← Book details Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 53 OF 84

Sashe 53

Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Dije!!" Inna ta ƙwallawa Dijen kira tace ta je ta kaishi ɗakin samartakar Usmanu ya ci abinci, Dije ta fito tana tunzure tunzure ta nufi ɗakin da ke cikin zauren gidan, wanda tun da safe Inna ta gyarashi tsaf aka malala ƙatuwar tabarma sabuwa dal, tare da wata babbar carpet a samanta, ga wani turaren wuta da aka ƙamsasa ɗakin da shi, kasancewar Abincin da komi da aka tanadar masa yana ɗakin an ajiye, Dije tana shiga ɗakin ta ja ta tsaya tana wani cin magani tana gunguni, Safwan cike tsantsar farin ciki ya nufi inda take tsaye ya tsaya tare da rungume hannuwa a ƙirji yana ƙare mata kallo cikin hasken ƙatuwar fitilar cajin da ke haskaka ɗakin, wadda takanas Usmanu ya siyowa su Inna ita har da Baffah da tashi ta zama torch light a babban birnin garinsu, idan zai je da safe ya fita da su a cikosu da caji ya kawo masu, shiyasa basu rabo da caji kullum gasu da ɗan karen haske tamkar nefa.

Kallon da Safwan ɗin yake yi mata ne yasa ta ɗago fuskarta tana yi masa hararar sama da ƙasa, sannan tace

"Ka daina murna don kaji ance zan koma WALLAHi muddin ka sake taɓani idan na baro garin to ko gidan nan bazan dawo ba, tunda na gano suma ɗin ba sona suke yi ba komi nayi sai anga laifina"

Safwan ya sauke wata ajiyar zuciya tare da ƙara matsowa daf da ita ya dafa bango da hannunshi ɗaya yayi mata rumfa, cikin tsoro ta yi saurin kallonshi tace

"A gidan namu ma bazaka barni ba kenan?"

Yayi wani murmushin gefen baki yace, "Ni ba a namu gidan kika so ki kasheni da soyayyarki ba? Ko kin manta abunda kika yi mani a gaban kowa wanda har yanzu gashi kin janyo budurwata ta gujeni?"

Dije ta yi saurin rufe fuska tace, "Surayya ce tace dani inyi hakan idan naganka tare da budurwar, to ma ni ina ruwana da ita da har zansa ta gujeka?, Ka je cen ku sasanta abunku don ni yanzu gaba ɗaya ma daga kai har ita baku gabana"

Ba shiri ya ɗora hannunshi saman leɓunan bakinta, cikin wata siririyar murya yace, "shiiiiiii! Bana son doguwar magana anan gidan, ki zo kawai ki bani abincin da aka ce ki bani yunwa nake ji"

Ya ƙare maganar tare da langaɓe mata kai kamar wani yaro, Dije ta kalleshi cike da mamakinshi ta ce

"Ka je gashi cen ka ci ni bana son salon yaudara don an ganni cikin gidanmu"

Safwan ya yi saurin haɗe fuska ya ce

"To shikenan bari inje in sanarwa da Inna kince in zuba da kaina"

Yana gama faɗar maganar ya nufi ƙofa da nufin fita ta yi saurin shan gabanshi tace, "To Ni dai ka tsaya ai ba cewa na yi bazan zuba ba ko?"

Ya yi saurin bushewa da dariya yace, "to muje ki bani kuma ga baki nake so idan ba haka ba yanzu inje in sanarwa da su Baffah"

Dije ta yi saurin zuwa wajen kayan abincin tana zuba masa ta ce

"shi dai mutum duk muguntarshi to ya kiyayi haɗa ɗiya da Uwayenta"

Cikin dariya ya ce

"Wannan kuma ai sai ki yiwa kanki wa'azi don ke kullum aikinki kenan haɗa ɗa da Uwatai, yanzu haka akanki ance kada ya kuskura ya sake taka gidan Ubanshi matuƙar ba tare da ke ya dawo ba, sai ki auna da tawa muguntar da taki wacece ta fi muni???"

To reader's ku bashi amsa in Dijen taku ta kasa🤪

Akafta🤣

D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*

*NA HADIZA D/AUTA*

*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*

*Ina baku haƙuri akan rashin mayar da reply ɗin da banyi ba na comments ɗinku😍amman ku sani na gani all kuma ngd gaba ɗayanku🙏🏻*

*Lamba ta 51*

Dije tace "taka muguntar ce mana, saboda miye ma Ni baka yi man ba?, Ai WALLAHi ka ci sa'ar Inna ta ce kada in koma yi maka wani abun da bai dace ba, da bazaka bar garin nan ba har sai na bar maka shaidar da zaka nuna a matsayin tarbar da nayi maka, wadda a kullum ka kalleta sai ka tuno da ni don kuwa tambon ba zai taɓa goguwa a jikinka ba"

Safwan ya tako a hankali ya ƙaraso inda take zuƙunne tana zuba abincin, shima ya yi durƙuso ido cikin ido yake kallonta na tsawon mintuna, sannan cikin wata murya mai kama da raɗa ya ce

"Ko yanzu mi ye marabar dambe da faɗa?, Ai tuni kin barni da taɓon da ya fi wanda kike da gurin yi mani a yanzu, tambon da nike da tabbacin har abada ba zai taɓa goguwa a cikin zuciyata ba, kin riga da kin sakar mani dafin da ya bi jikina ya mamaye ko'ina lungu da sak'o, a ganinki wannan tambon bai fi wanda kike ikirarin ki yi man ba a yanzu?"

Dije ta turo baki ta ce,

"Ai fa yanzu kam tunda an ganni gidanmu komi ma cewa za'a yi, amma da na yi sakacin da na bika kuma sai ka nunawa duniya cewa ni ɗin ba kowa ba ce bayan ƙaskantacciyar ƴar ƙauye, ka sani a shekarun baya ka yi nasara akaina wajen biyarka da na yi saboda daɗin bakin da ka yi mani, amman ka sani wannan karon daban da wancen cen, saboda cikin alƙawullan da ka ɗaukar mani ko ɗaya baka cika mani ba"

Cike da mutuwar jikin da kalaman nata suka haifar masa ya yi jarumtar faɗin

"Kamar wane da wane fa don ina son yanzu in tabbatar maki da gaskiyar duk abunda kika ji ya fito bakina"

Dije ta jawo abincin gabanshi ta ce

"Ka zauna da kyau ka ci abincin ni dai kada ƙafafuwanka su yi sanyi ace garinmu aka samu ciyon"

Tana ƙare faɗar maganar ta miƙe ya yi saurin riƙo hannunta yace, "ina zaki je kuma muna firarmu mai daɗi?"

Dije ta wurga masa wata harara tace, "abinci aka ce in baka Kuma gashi na baka to kuma ni yanzu zaman me kake so in yi anan?"

Safwan yana rike da hannunta ya yunƙura ya miƙe tsaye, cikin mayen sonta da ke fisgarshi ya saka hannu biyu ya rungumota duka jikinshi, ta yi saurin zillewa amman sai da ya sake rungumotan har ƙamshin turarenshi mai daɗi ya daki hancinta, cikin wata murya da ita kanta batasan ya aka yi ta canza ba tace

"Haba Malam ka daina abunda kake yi ba kyau fa, saboda akan wannan halin naka na dawo gida amman kuma gashi anan ɗin ma ban tsira ba, kai wai halan baka jin kunyar wani ya ganmu da wannan zunubin da kake ƙoƙarin aikatawa gareni kullum?"

Safwan ya kai bakinshi saiti da nata ya sakar mata wani guntun kiss, ta yi saurin kaucewa tana goge bakin da hannunta ta ce

"WALLAHi Malam kaji tsoron Allah Ni dai gaskiya nike faɗa maka"

Ya yi saurin damƙe hannunta yace "tsoron ALLAHn kenan tunda ba wani waje naje nayi hakan ba, kuma mallakina ce ke ina da ikon yin duk abunda nake so da ke, saboda Allah ya bani damar in zo maki a duk lokacin da na so kuma inyi abunda naga dama"

Dije ta zaro ido tare da rufe baki alamun firgici tace, "har da irin wannan abun duka?"

Ya ɗaga mata kai tare da lumshe ido sannan ya buɗesu fes akanta yace, "har da shi har da ma kuma abunda yafi hakan ɗin duka"

Dije ta yi saurin ƙwace jikinta ta ce, "Ni dai WALLAHI Allah ban son irin wannan lalacewar, don wannan ma idan wani ya ji ai sai kasa ayi mani kallon ƴar'iska, haka fa wani a tasha ya so ya lalaceni ALLAH ya taimakeni asirinshi ya tonu"

Dirim! dum! dam! Haka ƙirjinshi ya buga ba shiri tare zuwan wani aringizon tashin hankalin da ya ziyartoshi, yanayin da ta ganshi yasa ta yi saurin shan jinin jikinta saboda tsoron kada ya kai mata duka, amman duk da hakan sai da ya damƙo gashinta iya ƙarfinshi yace

"Me kika aikata man bayan idona? Wanene shi? Wa ya baki izinin fitowa gida ba tare da izinana ba? WALLAHi kinji na rantse kika yarda wani abu ya faru WALLAHi dake ki sani bazan taɓa yafe maki ba"

Ya yi wurgi da ita har sai da kanta ya daku da gini ba shiri ta fasa wata uwar ƙara, amman ko takanta bai bi ba ya fice ɗakin fuuu ko da su Baffah suka fito sai jin ƙarar tashin Motarshi suka yi, cike da mamaki suke tambayarta me ya faru

Cikin kuka take sanar da su cewa

"Wai fa daga na faɗa masa abunda wani ɗan iska yaso ya yi mani a cikin tasha shine fa ya jawo mani gashi iya ƙarfinshi har sai da na bugu da gini, ya yi fushi ya tafiyarshi gashi ko abincin ma bai tsaya ya ci ba"

Baffah da Inna da shi kanshi Usmanu suka ƙumshe dariyarsu, saboda kai tsaye sun gano cewa kishinta ne ya janyo yayi abunda yayi, Inna ta fara yi mata faɗan rashin dalili tace

"Ai in dai baki bar baƙin surutunki ba to sai ya janyo maki watarana ya yi maki ɗan karen duka, ai gara da ya yi maki hakan sai gobe ki ƙara tunda ke bakinki sam baya da sirri kwata kwata"

Dije ta yi fuuu ta wuce ɗakin Innar tana kuka saboda takaicin tafiyar da ya yi bai ci abincin ba, Usmanu ya yi sashenshi yana dariya a ranshi yace

"Wannan yarinya ko yaushe zata yi hankali Oho?"

Baffah da Inna Kam tsakar gida suka yada zango suna ta firar Dijen da shi Safwan ɗin, zuciyar inna cike da jin daɗin ganin Safwan ɗin yana mugun son Dijen tasu, saboda abunda ya yi yasa dukansu sun gano cewa ba ƙaramin so yake yi mata ba, haka ma yasan darajarta zai riƙeta amana ya bata kulawar da kowace mace take buƙata a wurin mijinta.
Chapter 53 · 0% Book details