Sashe 60
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kada ka ji komi ni zan baka ita da hannuna fatana kawai ALLAH ya sa ka riƙe mani ita Amana kuma ka dubi son da take yi maka ka riƙeta tsakani da ALLAH"
Safwan ya dafe goshinshi cikin rikicewa yace "na gode Alhaji"
Alhajin ya sake dafa kafaɗarshi cikin murna ya ce"ALLAH ya albarkaci aurenku"
Sannan ya koma cikin ɗakin cike da jin daɗin samarwa ƴarshi abunda take so, Safwan ya riƙe ƙarfen baranda ya yi shiru tare da juya zancen cikin ranshi, ya nutsa sosai cikin zurfin tunani sai jin magana ya yi ana ce wa da shi
"Ko wane Mutum tafe yake da kundin ƙaddararshi na yarda da tawa ƙaddarar na amince na rasa Zainab ALLAH Ubangiji ya baku zaman lafiya"
Zancen Aminu kenan da ke tsaye soke da hannunshi duka biyu a aljihu, yana ƙare faɗar hakan ya juya zai tafi Safwan ya yi saurin dafo kafaɗarshi ta baya Aminu ya tsaya cak! Kamar an masa dole, Safwan ya yi ƙarfin halin faɗin
"Kada ka yi fushi akan abunda kake so ka yi haƙuri ku daidaita da Zee ku yi aurenku kawai, Ni na haƙura na bar maka ita ka je ku yi aurenku plss"
Aminu ya juyo ya sauke hannun Safwan da ke kafaɗarshi ya sake mayar da hannunshi aljihu yace
"Kada ka ji komi ka ji da kanka ni na barwa ALLAH kuma ina da tabbacin zai yi man mafita"
Yana ƙare faɗar maganar ya bar wajen tare da jan Motarshi ya fice asibitin gaba ɗaya, Safwan cikin tashin hankali ya ciro wayarshi ya kira Lawi domin ya ji a ina zai sameshi, Lawi ya yi masa kwatance sannan ya fice Asibitin ko sallama bai yi da su ba ya nufi wurin Lawin.
Cikin guntun bayani mai gamsarwa Safwan ya yi masa bayanin duk halin da ake ciki, Lawi ya yi shiru yana nazari sannan ya ce
"To ka aureta kawai tunda ƙaddarar aurenta ne ya haɗaku tun farko"
Safwan ya goge jiɓin da ya jiƙa masa fuska yace, "Ni ban san da wane idon zan kalli Khadija in ce da ita zan yi aure ba, WALLAHi ni yanzu auren Zee ya fita kaina, na fi son in mayar da hankalina kan matata in gyara abunda na ɓata a baya, in nuna mata irin gatan da kowace mace take nema a wurin Mijinta, ka sanar da ni Abokina ta ya zan saukewa kaina auren Zee??"
Lawi ya ce "ba wata mafita gaskiya saboda kai kasan irin son da take yi maka, kuma nasan kai ma kana sonta to tunda har anyi hakan mafita ɗaya ce ka sami Aminun har gida ka sanar da shi da gaske kake yi ka bar masa Zee, idan ya amince shikenan idan kuma ya ƙi sai ka aureta kawai tunda ALLAH bai haramta maka ita ba"
Safwan ya yi shiru yana nazari sannan ya nemi Lawin ya rakashi su je gidansu Aminun ba musu suka nufi gidan, sai dai iya daɗin bakinsu da nuna masa su ma sun san fiqhu da Tauhidi bai sa Aminu ya karɓi buƙatarsa ba, don ya yi biris akan buƙatarsu sosai ya rufe ido ya nuna baya ra'ayin aurenta, sannan ya nuna masu cewa shi fa ya haƙura ya yi imani akan duk abunda ALLAH ya tsara masa, kuma insha ALLAHu shi ma kwanan nan zai fito da mata ya yi aurenshi, dole ba don sun so ba suka haƙura suka bar gidan cikin sanyin jiki.
Tare suka koma Asibitin da Lawi sun ɗan jima a cen sannan suka yi masu sallama suka dawo gidan Lawin, gidanshi da yake ta gyara saboda lokacin aurenshi da yake ta matsowa.
Da safe ma ko da suka koma sun taradda ita da sauƙi sosai don kuwa sai samuwa yake yi a hankali, ganin hakan yasa ƴan'uwan Zee suka ta yi masa godiya tare da yi masu fatar alkhairi a auren nasu, cike da jin nauyi yake amsa masu ba yabo ba fallasa.
Kasancewar Zee ta ji albishiri ɗin aurenta da Safwan a bakin mahaifinta yasa ta saki jiki sai wasar baki take yi, zuciyarta cike da jin daɗin mallakar mutumen da tafi so fiye da kowa ne ɗa Namiji a duniya.
Bayan kowa ya fice ne aka barta da Safwan ɗin don ko Lawi fitowarshi ya yi ya barosu, cike da jin daɗin ganinshi cikin muryar ciyo ta ce
"My hero ya zaka yi da mata biyu da kake ƙoƙarin haɗawa a zuciyarka?"
Safwan ya yi dariyar yaƙe ya ce
"ALLAH zan roƙa ya bani ikon yin adalci tsakaninku"
Cikin jin kishin matar tashi ta ce, "to yanzu idan mun yi auren da ita zamu koma school ko kuwa?"
Ya yi shiru sannan ya ce, "sai abunda Hajiyata ta ce sannan duk hukuncin da ta yanke muna to ni banda ja akanshi"
Cikin sauri aranta ta ce _"ALLAH yasa ma ta ce a barta anan ɗin mu mu tafiyarmu abunmu"_
Amman a fili tace
"ALLAH ya sa mu dace all, amman plss ka nuna mani wacece Uwargidana ko da a hoto ne, don ina son na nasan wacece ta yi saurin sace zuciyar Realitynah?"
Safwan ya yi ƴar dariya saboda tuno Dijen Baffah sannan ya ce "saurin me kike yi zaki santa soon Insha ALLAH "
Haka Zee ta yi ta shige masa suna ta firarsu cikin natsuwa har Safwan ɗin ya yi sallama da ita akan zai koma Yola ya turo Iyayenshi ayi zancen auren nasu.
Cike da tsantsar farin ciki ta yi ta jera masa kalaman soyayya tare da yi masa fatan ALLAH ya tsare hanya, da ma zai ta fi har son ta yi ta sauko ta rakashi sai da ya hanata sannan ta haƙura, tana yi masa bye bye yana yi mata suka rabu.
Mahaifinta ya karɓi account ɗin Safwan a take yanke ya yi masa transfer ta 2million ya ce da shi ya je ya fara shirye shiryen aurenshi da Zee, saboda komi cikin gaggawa yake son ayi saboda buƙatar su koma makaranta cikin lokaci.
Safwan ya tafi zuciyarshi ba yabo ba fallasa don har cikin ranshi bai yi wata murna akan auren ba bale kuɗin da Daddyn Zee ya ba shi, don a ganinshi tamkar ma ya renashi ne, saboda tambayar kanshi da ya yi akan cewa, shin ya ɗauki kuɗin ya bashi ne don ya siyeshi da kuɗin ya auri ƴarshi? ko ku wa don ya nuna masa cewa su ma masu kuɗi ne fiye da su?.
Oho Safwan🙄 ni dai in baka so ko 5ok ka yi man transfer a nawa bank account na yi maka alƙawari zan tayaka addu'ar neman zaɓin ALLAH😝
Akafta🤣
D/AUTA Ce
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Because of you ƙanwata Leemart pinkey MHiss purple ALLAHU ya bar zumunci ta hannun damata🖐🏻*
*Lamba ta 57*
Jiki ba kuzari yake driving har ya isa Yola cikin amincin ALLAH, sai dai yawan faɗuwar da gabanshi yake yi yasa ya ji baya sha'awar zuwa gida, sai da ya biya wajen Mubarak suka tattauna sosai akan matsalar sannan ya nufo gidan.
Jiki a sanyaye ya yi parking ya daɗe zaune cikin motar yana nazarin ta ina zai fara?, wurin Hajiya Mama ko wurin Khadijarshi?, a ƙarshe dai ya yanke shawarar fara tunkarar Hajiyar saboda ta fi khadija matsala a wurinshi, don ita da ya kanainayeta da daɗin baki zata bi ba tare da yasha wahala ba, cikin ƙarfin gwiwar da zuciyarshi take ba shi ne ya fito ya nufi cikin gidan, sai ko ya taki sa'a ya taradda Hajiyar da Fiddo a babban falo suna kallo, ya shigo da sallamarshi ya ƙaraso ya zauna tare da faɗin
"Wash! ALLAH Hajiyarmu gani na dawo lafiya"
Idonta akan tv tace "masha Allah sannu da dawowa"
Fiddo ta gayar da shi cikin ladabi sannan ta ce, ,"big bros ya jikin Aunty Zee ɗin? da fatar taji sauƙi sosai?"
Ya shafo sumar kanshi da take cike da gashi kwance baƙi ƙirin a saman kan nashi, sannan ya ce
"Ta sami lafiya khadija fa?"
Fiddo ta yi saurin kallon Hajiya Mama sannan ta ce "Tana ɗaki maybe bacci take yi"
Cikin jin nauyin idon Hajiyar ya ce "je ki ce ta kawo man abinci"
Fiddo ta daburce ta miƙe tana sosa kai tace "tun ɗazu fa kamar bata gidan nan don ban ga ko wulgawarta ba"
Cikin faɗuwar gaba ya zaro ido waje "me kike nufin sanar da ni? Ba ta nan to ina ta je ne ba tare da izinina ba??, Hajiyarmu ko ke kika aiketa ne don nasan Khadija ko ƙawa bata da a cikin garin nan bale ace ta je cen, ko dai tana gidan Surayya ne?"
Hajiya Mama cikin ko in kula ta ce, "mi ye damuwarka da ita ne? Ni fa bana son takura, saboda haka ka bar yarinya ta sha iska"
Safwan ya marairece fuska yace , "matata ce fa Hajiya ko ba komi akwai haƙƙin aurena a kanta"
Hajiya ta maka masa harara ta ce "don kana aurenta ai har yanzu bata zama kamar sauran matan aure ba, don cikin haƙƙoƙanta da Allah ya rataya a wuyanka nawa ka sauke faɗa man cinka? ko shanka? Ko kuma suturarka?, To bana son zaƙewa da yawa don ni nake da ikonta tunda kai da kanka ka saka muna ita cikin ƴan aikinmu, to yanzu kuma ka ke son zuwa ka kawo mani wani zancen banza cen"
Safwan ya yi saurin faɗin "to na tuba a gafarceni Hajiya yanzu ina ta je in je in ɗaukota",
Cikin basarwa Hajiyar ta ce "to Khadija dai bata gidan nan na turata aikatau wani gari, saboda naga mu nan ƴan aikin ma sun yi muna yawa, shine na ga da a barta haka kawai zaune ba wani moruwarta da muke yi, shine na ga gara kawai na turata cen ɗin, insha ALLAHu duk kuɗinta na wata wata idan an aiko mani zan je da kaina har ƙauyensu in kai wa iyayenta"
Firgici tashin hankali tare da ruɗewa duka suka ziyarto wa Safwan ba tare da ya shiryawa zuwansu ba, cike da wani tsantsar tsagwaron tashin hankalin da ya bayyana a kan fuskarshi ya ce
Safwan ya dafe goshinshi cikin rikicewa yace "na gode Alhaji"
Alhajin ya sake dafa kafaɗarshi cikin murna ya ce"ALLAH ya albarkaci aurenku"
Sannan ya koma cikin ɗakin cike da jin daɗin samarwa ƴarshi abunda take so, Safwan ya riƙe ƙarfen baranda ya yi shiru tare da juya zancen cikin ranshi, ya nutsa sosai cikin zurfin tunani sai jin magana ya yi ana ce wa da shi
"Ko wane Mutum tafe yake da kundin ƙaddararshi na yarda da tawa ƙaddarar na amince na rasa Zainab ALLAH Ubangiji ya baku zaman lafiya"
Zancen Aminu kenan da ke tsaye soke da hannunshi duka biyu a aljihu, yana ƙare faɗar hakan ya juya zai tafi Safwan ya yi saurin dafo kafaɗarshi ta baya Aminu ya tsaya cak! Kamar an masa dole, Safwan ya yi ƙarfin halin faɗin
"Kada ka yi fushi akan abunda kake so ka yi haƙuri ku daidaita da Zee ku yi aurenku kawai, Ni na haƙura na bar maka ita ka je ku yi aurenku plss"
Aminu ya juyo ya sauke hannun Safwan da ke kafaɗarshi ya sake mayar da hannunshi aljihu yace
"Kada ka ji komi ka ji da kanka ni na barwa ALLAH kuma ina da tabbacin zai yi man mafita"
Yana ƙare faɗar maganar ya bar wajen tare da jan Motarshi ya fice asibitin gaba ɗaya, Safwan cikin tashin hankali ya ciro wayarshi ya kira Lawi domin ya ji a ina zai sameshi, Lawi ya yi masa kwatance sannan ya fice Asibitin ko sallama bai yi da su ba ya nufi wurin Lawin.
Cikin guntun bayani mai gamsarwa Safwan ya yi masa bayanin duk halin da ake ciki, Lawi ya yi shiru yana nazari sannan ya ce
"To ka aureta kawai tunda ƙaddarar aurenta ne ya haɗaku tun farko"
Safwan ya goge jiɓin da ya jiƙa masa fuska yace, "Ni ban san da wane idon zan kalli Khadija in ce da ita zan yi aure ba, WALLAHi ni yanzu auren Zee ya fita kaina, na fi son in mayar da hankalina kan matata in gyara abunda na ɓata a baya, in nuna mata irin gatan da kowace mace take nema a wurin Mijinta, ka sanar da ni Abokina ta ya zan saukewa kaina auren Zee??"
Lawi ya ce "ba wata mafita gaskiya saboda kai kasan irin son da take yi maka, kuma nasan kai ma kana sonta to tunda har anyi hakan mafita ɗaya ce ka sami Aminun har gida ka sanar da shi da gaske kake yi ka bar masa Zee, idan ya amince shikenan idan kuma ya ƙi sai ka aureta kawai tunda ALLAH bai haramta maka ita ba"
Safwan ya yi shiru yana nazari sannan ya nemi Lawin ya rakashi su je gidansu Aminun ba musu suka nufi gidan, sai dai iya daɗin bakinsu da nuna masa su ma sun san fiqhu da Tauhidi bai sa Aminu ya karɓi buƙatarsa ba, don ya yi biris akan buƙatarsu sosai ya rufe ido ya nuna baya ra'ayin aurenta, sannan ya nuna masu cewa shi fa ya haƙura ya yi imani akan duk abunda ALLAH ya tsara masa, kuma insha ALLAHu shi ma kwanan nan zai fito da mata ya yi aurenshi, dole ba don sun so ba suka haƙura suka bar gidan cikin sanyin jiki.
Tare suka koma Asibitin da Lawi sun ɗan jima a cen sannan suka yi masu sallama suka dawo gidan Lawin, gidanshi da yake ta gyara saboda lokacin aurenshi da yake ta matsowa.
Da safe ma ko da suka koma sun taradda ita da sauƙi sosai don kuwa sai samuwa yake yi a hankali, ganin hakan yasa ƴan'uwan Zee suka ta yi masa godiya tare da yi masu fatar alkhairi a auren nasu, cike da jin nauyi yake amsa masu ba yabo ba fallasa.
Kasancewar Zee ta ji albishiri ɗin aurenta da Safwan a bakin mahaifinta yasa ta saki jiki sai wasar baki take yi, zuciyarta cike da jin daɗin mallakar mutumen da tafi so fiye da kowa ne ɗa Namiji a duniya.
Bayan kowa ya fice ne aka barta da Safwan ɗin don ko Lawi fitowarshi ya yi ya barosu, cike da jin daɗin ganinshi cikin muryar ciyo ta ce
"My hero ya zaka yi da mata biyu da kake ƙoƙarin haɗawa a zuciyarka?"
Safwan ya yi dariyar yaƙe ya ce
"ALLAH zan roƙa ya bani ikon yin adalci tsakaninku"
Cikin jin kishin matar tashi ta ce, "to yanzu idan mun yi auren da ita zamu koma school ko kuwa?"
Ya yi shiru sannan ya ce, "sai abunda Hajiyata ta ce sannan duk hukuncin da ta yanke muna to ni banda ja akanshi"
Cikin sauri aranta ta ce _"ALLAH yasa ma ta ce a barta anan ɗin mu mu tafiyarmu abunmu"_
Amman a fili tace
"ALLAH ya sa mu dace all, amman plss ka nuna mani wacece Uwargidana ko da a hoto ne, don ina son na nasan wacece ta yi saurin sace zuciyar Realitynah?"
Safwan ya yi ƴar dariya saboda tuno Dijen Baffah sannan ya ce "saurin me kike yi zaki santa soon Insha ALLAH "
Haka Zee ta yi ta shige masa suna ta firarsu cikin natsuwa har Safwan ɗin ya yi sallama da ita akan zai koma Yola ya turo Iyayenshi ayi zancen auren nasu.
Cike da tsantsar farin ciki ta yi ta jera masa kalaman soyayya tare da yi masa fatan ALLAH ya tsare hanya, da ma zai ta fi har son ta yi ta sauko ta rakashi sai da ya hanata sannan ta haƙura, tana yi masa bye bye yana yi mata suka rabu.
Mahaifinta ya karɓi account ɗin Safwan a take yanke ya yi masa transfer ta 2million ya ce da shi ya je ya fara shirye shiryen aurenshi da Zee, saboda komi cikin gaggawa yake son ayi saboda buƙatar su koma makaranta cikin lokaci.
Safwan ya tafi zuciyarshi ba yabo ba fallasa don har cikin ranshi bai yi wata murna akan auren ba bale kuɗin da Daddyn Zee ya ba shi, don a ganinshi tamkar ma ya renashi ne, saboda tambayar kanshi da ya yi akan cewa, shin ya ɗauki kuɗin ya bashi ne don ya siyeshi da kuɗin ya auri ƴarshi? ko ku wa don ya nuna masa cewa su ma masu kuɗi ne fiye da su?.
Oho Safwan🙄 ni dai in baka so ko 5ok ka yi man transfer a nawa bank account na yi maka alƙawari zan tayaka addu'ar neman zaɓin ALLAH😝
Akafta🤣
D/AUTA Ce
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Because of you ƙanwata Leemart pinkey MHiss purple ALLAHU ya bar zumunci ta hannun damata🖐🏻*
*Lamba ta 57*
Jiki ba kuzari yake driving har ya isa Yola cikin amincin ALLAH, sai dai yawan faɗuwar da gabanshi yake yi yasa ya ji baya sha'awar zuwa gida, sai da ya biya wajen Mubarak suka tattauna sosai akan matsalar sannan ya nufo gidan.
Jiki a sanyaye ya yi parking ya daɗe zaune cikin motar yana nazarin ta ina zai fara?, wurin Hajiya Mama ko wurin Khadijarshi?, a ƙarshe dai ya yanke shawarar fara tunkarar Hajiyar saboda ta fi khadija matsala a wurinshi, don ita da ya kanainayeta da daɗin baki zata bi ba tare da yasha wahala ba, cikin ƙarfin gwiwar da zuciyarshi take ba shi ne ya fito ya nufi cikin gidan, sai ko ya taki sa'a ya taradda Hajiyar da Fiddo a babban falo suna kallo, ya shigo da sallamarshi ya ƙaraso ya zauna tare da faɗin
"Wash! ALLAH Hajiyarmu gani na dawo lafiya"
Idonta akan tv tace "masha Allah sannu da dawowa"
Fiddo ta gayar da shi cikin ladabi sannan ta ce, ,"big bros ya jikin Aunty Zee ɗin? da fatar taji sauƙi sosai?"
Ya shafo sumar kanshi da take cike da gashi kwance baƙi ƙirin a saman kan nashi, sannan ya ce
"Ta sami lafiya khadija fa?"
Fiddo ta yi saurin kallon Hajiya Mama sannan ta ce "Tana ɗaki maybe bacci take yi"
Cikin jin nauyin idon Hajiyar ya ce "je ki ce ta kawo man abinci"
Fiddo ta daburce ta miƙe tana sosa kai tace "tun ɗazu fa kamar bata gidan nan don ban ga ko wulgawarta ba"
Cikin faɗuwar gaba ya zaro ido waje "me kike nufin sanar da ni? Ba ta nan to ina ta je ne ba tare da izinina ba??, Hajiyarmu ko ke kika aiketa ne don nasan Khadija ko ƙawa bata da a cikin garin nan bale ace ta je cen, ko dai tana gidan Surayya ne?"
Hajiya Mama cikin ko in kula ta ce, "mi ye damuwarka da ita ne? Ni fa bana son takura, saboda haka ka bar yarinya ta sha iska"
Safwan ya marairece fuska yace , "matata ce fa Hajiya ko ba komi akwai haƙƙin aurena a kanta"
Hajiya ta maka masa harara ta ce "don kana aurenta ai har yanzu bata zama kamar sauran matan aure ba, don cikin haƙƙoƙanta da Allah ya rataya a wuyanka nawa ka sauke faɗa man cinka? ko shanka? Ko kuma suturarka?, To bana son zaƙewa da yawa don ni nake da ikonta tunda kai da kanka ka saka muna ita cikin ƴan aikinmu, to yanzu kuma ka ke son zuwa ka kawo mani wani zancen banza cen"
Safwan ya yi saurin faɗin "to na tuba a gafarceni Hajiya yanzu ina ta je in je in ɗaukota",
Cikin basarwa Hajiyar ta ce "to Khadija dai bata gidan nan na turata aikatau wani gari, saboda naga mu nan ƴan aikin ma sun yi muna yawa, shine na ga da a barta haka kawai zaune ba wani moruwarta da muke yi, shine na ga gara kawai na turata cen ɗin, insha ALLAHu duk kuɗinta na wata wata idan an aiko mani zan je da kaina har ƙauyensu in kai wa iyayenta"
Firgici tashin hankali tare da ruɗewa duka suka ziyarto wa Safwan ba tare da ya shiryawa zuwansu ba, cike da wani tsantsar tsagwaron tashin hankalin da ya bayyana a kan fuskarshi ya ce