mutane suka yi ta tsine mani ana cewa da ni daman cen Ni Munafuka ce, gashi yanzu zan haɗa rigima don kawai na tsani ɗayar, ke a taƙaice dai akan hakan Ummaru ya sakeni na koma gida sai daga baya da gaskiya ta fito aka gano makirci ne ta ƙulla ashe ta ji lokacin da nike faɗawa waccen ɗin, shine ta liƙaman sharri sai cikin ikon ALLAH bayan bana gidan faɗa ya haɗasu ta ɗauko taɓarya ta ce sai ta kashe kishiyar, da komi ya lafa aka gano gaskiya don ta yi iƙirari da bakinta akan cewa itace ta faɗa na ji a lokacin, shine fa ya dawo da ni gidanshi bayan an ja kunnena da faɗi ba'a tambayeka ba, to tun daga haka na kame bakina ba ruwana da faɗin abunda bai shafeni ba, kinji mafarin shiriyata, yanzu ko a gabana aka yi abu WALLAhi ba abunda ya dameni bale in fad'a"
Dije tana dariya ta ce "Alhmdllh ƙawata baki dadi wallahi yanzu ki ce ko a gabanki mu yi kashinmu ba zaki faɗa ba? "
Mune tana dariya ta ce "tabbas Ni ce ma zan sakayaku in yi maku labule don kar a ganku"
Gaba ɗaya aka saka dariya, haka suka yi ta tuno baya suna mayar da zance suna dariya, sun ɗauki lokaci sunata firarsu har dare ya raba sannan suka je suka kwanta.
Tunda sassafe suka yi sallama da kowa suka kama hanyar zuwa inda suka fito, da nufin sati yana zagayowa itama zata bi su ta je wankan gida a garinsu .
Haka ko aka yi Satin yana zuwa Fiddo da Zee da wata dattijuwaar da zata dinga taimakonta suka rakata zuwa garinsu ta jirgin sama da zai rage masu hanya zuwa sannan su ci gaba da motar, saboda kawai Yaron Safwan da ko ƙuda baya son su hau kanshi bale wahalar doguwar tafiya irin wannan.
Ko da Jirgin ya saukesu motar tana jiransu saboda tuni ta taso sannan su daga baya suka biyo hanya, kasancewar an samu ci gaba sosai a babban birninsu Dijen har cikin ƙauyensu, shi yasa basu sha wata wahala ba suka isa ƙauyen ƙiriu garinsu Dijen Baffah.
Mamaki bai kashe Dijen ba har sai da suka isa ƙofar gidan nasu taga kamar ma ba nan ne ba, don kuwa gida ne na alfarma Safwan ya ƙyanƙyara masu saboda kawai ya basu tukuicin faranta masan da ƴarsu take yi a kullum, ga kuma hasken solar ta ko'ina tun daga ƙofar gidan har cikin gidan fes yake masha ALLAH tare da sabon fentiin da ya ƙara fito da kyawon gidan.
Baki sake Dije take kallon gidan don ko kula da masu yi mata sannu da zuwa bata yi ba har suka isa cikin gidan ita da su Zee, Baki bud'e ta ƙura wa inna ido cikin shiga mai kyau ta buɗe wata doguwar freezer tana fito da wasu gorunan ruwa tana saka wasu, bakinta washe ta ke faɗin
"Sannunku da zuwa mutanen Yola sannu da zuwa"
Fiddo kanta mamaki abun ya bata saboda tasan yanda gidan ya ke acen baya, Zee kam wasar bakinta kawai ta ke yi har suka shiga falon Inna da ya ƙawatu da kujeru irin na ƴan gayu, Suka zazzauna Dije kam ƙurya ta shige saboda kukan da ya zo mata kuma ba zata iya danneshi ba, haka ma bata son ta yi shi a gaban Zee ta fahimci wani abu.
Inna ta fara jera masu abinci kala kala da ruwa da lemuka tana faɗin "ku sha ruwa kun kwaso hanya kam"
Fiddo ta karɓi Sayyid hannun Zee ta ce
"Inna ba zan baki yarona ba tunda har baki yi murna da zuwanshi ba"
Inna ta rufe Baki tana dariya ta ce "ku yi ta kaya Ni mai Malam me zan yi da wannan mijin cikin zane komai sai anyi masa?"
ZEE ta ɗauki ruwa tana tsiyayawa a kofi tace "ai dai inna shi sabon miji daban yake tsoho, idan kuma kika bari ya yi fushi ya ce ya fasa kuma shikenan sai mu nemo masa wasu matan"
Shigowar Hansai cikin tsantsar farin ciki yasa Inna Bata Sami damar mayar masu da amsa ba, Hansai ta karɓe yaron tana ihun faɗin
"Wayyo daɗi ɗanmu ya zama ɗan turawa Inna duba ki gani"
Inna ta ƙarɓeshi da bisimillah tana faɗin
"Waɗannan uwayen dai akwai kuri, to ALLAH yasa kafin ku haifu wasu sun rigaku haifuwar"
Ta ƙare maganar tare da zaunawa tana gyara masa hannun rigarshi ta kayan sanyin da ke jikinshi ya sauko ƙasa ya rufe tafinshi, Zee tana dariya ta ce
"Mu dai na mu muka sani Inna don zamu iya bugun ƙirji mu ce namu ya fi na kowa"
Inna tana dariya ta ɗagashi sama tana yin miƙa yana wani botsarewa alamun ya ji daɗin hakan, Inna ta kalli Fiddo ta ce
"Ku ne da yaron amman baku iya renon ba, to ku biya kawai a tayaku renonshi kawai"
Dattijuwaar da suka zo da ita tana dariya ta ce "Mutum da Matarshi har sai an biya? To a biyosu bashi idan ya girma sai ya biya da kanshi"
Sai ga sallamar Baffah ya shigo Dije da ke ƙuryar ɗaki tana kuka Hansai na lallashinta Muryar Baffah ta sa ta fito da saurinta ta taryeshi cike da jin daɗin ganinshi ta durƙusa tana gayar da shi, cike tsantsan farin ciki ya ke amsawa sannan ya tsaya bakin ƙofar falon ya gaisa da su Zee, sannan ya yi masu sannu da zuwa tare da tambayar mutanen gida, bayan sun ƙare gaisawar ne ya yi ɗakinshi Dije ta biyoshi zuciyarta cike tsantsan farin cikin ganin yanda yayi ƙiba hankalinshi a kwance, ta zauna tana wasa da yan yatsunta suka sake gaisawa a tsanake sannan ya kalleta yana ƴar dariya ya ce
"Wa ya taɓa man Dijeta daga zuwanta?"
Dije ta share hawayenta tana dariya ta ce "naga gida ya yi kyau Baffah ashe haka ka gyara gidan?"
Yana dariyarsu ta manya ya ce "na gyara ko aka gyara man? ki yi haƙuri shi ya ce kada a sanar da ke sai in kin zo kin gani da idonki, don yanzu haka bamu fi wata uku da tarewa ba, saboda cikin ƴan watanni aka yi komi aka gama, mutane da yawa sunyi mamakin yanda aka kammala ginin cikin lokaci kaɗan, Alhmdllh kam mun godewa ALLAH da ya had'amu da mutanen kirki masu mutunci da sanin Yakamata, da ace duk sauran mutane haka su ke da ina tabbatar maki mabuƙata ba zasu taɓa yin kuka ba, to matsalar da aka samu irinsu ƙaɗan ne a cikin al'umma"
Dije ta share hawayenta ta ce "Ni ban ma san mi zan ce ba Baffah saboda tun da naga wannan gyaran nasab aikinshi ne, haka fa ya aikowa da su Ladiyo kuɗi Ni banma sani ba ya ce in jini su ja jari"