Sashe 50
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Safwan cike da jin haushinshi yace, "kai da ka yi mani waliccin auren ai sai ka yi mata bayani da bakinka don sai tafi saurin gamsuwa dai dai"
Zee ta washe baki ta ce "ƙyaleshi my cuddle bear nasan kishi ne yake taya Abokinshi bayan ni na riga da na yi masu nisa sai dai haƙuri"
Kamal ya yi mata wani kallo cike da jin haushin irin cin amanar da zata yi wa Abokinshi yace, "ita dai gaskiya idan ta tashi fita tafin hannu ya yi kaɗan da ya kareta, haka duk wanda ya ci amana to ya sani akwai lokacin da ranar sakamako zata ziyartoshi, ni kinga tafiyata fatana kawai ita Uwargidan ALLAH ya bata haƙurin sammakon da za'a yi mata"
Yana ƙare faɗar haka ya wuce abinshi, daga Safwan har ita Zee suka bishi da wani kallo mai ƙumshe da harara, ran Zee a jagule ta kalli Safwan ta ce"
"My hero Wai me yasa a ko'ina sai an samu yan adawa ne?, Ji don ALLAH yanda yake wani zaƙewa sai kace shine Aminun?"
Safwan ranshi a ɓace yace, "shareshi kawai hassada ce zo muje ki yi sallama da Hajiya mu je in raka ku gida tun kafin wannan magulmacin ya ɓata muna tsari"
Ya yi gaba Zee tare da janyo hannun ƙawarta amman sai Ruma ta ce da ita su je kawai ita zata jirasu, suna shigewa Ruma ta yi wurin Kamal zuciyarta cike da son jin gaskiyar abunda yake son sanar da Zee, ta nemi izinin ganinshi na ɗan lokaci suka keɓe gefe, Ruma ta zama serious bayan sun ƙare ɗan barkwancin da suka saba tace
"Kamal don ALLAH ka sanar da ni gaskiyar zance shin da gaske Man ɗin Zee yana da aure?"
Kamal ya yi yar gajeruwar dariya yace, "tunda kince ALLAH to ba wani kwana da zan tsaya yi maki, tabbas Safwan yana da Mata asali ma yanzu haka shekararshi biyu cikin ta uku da aurensu"
Ruma ta zaro ido waje tace, "Kamal kasan dai bamu irin wannan wasar da kai ko?, tsakaninka da ALLAH na roƙeka ka faɗa mani gaskiyar lamarin, saboda WALLAHi Zee ta mato sosai akan wannan guy ɗin idan har ta ji wannan magana nasan ba ƙaramin tashin hankali zata shiga ba"
Kamal ya karkace baki yana dariyar gefe idonshi suka kai ga Surayya da ke ta ɗaukar hotuna da Ƙawayenta ya yafitota da hannu, ta nufoshi tana dariya kasancewar tasanshi sosai saboda tare suka yi karatu da Safwan a garin, asali ma kamar gidan suke dukansu har da Lawi a lokacin da suka yi karatun jami'arsu.
Tana zuwa ta gayar da shi a mutunce bayan sun gaisa ya ce da ita, "Surayya ki yi mata bayanin gaskiya saboda ta ji da kunnuwanta, shin da gaske Safwan yana da aure ko kuwa?"
Surayya ta washe baki tace, "ALLAH sarki ƴar uwa da gaske kuwa Yayanmu yana da aure kuma yana bala'in son Matarshi, haka itama kuma tana sonshi sosai"
Diirim! dum! Shine abunda zuciyar Ruma ta yi saboda maganar ba ƙaramin bugun zuciyarta ta yi ba, nan take ta fara tausayin ƙawarta cikin canzawar yanayinta da ya koma kalar damuwa ta ce
"ALLAH sarki ko zaki iya nuna mani matar in ganta don ALLAH"
Surry tace, "bari in dubota don tun ɗazu ma ban ganta ba"
Surry ta yi cikin gidan zuciyarta cike da fatar ALLAH yasa ma auren ya wargaje kowa ma ya huta, sai dai duk bulayin neman Dijen da ta yi bata ganta ba, dole ta dawo da nufin sanar da ita cewa bata ganta ba, sai ga shi ma ta taradda su duka har da Safwan ɗin suna sallama da juna, saboda Ruma bata nuna komi ba nufinta sai sun je masaukinsu ta sanar wa da ƙawarta gaskiyar zancen.
Cikin tsoro Surry ta yi saurin komawa cikin gidan ta laɓe, har suka fita Gate ɗin gida Safwan ya bi su a baya sannan ta fito tana sauke ajiyar zuciya.
To sai dai abu kamar wasa har dare anata neman Dijen Baffah ammsn ba'a ganta ba, tun ana ɗaukar abun wasa har kowa hankalinshi ya fara tashi don kuwa anyi nemanta ko'ina gidan kaf ba'a ganta ba, Hajiya ta firgice sosai sai kiran Safwan take yi akan ta ji shin yana tare da Dijen ko kuwa, amman bai ɗauka ba saboda bai ma san ta kirashi ba don wayar a silen take, sai bayan ya gama firarshi da Zee ne Suka yi sallama yana kan hanya ya ga tarin miss calls na Hajiyar da su Surry da wasu ƴan uwansu duka, cikin tashin hankali ya dannawa Hajiyar kira sai ko ta yi caraf ta ɗauka, ba tare da ta jira jin abinda zai faɗa ba ta ce
"Ina khadija kuna tare da ita ne?"
Safwan a firgice yace "A'a WALLAHi Ni tun ɗazu rabon da na ganta"
Hajiyar ta yi saurin faɗin ka yi gaggawar nemota duk inda take, saboda an duba kaf gidan nan ba'a ganta ba, kuma jikina yana bani kai ne ka yi mata abunda ya janyo ta bar gidan, WALLAHi ka ji na rantse matuƙar baka nemo man ita ba to ko kada ka kuskura ka tako ƙafarka cikin gidan nan".
Kitt! Ta kashe wayar zuciyarshi cike da tashin hankali ya furta "Innalilahi wa'Inna ilairraji'un"
Cikin ruɗewa ya nufi tasha saboda cen zuciyarshi ta hasko masa zata nufa, saboda cewar da ta yi masa bata son karatun ita garinsu zata koma, sai dai kuma duk iya binciken da aka yi tashar babu sunan Khadija Umar a cikin jerin list ɗin mutanen da Motarsu ta tashi ranar a tashar, ya fito a gigice ya nufi wata ƙaramar tashar da ake shiga Mota nan ma ba wani alamun ta je cen, haka ya yi ta zagayen wuri wuri amman ko mai kama da ita bai gani ba, dole ya yi parking ya fito dafe da kanshi da ke yi masa mugun sara gashi dare ya fara yi da ke yi, saboda tsabar tashin hankalin da yake ciki sai waige waige yake yi a tunaninshi ko zai hangota, yana cikin hakan ne ya ji wayarshi ta yi Virbration cikin sauri ya ɗaukota tsammanin Hajiya ce zata sanar da shi cewa ya dawo an ganta, sai kawai ya ji Muryar Zee tana kuka tana faɗin
"Munafukin banza baƙin mayaudari ashe daman kai maƙaryaci ne ban sani ba? To asirinka ya tonu yau gaskiya ta fito labarin aurenka ya zo kunnuwana, ashe daman cen kana da Mata shine ka ɓoye man, to ka sani na tsaneka na tsaneka tsana mafi muni a rayuwata"
Ƙitttt ta kashe wayar, cikin wani sabon tashin hankalin da ya ƙara ziyartoshi ba shiri ya kai zaune daɓas ƙasa dafe da kai yace
"Kai wannan bala'in da me ya yi kama wayyo ALLAHna khadija ina zan ganki WALLAHi ina sonki don ALLAH ki dawo gareni plss!"
Ni ma dai tashin hankalin yasa alkalamina ya faɗi ba shiri🙀
Akafta🤪
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Kar kuji komai allurar ƙarfi aka yi man😂😂😂😂😂shiyasa na zauce hannuna ya HAUKACE yana ta suburbuɗo maku typing, ku sha sha'aninku kawai kafin Nima in sha nawa idan allurar ta sakeni yasin😝*
*Lamba ta 49*
Dijen Baffah kam tunda ta fito ɗakinshi ta nufi ɗakinsu cikin dubarar rufe fuskarta da ɗankwalin doguwar rigar da ke jikinta, ta ɗauko jakarta da kuɗin liƙinta suke ciki ta rataya, ta fito kamar wacce zata shiga wurin walimar ta fice gidan cikin sauri ta tare Napep ta haye sai babbar tasha, ta ce motar garinsu take nema aka ce da ita sai dai ta Gombe idan taje sai ta shiga motar Kano, daga cen sai ta shiga motar da zata kaita babban birnin garinsu, cikin rashin tsoro ta faɗa motar jikinta yana rawa ta tambayi kuɗin motar aka faɗa mata ta biya, da aka zo wajen rubuta suna da numbar waya kamar tasan za'a nemeta ta rubuta sunan ƙarya da numbobin banza, tunda ita ko wayar ma bata da bale ta yi number, zuwanta bai wuce minti goma ba motar ta cika suka tafi don ko da tara na dare ta buga tana garin Gombe, sai da aka je cen ne wani tsoro ya shigeta saboda batasan inda zata je ta kwana ba, ta rakuɓe gefen wata mota tana ta sharar ƙwallah saboda motar da taga za'a hau a lokacin kuma a ce wai tafiya za'a yi cikin daren, tana nan tsaye sai ga wani ɗan union ya zo yana faɗin
"Ina zaki je ne Kano ko Kaduna ko Bauchi Sokoto ko Zamfara?"
Dije ta yi saurin goge ƙwallarta tace "kano"
Yace "to zo mu je ga motocin Kano cen ina kayanki?"
Tace "babu"
Ya yi saurin waigowa yace, "bangane babu ba an sace kayan ne ko yaya?"
Ta ce "bani da kaya"
Ya ce ",to ai sai ki yi bayani yanda zan gane zo mu je kar motar ta tashi don ta kusa cika"
Dije ta bi bayanshi har inda motar take aka yi mata mazauni ta yi tsalle ta shige saboda ƙatuwar mota ce, ta sami wuri ta rakuɓe tana muzurai saboda tsoron yanda za'a bi hanyar zuwa wani gari cikin daren, zamanta ba wuya aka tada motar suka kama hanya, tafe take tana addu'ar ALLAH ya kaisu lafiya har bacci ya yi awon gaba da ita, ga masifar yunwar da ta addabeta don rabonta da abinci tun Yola.
Zee ta washe baki ta ce "ƙyaleshi my cuddle bear nasan kishi ne yake taya Abokinshi bayan ni na riga da na yi masu nisa sai dai haƙuri"
Kamal ya yi mata wani kallo cike da jin haushin irin cin amanar da zata yi wa Abokinshi yace, "ita dai gaskiya idan ta tashi fita tafin hannu ya yi kaɗan da ya kareta, haka duk wanda ya ci amana to ya sani akwai lokacin da ranar sakamako zata ziyartoshi, ni kinga tafiyata fatana kawai ita Uwargidan ALLAH ya bata haƙurin sammakon da za'a yi mata"
Yana ƙare faɗar haka ya wuce abinshi, daga Safwan har ita Zee suka bishi da wani kallo mai ƙumshe da harara, ran Zee a jagule ta kalli Safwan ta ce"
"My hero Wai me yasa a ko'ina sai an samu yan adawa ne?, Ji don ALLAH yanda yake wani zaƙewa sai kace shine Aminun?"
Safwan ranshi a ɓace yace, "shareshi kawai hassada ce zo muje ki yi sallama da Hajiya mu je in raka ku gida tun kafin wannan magulmacin ya ɓata muna tsari"
Ya yi gaba Zee tare da janyo hannun ƙawarta amman sai Ruma ta ce da ita su je kawai ita zata jirasu, suna shigewa Ruma ta yi wurin Kamal zuciyarta cike da son jin gaskiyar abunda yake son sanar da Zee, ta nemi izinin ganinshi na ɗan lokaci suka keɓe gefe, Ruma ta zama serious bayan sun ƙare ɗan barkwancin da suka saba tace
"Kamal don ALLAH ka sanar da ni gaskiyar zance shin da gaske Man ɗin Zee yana da aure?"
Kamal ya yi yar gajeruwar dariya yace, "tunda kince ALLAH to ba wani kwana da zan tsaya yi maki, tabbas Safwan yana da Mata asali ma yanzu haka shekararshi biyu cikin ta uku da aurensu"
Ruma ta zaro ido waje tace, "Kamal kasan dai bamu irin wannan wasar da kai ko?, tsakaninka da ALLAH na roƙeka ka faɗa mani gaskiyar lamarin, saboda WALLAHi Zee ta mato sosai akan wannan guy ɗin idan har ta ji wannan magana nasan ba ƙaramin tashin hankali zata shiga ba"
Kamal ya karkace baki yana dariyar gefe idonshi suka kai ga Surayya da ke ta ɗaukar hotuna da Ƙawayenta ya yafitota da hannu, ta nufoshi tana dariya kasancewar tasanshi sosai saboda tare suka yi karatu da Safwan a garin, asali ma kamar gidan suke dukansu har da Lawi a lokacin da suka yi karatun jami'arsu.
Tana zuwa ta gayar da shi a mutunce bayan sun gaisa ya ce da ita, "Surayya ki yi mata bayanin gaskiya saboda ta ji da kunnuwanta, shin da gaske Safwan yana da aure ko kuwa?"
Surayya ta washe baki tace, "ALLAH sarki ƴar uwa da gaske kuwa Yayanmu yana da aure kuma yana bala'in son Matarshi, haka itama kuma tana sonshi sosai"
Diirim! dum! Shine abunda zuciyar Ruma ta yi saboda maganar ba ƙaramin bugun zuciyarta ta yi ba, nan take ta fara tausayin ƙawarta cikin canzawar yanayinta da ya koma kalar damuwa ta ce
"ALLAH sarki ko zaki iya nuna mani matar in ganta don ALLAH"
Surry tace, "bari in dubota don tun ɗazu ma ban ganta ba"
Surry ta yi cikin gidan zuciyarta cike da fatar ALLAH yasa ma auren ya wargaje kowa ma ya huta, sai dai duk bulayin neman Dijen da ta yi bata ganta ba, dole ta dawo da nufin sanar da ita cewa bata ganta ba, sai ga shi ma ta taradda su duka har da Safwan ɗin suna sallama da juna, saboda Ruma bata nuna komi ba nufinta sai sun je masaukinsu ta sanar wa da ƙawarta gaskiyar zancen.
Cikin tsoro Surry ta yi saurin komawa cikin gidan ta laɓe, har suka fita Gate ɗin gida Safwan ya bi su a baya sannan ta fito tana sauke ajiyar zuciya.
To sai dai abu kamar wasa har dare anata neman Dijen Baffah ammsn ba'a ganta ba, tun ana ɗaukar abun wasa har kowa hankalinshi ya fara tashi don kuwa anyi nemanta ko'ina gidan kaf ba'a ganta ba, Hajiya ta firgice sosai sai kiran Safwan take yi akan ta ji shin yana tare da Dijen ko kuwa, amman bai ɗauka ba saboda bai ma san ta kirashi ba don wayar a silen take, sai bayan ya gama firarshi da Zee ne Suka yi sallama yana kan hanya ya ga tarin miss calls na Hajiyar da su Surry da wasu ƴan uwansu duka, cikin tashin hankali ya dannawa Hajiyar kira sai ko ta yi caraf ta ɗauka, ba tare da ta jira jin abinda zai faɗa ba ta ce
"Ina khadija kuna tare da ita ne?"
Safwan a firgice yace "A'a WALLAHi Ni tun ɗazu rabon da na ganta"
Hajiyar ta yi saurin faɗin ka yi gaggawar nemota duk inda take, saboda an duba kaf gidan nan ba'a ganta ba, kuma jikina yana bani kai ne ka yi mata abunda ya janyo ta bar gidan, WALLAHi ka ji na rantse matuƙar baka nemo man ita ba to ko kada ka kuskura ka tako ƙafarka cikin gidan nan".
Kitt! Ta kashe wayar zuciyarshi cike da tashin hankali ya furta "Innalilahi wa'Inna ilairraji'un"
Cikin ruɗewa ya nufi tasha saboda cen zuciyarshi ta hasko masa zata nufa, saboda cewar da ta yi masa bata son karatun ita garinsu zata koma, sai dai kuma duk iya binciken da aka yi tashar babu sunan Khadija Umar a cikin jerin list ɗin mutanen da Motarsu ta tashi ranar a tashar, ya fito a gigice ya nufi wata ƙaramar tashar da ake shiga Mota nan ma ba wani alamun ta je cen, haka ya yi ta zagayen wuri wuri amman ko mai kama da ita bai gani ba, dole ya yi parking ya fito dafe da kanshi da ke yi masa mugun sara gashi dare ya fara yi da ke yi, saboda tsabar tashin hankalin da yake ciki sai waige waige yake yi a tunaninshi ko zai hangota, yana cikin hakan ne ya ji wayarshi ta yi Virbration cikin sauri ya ɗaukota tsammanin Hajiya ce zata sanar da shi cewa ya dawo an ganta, sai kawai ya ji Muryar Zee tana kuka tana faɗin
"Munafukin banza baƙin mayaudari ashe daman kai maƙaryaci ne ban sani ba? To asirinka ya tonu yau gaskiya ta fito labarin aurenka ya zo kunnuwana, ashe daman cen kana da Mata shine ka ɓoye man, to ka sani na tsaneka na tsaneka tsana mafi muni a rayuwata"
Ƙitttt ta kashe wayar, cikin wani sabon tashin hankalin da ya ƙara ziyartoshi ba shiri ya kai zaune daɓas ƙasa dafe da kai yace
"Kai wannan bala'in da me ya yi kama wayyo ALLAHna khadija ina zan ganki WALLAHi ina sonki don ALLAH ki dawo gareni plss!"
Ni ma dai tashin hankalin yasa alkalamina ya faɗi ba shiri🙀
Akafta🤪
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Kar kuji komai allurar ƙarfi aka yi man😂😂😂😂😂shiyasa na zauce hannuna ya HAUKACE yana ta suburbuɗo maku typing, ku sha sha'aninku kawai kafin Nima in sha nawa idan allurar ta sakeni yasin😝*
*Lamba ta 49*
Dijen Baffah kam tunda ta fito ɗakinshi ta nufi ɗakinsu cikin dubarar rufe fuskarta da ɗankwalin doguwar rigar da ke jikinta, ta ɗauko jakarta da kuɗin liƙinta suke ciki ta rataya, ta fito kamar wacce zata shiga wurin walimar ta fice gidan cikin sauri ta tare Napep ta haye sai babbar tasha, ta ce motar garinsu take nema aka ce da ita sai dai ta Gombe idan taje sai ta shiga motar Kano, daga cen sai ta shiga motar da zata kaita babban birnin garinsu, cikin rashin tsoro ta faɗa motar jikinta yana rawa ta tambayi kuɗin motar aka faɗa mata ta biya, da aka zo wajen rubuta suna da numbar waya kamar tasan za'a nemeta ta rubuta sunan ƙarya da numbobin banza, tunda ita ko wayar ma bata da bale ta yi number, zuwanta bai wuce minti goma ba motar ta cika suka tafi don ko da tara na dare ta buga tana garin Gombe, sai da aka je cen ne wani tsoro ya shigeta saboda batasan inda zata je ta kwana ba, ta rakuɓe gefen wata mota tana ta sharar ƙwallah saboda motar da taga za'a hau a lokacin kuma a ce wai tafiya za'a yi cikin daren, tana nan tsaye sai ga wani ɗan union ya zo yana faɗin
"Ina zaki je ne Kano ko Kaduna ko Bauchi Sokoto ko Zamfara?"
Dije ta yi saurin goge ƙwallarta tace "kano"
Yace "to zo mu je ga motocin Kano cen ina kayanki?"
Tace "babu"
Ya yi saurin waigowa yace, "bangane babu ba an sace kayan ne ko yaya?"
Ta ce "bani da kaya"
Ya ce ",to ai sai ki yi bayani yanda zan gane zo mu je kar motar ta tashi don ta kusa cika"
Dije ta bi bayanshi har inda motar take aka yi mata mazauni ta yi tsalle ta shige saboda ƙatuwar mota ce, ta sami wuri ta rakuɓe tana muzurai saboda tsoron yanda za'a bi hanyar zuwa wani gari cikin daren, zamanta ba wuya aka tada motar suka kama hanya, tafe take tana addu'ar ALLAH ya kaisu lafiya har bacci ya yi awon gaba da ita, ga masifar yunwar da ta addabeta don rabonta da abinci tun Yola.