Sashe 77
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana ƙare faɗar hakan ya fice ɗakin fuuu ya barta zaune sake da baki, zuciyarta cike da tabbacin abunda Inna ta nusar da ita wanda ita ta kasa gano hakan sai yanzu da ta tabbatar da hangen nesan Innarta, cikin tsananin farin ciki tace
"ALLAH ya ƙara maki tsawon rai innata"
To Ameen Dijen Safwan tare da namu Innonin duka kuma ya ƙaro masu lafiya mai ɗorewa Amee🤲🏻.
Akafta🥰
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Don Allah masu neman book ɗin Ƙarangiya daga farko ku yi haƙuri idan an kammala za ku sameshi a complete ɗinshi, plss ku yi haƙuri kunji😢saboda anyi nisa sosai kuma bana son kuna tambaya baku samu ba😆*
*Lamba 69*
Duk da take cikin farin ciki haka ta fito ɗakin haɗe da fuska ta zo ta zauna tana shan ƙamshi tare da mayar da hankalinta ga kallon tv'n da ke ta aiki shi kaɗai, don shi kwance yake tare da rufe fuskarshi da hannu alamun yana cikin damuwa a zahiri, jin motsin shigowarta yasa ya buɗe ido yana kallonta, ganin yanayinta kuma ta ƙi kulashi yasa ya ji ba daɗi, ya miƙe zaune yana kallon yanda ta haɗe fuska tamau ba alamun wasa, cikin danne dariya ya taso ya zo gabanta ya yi tsugunno tare da riƙo hannunta yace
"Wai ke wace irin mace ce ke? Ni dai nasan kowace mace tana kishin mijinta amman ke har ingizashi kike yi akan ya yo maki kishiya"
Dije ta zare hannunta a hankali zata miƙe tsaye ya yi saurin dafeta ya ta shi ya zauna kan kujerar ya rungumota jikinshi ya ce
"Ki ji tsoron Allah kar ki jefa Mijinki a damuwa saboda macen da bata san muhimmancin kanta ba ma bale tasan na wani, kina kallo gaban idonki ta so kashemu da ma bata sami sa'a ba wuƙa ta ɗauko da nufin ta soka man, yanzu irin wannan matar kike so in sake dawo da ita cikinmu?"
Dije ta riƙo hannunshi ta ce "ba laifi bane don an yi maka laifi ka yafewa wanda ya cutar da kai, don ALLAH da kanshi haƙuri yake yi da mu da halayenmu saboda darajar fiyayyen halitta Annabinmu Muhammadu s.a.w da muke cin albarkacin shi, kuma a shirye yake da ya yafe muna a duk lokacin da mu ka yi tuba zuwa gareshi, tunda haka ne mu me zai hana mu yafe mata akan abunda ta aikata muna a baya?, Don ALLAH ka yafe don ni tuni na yafe mata ka sake bata wata dama matuƙar ka tabbatar da ingancin nadamar da ta yi "
Safwan ya sauke ajiyar zuciya yace "zan dawo da ita kamar yanda kika nema in har na tabbatar da gaske ta yi nadamar, amman da sharaɗin bata zo nan Abujar ba sai dai idan har ta amince zata zauna Yola, don bazan haɗaku waje ɗaya ba ta je ta koya maki mugun hali"
Dije ta ji wani sanyin daɗi ya ratsa zuciyarta cike da tsantsar farin ciki tace " ina sonka Mijina ALLAH ya baka ikon yin adalci a tsakaninmu"
Ya lakuce mata hanci
"Ya ce Ameen Matata ke ma ina sonki son da Ni kaina ban san iya adadinshi ba, na godewa ALLAH da ya azurtani da samun mace irinki, wadda take da wankakkiyar zuciya mai sowa wata abunda ta sowa kanta, don ba kowa ce mace zata iya yin abunda kika yi ba, ALLAH Ubangiji ya yi maki albarka ya kuma saukeki man ke lafiya tare da Babyna"
Cike da jin daɗi take ta faɗin "Ameen Ameen Habibyna, tom kirata yanzu ka sanar da ita ta dawo ka yafe mata"
Ya maka mata wata uwar harara ya ce "su kenan ba sai an tantance ba? Ai WALLAHI sai na tabbatar da lalle ta gyaru sannan in ce ta dawo, don bazan taɓa yarda in siyowa kaina rariyar da zata yi man asarar ruwa ba"
Dije ta ƙyalƙyale da dariya ta ce "uhummm har na tuna lokacin da ake yi man kashedi akanta, daɗin abun da dai komi yake wucewa don yanzu ga shi kai da kanka ka bayyana mata matsayina bayan ka gama yi mata ɓoyo, ai WALLAHI kai ma da naka laifi Malamina don da tun farko ka sanar da ita da abun bai yi tsananin irin wannan ba, don da ace ta kashemu da shikenan mun tafi bamu bar masu yi muna addu'a ba"
Ya sosa kanshi cike da jin nauyin maganar tata ya ce "Ni dai bana son tone tone idan abu ya wuce a dinga barinshi a matsayin ya wuce, ki ta so mu je dai ki ji wata magana dare ya fara tsalawa"
Ta bishi da wani kallo tana ƙumshe dariyarta tace
"Ni yau anan ma zan yi baccina na gaji da kwanciya akan gadon nan"
Ba shiri ya waigo ya ce "Ashe ko da ke ce zaki wahala don WALLAhi in Banda tausayin abun cikina da kinsha mamakina, amman tunda hakan kike so bari in zo daga baya na baiwa abun cikina haƙuri"
Sanin halinshi yasa ta yi saurin tashi tana dariya ta ce "mu je Ni dai yasin idan na koma haifuwa garinmu sai na yi kusan shekara ban dawo ba"
Ya riƙo hannunta yana dariya ya ce "ki ce kawai in rubuta takardar barin aiki don kin san ƙafata ƙafarki kuma idan sun gaji da halina sai su korani in koma Yola dolena"
Ta yi masa wani mintsina a gefen ciki tana dariya ta yi ɗakinta da sauri tana faɗin "banji bakinka ba WALLAhi, Ni da nake shirin zama student kake so ka yi man ciki baƙi?"
Ya bita yana dariya ya ce " to Alhudahuda ai dai kya bari ki haife man abun cikina ko?"
Haka suka dinga wasarsu cikin raha har suka kwanta bacci bayan sun gama farantawa juna cikin tsantsar ƙaunar juna.
****
Ruma kam jikinta yana rawa tun da sassafe ta je ta sanarwa Zee abunda ya faru bayan barinta wurinta, cikin sanyin jiki da zubowar hawayen tausayin kanta ta karɓi wayar ta sake kiranshi, sai dai ta yi rashin sa'a wayarshi a kashe lokacin suna gudanar da wani meeting, ganin ta ƙi samunshi ne yasa ta rubuta masa saƙo ta tura masa kamar haka
_Aslm_
_Plss my Man Ni ce Zee don girman ALLAH ka yafe mani abunda na yi maka WALLAhi na yi nadama kuma na yi godiya ga Allah da ban ci nasarar abunda na so aikatawa ba, don yanzu haka Daddyna yana kwance har yanzu bai koma dai dai ba, kuma Mummy ta tsaneni ko kusa da ita bata bari inje, gani gidan ƙasar Daddy sai azabtar da ni take yi da ayyuka kala kala don ALLAH ka taimaki rayuwata ka ce in dawo ɗakina, WALLAhi na yi alƙawarin ba zan sake_ yin abunda bai da ce ba, plss ka yafe mani mu cuddle bear wallahi sonka ne ya
rufe mani ido ya janyo
na so aikata duk abunda ka gani, don ALLAH ka ce ka yafe mani in dawo don ALLAH my Bobbie.
Tana kuka take rubuta text ɗin bayan ta tura kuma ta sake bi da kira amman kuma bata shiga ba, saboda bai buɗe wayarshi ba har sai ya dawo gida ne bayan ya gama komi sannan ya buɗe, aiko buɗewar ke da wuya sai ga saƙon Zee ya danno kai, ba ɓata lokaci ya duba duk da ya tausaya mata amman hakan bai sa ya mayar mata da amsa ko ɗaya ba, asali ma goge text ɗin ya yi gaba ɗaya a wayar, sannan ya mayar da hankalinshi akan sauran saƙonnin da suke ta shigowa.
Zee ta gaji da jira ta sake gwada kiran sai ko ta yi dace ta shiga cike da tsananin jin daɗi ta yi wani ihu saboda murna, yana ɗauka ta daburce tana ta kame kame ganin bata da abun faɗa ne ya sa ya katse kiran, cikin sauri ta sake binshi da wani kiran har sai da ta tsinke bai ɗauka ba, bata gaji ba ta sake kira ganin zata dameshi ne yasa ya ɗauka, cikin rikicewa ta fara rawar murya tana faɗin
"Don Allah ka yi haƙuri ka yafe mani my Bonnie plss"
Cikin ko in kula ya ce
"Ni fa yanzu matata ta isheni bana fatar haɗata da kowace mace a matsayin kishiya ballantana mai som ta kashe mu Ni da ita, don haka ki ƙara haƙuri sai na yi shawara in ta amince tukunna"
Yana kare faɗar maganar ya kashe wayar, Zee ta fashe da kuka cikin tsananin takaicin kanta da har ta yi abunda ya janyo mata faɗuwar daraja warwas, don daman cen ya lafiyar kura ballantana yanzu ta ci sarauta?, Dole sai haƙuri cikin kukan ta sake kiranshi caraf ya ɗauka cike da Muryar kuka ta ce
"Ko a ƴar aikinta ka ce in zo Zan zo idan har zaka yafe man abunda na yi maka"
Safwan ya ɓata fuska kamar yana ganinta ya ce "kina da labarin ina Abuja yanzu ko?"
Ta ce "a'a bani da labari" ya ce "Ok tom yanzu haka ina Abuja Ni da Matata nasami aiki ne a cen, idan kin shiryawa zaman Yola to ki tattaro kayanki ki koma, amman ki sani weekend kawai zai dawo da ni Yola idan kin amince shikenan fine, idan kuma kin ji ba zaji iyawa ba Tom sai mu sahalewa juna"
Cike da jin daɗi bakinta yana rawa ta ce
"Na amince My Man amman don ALLAH ka ce ka yafe man, itama ka nemar mani tafiyarta kafin ku haɗu"
To kawai ya ce ya kashe wayar, Zee ta yo sororo da waya a hannu tana kallon Ruma ta ce
"Ya ce in koma amman har yanzu bai ce ya yafe mani ba"
Ruma cike da tausayinta ta ce "kada ki damu a hankali yafiyar zata biyo baya in har ya fahimci kin canza ba Zee ɗin da ya sani ba ce a cen baya, fatana kawai ki san yanda zaki taushi zuciyarki saboda tsoron aikata abinda za'a azo ana da ansani daga baya"
"ALLAH ya ƙara maki tsawon rai innata"
To Ameen Dijen Safwan tare da namu Innonin duka kuma ya ƙaro masu lafiya mai ɗorewa Amee🤲🏻.
Akafta🥰
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Don Allah masu neman book ɗin Ƙarangiya daga farko ku yi haƙuri idan an kammala za ku sameshi a complete ɗinshi, plss ku yi haƙuri kunji😢saboda anyi nisa sosai kuma bana son kuna tambaya baku samu ba😆*
*Lamba 69*
Duk da take cikin farin ciki haka ta fito ɗakin haɗe da fuska ta zo ta zauna tana shan ƙamshi tare da mayar da hankalinta ga kallon tv'n da ke ta aiki shi kaɗai, don shi kwance yake tare da rufe fuskarshi da hannu alamun yana cikin damuwa a zahiri, jin motsin shigowarta yasa ya buɗe ido yana kallonta, ganin yanayinta kuma ta ƙi kulashi yasa ya ji ba daɗi, ya miƙe zaune yana kallon yanda ta haɗe fuska tamau ba alamun wasa, cikin danne dariya ya taso ya zo gabanta ya yi tsugunno tare da riƙo hannunta yace
"Wai ke wace irin mace ce ke? Ni dai nasan kowace mace tana kishin mijinta amman ke har ingizashi kike yi akan ya yo maki kishiya"
Dije ta zare hannunta a hankali zata miƙe tsaye ya yi saurin dafeta ya ta shi ya zauna kan kujerar ya rungumota jikinshi ya ce
"Ki ji tsoron Allah kar ki jefa Mijinki a damuwa saboda macen da bata san muhimmancin kanta ba ma bale tasan na wani, kina kallo gaban idonki ta so kashemu da ma bata sami sa'a ba wuƙa ta ɗauko da nufin ta soka man, yanzu irin wannan matar kike so in sake dawo da ita cikinmu?"
Dije ta riƙo hannunshi ta ce "ba laifi bane don an yi maka laifi ka yafewa wanda ya cutar da kai, don ALLAH da kanshi haƙuri yake yi da mu da halayenmu saboda darajar fiyayyen halitta Annabinmu Muhammadu s.a.w da muke cin albarkacin shi, kuma a shirye yake da ya yafe muna a duk lokacin da mu ka yi tuba zuwa gareshi, tunda haka ne mu me zai hana mu yafe mata akan abunda ta aikata muna a baya?, Don ALLAH ka yafe don ni tuni na yafe mata ka sake bata wata dama matuƙar ka tabbatar da ingancin nadamar da ta yi "
Safwan ya sauke ajiyar zuciya yace "zan dawo da ita kamar yanda kika nema in har na tabbatar da gaske ta yi nadamar, amman da sharaɗin bata zo nan Abujar ba sai dai idan har ta amince zata zauna Yola, don bazan haɗaku waje ɗaya ba ta je ta koya maki mugun hali"
Dije ta ji wani sanyin daɗi ya ratsa zuciyarta cike da tsantsar farin ciki tace " ina sonka Mijina ALLAH ya baka ikon yin adalci a tsakaninmu"
Ya lakuce mata hanci
"Ya ce Ameen Matata ke ma ina sonki son da Ni kaina ban san iya adadinshi ba, na godewa ALLAH da ya azurtani da samun mace irinki, wadda take da wankakkiyar zuciya mai sowa wata abunda ta sowa kanta, don ba kowa ce mace zata iya yin abunda kika yi ba, ALLAH Ubangiji ya yi maki albarka ya kuma saukeki man ke lafiya tare da Babyna"
Cike da jin daɗi take ta faɗin "Ameen Ameen Habibyna, tom kirata yanzu ka sanar da ita ta dawo ka yafe mata"
Ya maka mata wata uwar harara ya ce "su kenan ba sai an tantance ba? Ai WALLAHI sai na tabbatar da lalle ta gyaru sannan in ce ta dawo, don bazan taɓa yarda in siyowa kaina rariyar da zata yi man asarar ruwa ba"
Dije ta ƙyalƙyale da dariya ta ce "uhummm har na tuna lokacin da ake yi man kashedi akanta, daɗin abun da dai komi yake wucewa don yanzu ga shi kai da kanka ka bayyana mata matsayina bayan ka gama yi mata ɓoyo, ai WALLAHI kai ma da naka laifi Malamina don da tun farko ka sanar da ita da abun bai yi tsananin irin wannan ba, don da ace ta kashemu da shikenan mun tafi bamu bar masu yi muna addu'a ba"
Ya sosa kanshi cike da jin nauyin maganar tata ya ce "Ni dai bana son tone tone idan abu ya wuce a dinga barinshi a matsayin ya wuce, ki ta so mu je dai ki ji wata magana dare ya fara tsalawa"
Ta bishi da wani kallo tana ƙumshe dariyarta tace
"Ni yau anan ma zan yi baccina na gaji da kwanciya akan gadon nan"
Ba shiri ya waigo ya ce "Ashe ko da ke ce zaki wahala don WALLAhi in Banda tausayin abun cikina da kinsha mamakina, amman tunda hakan kike so bari in zo daga baya na baiwa abun cikina haƙuri"
Sanin halinshi yasa ta yi saurin tashi tana dariya ta ce "mu je Ni dai yasin idan na koma haifuwa garinmu sai na yi kusan shekara ban dawo ba"
Ya riƙo hannunta yana dariya ya ce "ki ce kawai in rubuta takardar barin aiki don kin san ƙafata ƙafarki kuma idan sun gaji da halina sai su korani in koma Yola dolena"
Ta yi masa wani mintsina a gefen ciki tana dariya ta yi ɗakinta da sauri tana faɗin "banji bakinka ba WALLAhi, Ni da nake shirin zama student kake so ka yi man ciki baƙi?"
Ya bita yana dariya ya ce " to Alhudahuda ai dai kya bari ki haife man abun cikina ko?"
Haka suka dinga wasarsu cikin raha har suka kwanta bacci bayan sun gama farantawa juna cikin tsantsar ƙaunar juna.
****
Ruma kam jikinta yana rawa tun da sassafe ta je ta sanarwa Zee abunda ya faru bayan barinta wurinta, cikin sanyin jiki da zubowar hawayen tausayin kanta ta karɓi wayar ta sake kiranshi, sai dai ta yi rashin sa'a wayarshi a kashe lokacin suna gudanar da wani meeting, ganin ta ƙi samunshi ne yasa ta rubuta masa saƙo ta tura masa kamar haka
_Aslm_
_Plss my Man Ni ce Zee don girman ALLAH ka yafe mani abunda na yi maka WALLAhi na yi nadama kuma na yi godiya ga Allah da ban ci nasarar abunda na so aikatawa ba, don yanzu haka Daddyna yana kwance har yanzu bai koma dai dai ba, kuma Mummy ta tsaneni ko kusa da ita bata bari inje, gani gidan ƙasar Daddy sai azabtar da ni take yi da ayyuka kala kala don ALLAH ka taimaki rayuwata ka ce in dawo ɗakina, WALLAhi na yi alƙawarin ba zan sake_ yin abunda bai da ce ba, plss ka yafe mani mu cuddle bear wallahi sonka ne ya
rufe mani ido ya janyo
na so aikata duk abunda ka gani, don ALLAH ka ce ka yafe mani in dawo don ALLAH my Bobbie.
Tana kuka take rubuta text ɗin bayan ta tura kuma ta sake bi da kira amman kuma bata shiga ba, saboda bai buɗe wayarshi ba har sai ya dawo gida ne bayan ya gama komi sannan ya buɗe, aiko buɗewar ke da wuya sai ga saƙon Zee ya danno kai, ba ɓata lokaci ya duba duk da ya tausaya mata amman hakan bai sa ya mayar mata da amsa ko ɗaya ba, asali ma goge text ɗin ya yi gaba ɗaya a wayar, sannan ya mayar da hankalinshi akan sauran saƙonnin da suke ta shigowa.
Zee ta gaji da jira ta sake gwada kiran sai ko ta yi dace ta shiga cike da tsananin jin daɗi ta yi wani ihu saboda murna, yana ɗauka ta daburce tana ta kame kame ganin bata da abun faɗa ne ya sa ya katse kiran, cikin sauri ta sake binshi da wani kiran har sai da ta tsinke bai ɗauka ba, bata gaji ba ta sake kira ganin zata dameshi ne yasa ya ɗauka, cikin rikicewa ta fara rawar murya tana faɗin
"Don Allah ka yi haƙuri ka yafe mani my Bonnie plss"
Cikin ko in kula ya ce
"Ni fa yanzu matata ta isheni bana fatar haɗata da kowace mace a matsayin kishiya ballantana mai som ta kashe mu Ni da ita, don haka ki ƙara haƙuri sai na yi shawara in ta amince tukunna"
Yana kare faɗar maganar ya kashe wayar, Zee ta fashe da kuka cikin tsananin takaicin kanta da har ta yi abunda ya janyo mata faɗuwar daraja warwas, don daman cen ya lafiyar kura ballantana yanzu ta ci sarauta?, Dole sai haƙuri cikin kukan ta sake kiranshi caraf ya ɗauka cike da Muryar kuka ta ce
"Ko a ƴar aikinta ka ce in zo Zan zo idan har zaka yafe man abunda na yi maka"
Safwan ya ɓata fuska kamar yana ganinta ya ce "kina da labarin ina Abuja yanzu ko?"
Ta ce "a'a bani da labari" ya ce "Ok tom yanzu haka ina Abuja Ni da Matata nasami aiki ne a cen, idan kin shiryawa zaman Yola to ki tattaro kayanki ki koma, amman ki sani weekend kawai zai dawo da ni Yola idan kin amince shikenan fine, idan kuma kin ji ba zaji iyawa ba Tom sai mu sahalewa juna"
Cike da jin daɗi bakinta yana rawa ta ce
"Na amince My Man amman don ALLAH ka ce ka yafe man, itama ka nemar mani tafiyarta kafin ku haɗu"
To kawai ya ce ya kashe wayar, Zee ta yo sororo da waya a hannu tana kallon Ruma ta ce
"Ya ce in koma amman har yanzu bai ce ya yafe mani ba"
Ruma cike da tausayinta ta ce "kada ki damu a hankali yafiyar zata biyo baya in har ya fahimci kin canza ba Zee ɗin da ya sani ba ce a cen baya, fatana kawai ki san yanda zaki taushi zuciyarki saboda tsoron aikata abinda za'a azo ana da ansani daga baya"