Sashe 71
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Safwan ya dafe kanshi da ke ta sara masa ya ce, "ai kuma yanzu sai dai ta bi wasu shanun don nikam WALLAhi saki uku ringis zan dannawa shegiya, don bana fatar ko a hanya in sake haɗuwa da ita bale ta sake zama gidana"
Surayya ta yi saurin faɗin, "hukuncin da ya dace ita kenan baƙar arniya mai zuciyar kafuran farko"
Hajiya Mama ta maka mata wata harara Surayya ta ce,. "Haba Hajiyarmu yanzu da ace ta kashe muna su ai da mu ta bari da shiga uku, don duk hukuncin da za'a yi mata ba lalle ne ya zama dai dai da abunda ta aikata ba"
A harzuƙe Husnah tace "Ni WALLAHI na ma so mun illata shegiya kafin Auncle ya zo"
Aunty Ummi ta ce "ai WALLAHI da ace ina kusa sai na ja shegiya na damalmala kanta cikin fetur ɗin sannan in fito da ita tsakar gidan nan in ƙyasta mata ashanar sai ta ci wutar ƴar shegiya"
Hajiyarmu ta yi saurin faɗin "to kenan da ke da ita duk hukuncinku ɗaya in har kika aika wannan shirmen, yanzu dai abu ɗaya ya rage ka kira Mahaifinta ka sanar da shi abunda ke faruwa"
Safwan ya ɓata fuska ya ce "Ƴan'uwanta da aka yi a gabansu miye amfaninsu da ba zasu sanar da su abunda yake faruwa ba?"
Hajiyarmu ta ɓata fuska ta ce, "kaine ke da haƙƙin sanar da su ba wasu ba, saboda haka ka kirasu yanzu ka sanar da su abunda ke faruwa"
Safwan cike da jin haushi ya ɗaga waya ya kira Daddyn Zee ba tare da jiran komi ba ya ce
"Na saki Zee saki biyu a bisa sunnah da in ana yin ɗari duk sai nayi mata, don haka ayi gaggawar zuwa a kwashe mani tarkacen kayanta cikin gidana"
To fa 😳😳😳kai ko Malam Safwanu saki haka da sauri 😔
Akafta🙌🏻
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Am sorry fo you my FANS😊 jiya kun ji Ni shiru ko? To ku yi haƙuri yanzu gani tare da ku😸fatana kawai ku biyoni mu je🏃🏻♀️*
*Lamba ta 65*
Yana ƙare maganar ya kashe wayar cikin fushi ya miƙe zai bar falon Hajiya Mama ta kira sunanshi a hankali cikin wata murya mai cike da alhini, ba shiri ya waigo ta ce da shi ya dawo ya zauna, sannan ya dawo ya zauna sai wani cika yake yi alamun a wuya ya ke sosai, Hajiya Mama ta sake kiran sunanshi ta ce
"Abunda na ce ka aikata kenan? Me yasa kai a koda yaushe baka iya dafa mutum cikin ruwan sanyi ba?, Nasan Zainab bata kyauta ba amman shi mahaifinta laifin me ya yi da har zaka yi masa wannan cin fuskar?, Yanzu idan kai ne a matsayinshi wani ya kiraka ya saki ƴarka irin haka wane irin hali kake tsammanin zaka shiga?, To bari ka ji banji daɗin abunda ka aikata ba, don Mahaifinta komi lalacewarshi ya gama maka komi tunda har ya ɗauki ɗiyarshi ya baka, don haka ka sani laifin wani baya shafuwar wani, saboda shi mutum daraja gareshi mussaman wanda ya ke sama da kai irin haka, saboda haka ka dinga kwatanta adalci akan duk wanda mu'amala ta haɗaka da shi, don da ace ka yi cuta gara ace kai ne aka cuta, don yanzu wannan abun da ka yi masa har abada ba zai taɓa mantawa ba, tabbas kam ƴarshi bata yi abunda ya dace ba amman ka sani kai ka yi abunda ya fi wanda ta aikata muni"
Safwan da su Aunty Ummi Suka kallota cikin mamaki ta ce
"Eh tabbas haka ne don ita da makami ta yi niyya kasheka cikin fushi, kai kuka ka yi amfani da dafin harshe ka caki ubanta da mummunar maganar da dole ne ta daki zuciyarshi, ko baki ji ance dafin harshe ya fi na takobi zafi ba?, to bari ka ji yanzu wannan raunin da ta ji maka a hannu zai iya warkewa har wurin ya koma tamkar ma ba'a yi, amman dafin abunda ka yi wa mahaifinta ka sani har abada ba zai taɓa goguwa a cikin zuciyarshi ba, saboda haka ka daina yanke hukunci cikin fushi a koda yaushe idan har kasan abunda zaka faɗa ba mai kyau bane, to ka yi ƙoƙarin danne zuciyarka ka yi shiru saboda faɗar Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama da ya ce(falyaƙul khairan auliyasmut, ka faɗi alkhairi ko ka yi shiru) saboda shi baki dafi ne da shi wanda idan aka yi maka wata mummunar magana har abada ba zaka taɓa mantawa da ita ba"
Safwan ya shafo kanshi da hannunshi mai lafiya ya ce "na yi kuskure Hajiyarmu kuma Insha ALLAH bazan sake maimaita kwatankwacin hakan ba...."
Kiran wayar Safwan ce ta katse maganar da yake yi, cikin sauri ya duba mai kiran sai ga shi da kallo Hajiyar cikin sauri ya ce
"Mahaifinta ne"
Hajiyarmu ta ce
"Ka ɗauka ka ji to"
Ya ɗaga ba tare da ya ce ƙanzil ba ya saka hands free, sai ga muryar Mahaifiyar Zee cikin wayar tar! tar! tana kuka tana faɗin
"Me ke faruwa ne? Me ya sami Zainab ɗin ne? ga Daddynta nan ya faɗi rai a hannun ALLAH sai sunanta ya ke kira, me ke faruwa ne na ce?"
Ta ƙare maganar cikin kuka tare da ɗaga murya Hajiya Mama ta yi masa nuni da hannu alamun ya sanar da ita, cikin sanyin jiki ya fayyace mata abunda ya faru a dunƙule, mahaifiyarta ta fasa wata uwar ƙara tare da cewa
"Innalilahi wa'Inna ilairraji'un, Allahumma ajirni fi musibati wa alkhalifni khairun minha"
Sannan ta kashe wayar gaba ɗaya jikin kowa ya yi sanyi, ran Hajiyar a matuƙar ɓace cikin tagumi ta ce "ka ga abunda nike sanar da kai ko? To idan har ka yi sanadin mutuwarshi sai kasan abunda zaka faɗawa ALLAH idan kun je lahira"
Hajiyar Mama ta miƙe cikin fushi zata fita ya yi saurin shan gabanta yana bata haƙuri tare da su Aunty Ummi, Dije ta duƙa ƙasa ta riƙo leɓen zanenta cikin kuka ta ce
"Ki yi haƙuri Hajiyarmu kada ki fushi da Malam don ALLAH ki yafe masa"
Hajiyar ta duƙa ta ɗagota tare da share mata hawayen da suke ta zuba a idonta ta ce, "komi ya wuce na haƙura insha ALLAHu amman matuƙar yana son in yafe masa to sai ya furta ya mayar da Zainab a matsayin matarshi"
Dije da su Aunty Ummi da shi kanshi suka zaro ido waje saboda bugawar da zuciyoyinsu suka yi, cikin tabbatarwa ta sake ce wa "haka na ce kuma haka ni ke son ayi don hakan kawai zai rage raɗadin baƙin cikin abunda zai faru ga mahaifinta, wanda ko kaɗan bani fatar ace kai ne ka yi silar mutuwarshi da hannunka, duk da bana fatar hakan amman ka sani duk ya mutu a sanadin wautarka to baka yi wa kanka adalci ba"
Safwan da su Aunty Suka yi shiru kowa da nazarin da yake yi a zuciyarshi, Dije ta je gabanshi tare da haɗa hannuwa biyu alamun roƙo ta ce
"Don Allah Malam ka dawo da ita a matsayin matarka plss"
Cikin tsananin ɓacin rai ya ce "na dawo da ita da sauran igiya ɗayar da ta rage a tsakaninmu, amman WALLAhi bazan taɓa yafe mata abunda ta aikata man ba"
Yana ƙare faɗar hakan ya bar wajen cikin ƙunar zuciya, Hajiyar ma ta ce da su Aunty Ummi su zo su tafi gida, kasancewar isha ma ta wuce kuma ga shi wasu cikinsu ko SALLAHr magrib ma ba su yi ba, har bakin motar da ta kawosu Surayya da Dije suka rakasu, bayan sun tafi ne itama Surayya ta kira Mijinta ya zo ya ɗauketa, Dije ta nufi ɗakinta ta yi sallolinta sannan ta nufo ɗakinshi da ke sashenta, inda ta taraddashi zaune akan carpet fuskar haɗe ya yi shiru alamun ya faɗa cikin dogon nazari, ta sami gefenshi ta zauna tare da riƙo hannunshi mai yankuwa ta ɗora saman jikinta, cikin sanyin murya ta ce
"Don Allah ka daina wannan damuwar komi da ka ganshi daman cen rubuce yake mune ba mu sani ba, sai abun ya faru ne mu ke ganinshi tamkar sabon abu, don ALLAH Malam ka daina wannan damuwar WALLAhi bana son ganinta a fuskarka ni dai"
Safwan ya kallota da jajayen idonshi da suka rine saboda tsabar ɓacin rai ya ce "Ta ya bazan yi damuwa ba? Bayan Hajiyarmu ta sani mayar da wannan matar bala'i cikin rayuwarmu,yanzu ta sami damar yin haka ina ga abunda zata aikata a gaba? Hajiyarmu me yasa ta kasa gano Zainab ba alkhairi ce ga rayuwarmu ba? To Wallahi ko da ace zata dawo ɗin to ni kuma bazata taɓa jin daɗin zama da ni ba, sai ta bar gidan nan da ƙafafuwanta ba tare da ta shirya ba"
Dije ta yi saurin kwantawa saman kafaɗarshi cikin muryar kuka ta ce
"Ni dai ka yi haƙuri don ALLAH Malam saboda Hajiyarmu bazata taɓa cewa ka yi abunda bai dace ba kai ma ka sani?"
Safwan ya shafo kanta cikin tausayinta ya ce "wai waye malamin? Ni fa bana son wannan sunan na fara gajiya da shi, don bazan yarda ki mayar da ni tamkar wani tsoho ba, amman ki daina kukan nan bana sonshi"
Ya ƙare maganar tare da goge mata hawayen da ke ta kwaranya akan fuskarta, saboda zafin dawo da Zee ɗin da ya yi har cikin zuciyarta bata ji daɗin hakan ba, amman bata son ta nuna ne don kada aga rashin kyautawarta, amman ta ci alwashin duk ranar da ta dawo ita kuma a ranar zata bar gidan don bazata zauna ba ta kasheta a banza ba, Dijen ta ɗago fuskarta tare da saka hannu ta share hawayenta sannan ta ce
"Mu je mu ci abinci"
Ya bita da kallon mamaki ya ce " Ke kina jin yunwa ne?"
Ta ɗaga masa kai, ya ce "magana za ki yi" cikin siriryar murya ta ce "Eh" sannan ya miƙe suka fito ɗakin har zata cire hijabin da ke jikinta ya ce ta barshi fita za su yi, ta biyoshi a baya suka shiga Mota kai tsaye ya ja suka fice.
Surayya ta yi saurin faɗin, "hukuncin da ya dace ita kenan baƙar arniya mai zuciyar kafuran farko"
Hajiya Mama ta maka mata wata harara Surayya ta ce,. "Haba Hajiyarmu yanzu da ace ta kashe muna su ai da mu ta bari da shiga uku, don duk hukuncin da za'a yi mata ba lalle ne ya zama dai dai da abunda ta aikata ba"
A harzuƙe Husnah tace "Ni WALLAHI na ma so mun illata shegiya kafin Auncle ya zo"
Aunty Ummi ta ce "ai WALLAHI da ace ina kusa sai na ja shegiya na damalmala kanta cikin fetur ɗin sannan in fito da ita tsakar gidan nan in ƙyasta mata ashanar sai ta ci wutar ƴar shegiya"
Hajiyarmu ta yi saurin faɗin "to kenan da ke da ita duk hukuncinku ɗaya in har kika aika wannan shirmen, yanzu dai abu ɗaya ya rage ka kira Mahaifinta ka sanar da shi abunda ke faruwa"
Safwan ya ɓata fuska ya ce "Ƴan'uwanta da aka yi a gabansu miye amfaninsu da ba zasu sanar da su abunda yake faruwa ba?"
Hajiyarmu ta ɓata fuska ta ce, "kaine ke da haƙƙin sanar da su ba wasu ba, saboda haka ka kirasu yanzu ka sanar da su abunda ke faruwa"
Safwan cike da jin haushi ya ɗaga waya ya kira Daddyn Zee ba tare da jiran komi ba ya ce
"Na saki Zee saki biyu a bisa sunnah da in ana yin ɗari duk sai nayi mata, don haka ayi gaggawar zuwa a kwashe mani tarkacen kayanta cikin gidana"
To fa 😳😳😳kai ko Malam Safwanu saki haka da sauri 😔
Akafta🙌🏻
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Am sorry fo you my FANS😊 jiya kun ji Ni shiru ko? To ku yi haƙuri yanzu gani tare da ku😸fatana kawai ku biyoni mu je🏃🏻♀️*
*Lamba ta 65*
Yana ƙare maganar ya kashe wayar cikin fushi ya miƙe zai bar falon Hajiya Mama ta kira sunanshi a hankali cikin wata murya mai cike da alhini, ba shiri ya waigo ta ce da shi ya dawo ya zauna, sannan ya dawo ya zauna sai wani cika yake yi alamun a wuya ya ke sosai, Hajiya Mama ta sake kiran sunanshi ta ce
"Abunda na ce ka aikata kenan? Me yasa kai a koda yaushe baka iya dafa mutum cikin ruwan sanyi ba?, Nasan Zainab bata kyauta ba amman shi mahaifinta laifin me ya yi da har zaka yi masa wannan cin fuskar?, Yanzu idan kai ne a matsayinshi wani ya kiraka ya saki ƴarka irin haka wane irin hali kake tsammanin zaka shiga?, To bari ka ji banji daɗin abunda ka aikata ba, don Mahaifinta komi lalacewarshi ya gama maka komi tunda har ya ɗauki ɗiyarshi ya baka, don haka ka sani laifin wani baya shafuwar wani, saboda shi mutum daraja gareshi mussaman wanda ya ke sama da kai irin haka, saboda haka ka dinga kwatanta adalci akan duk wanda mu'amala ta haɗaka da shi, don da ace ka yi cuta gara ace kai ne aka cuta, don yanzu wannan abun da ka yi masa har abada ba zai taɓa mantawa ba, tabbas kam ƴarshi bata yi abunda ya dace ba amman ka sani kai ka yi abunda ya fi wanda ta aikata muni"
Safwan da su Aunty Ummi Suka kallota cikin mamaki ta ce
"Eh tabbas haka ne don ita da makami ta yi niyya kasheka cikin fushi, kai kuka ka yi amfani da dafin harshe ka caki ubanta da mummunar maganar da dole ne ta daki zuciyarshi, ko baki ji ance dafin harshe ya fi na takobi zafi ba?, to bari ka ji yanzu wannan raunin da ta ji maka a hannu zai iya warkewa har wurin ya koma tamkar ma ba'a yi, amman dafin abunda ka yi wa mahaifinta ka sani har abada ba zai taɓa goguwa a cikin zuciyarshi ba, saboda haka ka daina yanke hukunci cikin fushi a koda yaushe idan har kasan abunda zaka faɗa ba mai kyau bane, to ka yi ƙoƙarin danne zuciyarka ka yi shiru saboda faɗar Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama da ya ce(falyaƙul khairan auliyasmut, ka faɗi alkhairi ko ka yi shiru) saboda shi baki dafi ne da shi wanda idan aka yi maka wata mummunar magana har abada ba zaka taɓa mantawa da ita ba"
Safwan ya shafo kanshi da hannunshi mai lafiya ya ce "na yi kuskure Hajiyarmu kuma Insha ALLAH bazan sake maimaita kwatankwacin hakan ba...."
Kiran wayar Safwan ce ta katse maganar da yake yi, cikin sauri ya duba mai kiran sai ga shi da kallo Hajiyar cikin sauri ya ce
"Mahaifinta ne"
Hajiyarmu ta ce
"Ka ɗauka ka ji to"
Ya ɗaga ba tare da ya ce ƙanzil ba ya saka hands free, sai ga muryar Mahaifiyar Zee cikin wayar tar! tar! tana kuka tana faɗin
"Me ke faruwa ne? Me ya sami Zainab ɗin ne? ga Daddynta nan ya faɗi rai a hannun ALLAH sai sunanta ya ke kira, me ke faruwa ne na ce?"
Ta ƙare maganar cikin kuka tare da ɗaga murya Hajiya Mama ta yi masa nuni da hannu alamun ya sanar da ita, cikin sanyin jiki ya fayyace mata abunda ya faru a dunƙule, mahaifiyarta ta fasa wata uwar ƙara tare da cewa
"Innalilahi wa'Inna ilairraji'un, Allahumma ajirni fi musibati wa alkhalifni khairun minha"
Sannan ta kashe wayar gaba ɗaya jikin kowa ya yi sanyi, ran Hajiyar a matuƙar ɓace cikin tagumi ta ce "ka ga abunda nike sanar da kai ko? To idan har ka yi sanadin mutuwarshi sai kasan abunda zaka faɗawa ALLAH idan kun je lahira"
Hajiyar Mama ta miƙe cikin fushi zata fita ya yi saurin shan gabanta yana bata haƙuri tare da su Aunty Ummi, Dije ta duƙa ƙasa ta riƙo leɓen zanenta cikin kuka ta ce
"Ki yi haƙuri Hajiyarmu kada ki fushi da Malam don ALLAH ki yafe masa"
Hajiyar ta duƙa ta ɗagota tare da share mata hawayen da suke ta zuba a idonta ta ce, "komi ya wuce na haƙura insha ALLAHu amman matuƙar yana son in yafe masa to sai ya furta ya mayar da Zainab a matsayin matarshi"
Dije da su Aunty Ummi da shi kanshi suka zaro ido waje saboda bugawar da zuciyoyinsu suka yi, cikin tabbatarwa ta sake ce wa "haka na ce kuma haka ni ke son ayi don hakan kawai zai rage raɗadin baƙin cikin abunda zai faru ga mahaifinta, wanda ko kaɗan bani fatar ace kai ne ka yi silar mutuwarshi da hannunka, duk da bana fatar hakan amman ka sani duk ya mutu a sanadin wautarka to baka yi wa kanka adalci ba"
Safwan da su Aunty Suka yi shiru kowa da nazarin da yake yi a zuciyarshi, Dije ta je gabanshi tare da haɗa hannuwa biyu alamun roƙo ta ce
"Don Allah Malam ka dawo da ita a matsayin matarka plss"
Cikin tsananin ɓacin rai ya ce "na dawo da ita da sauran igiya ɗayar da ta rage a tsakaninmu, amman WALLAhi bazan taɓa yafe mata abunda ta aikata man ba"
Yana ƙare faɗar hakan ya bar wajen cikin ƙunar zuciya, Hajiyar ma ta ce da su Aunty Ummi su zo su tafi gida, kasancewar isha ma ta wuce kuma ga shi wasu cikinsu ko SALLAHr magrib ma ba su yi ba, har bakin motar da ta kawosu Surayya da Dije suka rakasu, bayan sun tafi ne itama Surayya ta kira Mijinta ya zo ya ɗauketa, Dije ta nufi ɗakinta ta yi sallolinta sannan ta nufo ɗakinshi da ke sashenta, inda ta taraddashi zaune akan carpet fuskar haɗe ya yi shiru alamun ya faɗa cikin dogon nazari, ta sami gefenshi ta zauna tare da riƙo hannunshi mai yankuwa ta ɗora saman jikinta, cikin sanyin murya ta ce
"Don Allah ka daina wannan damuwar komi da ka ganshi daman cen rubuce yake mune ba mu sani ba, sai abun ya faru ne mu ke ganinshi tamkar sabon abu, don ALLAH Malam ka daina wannan damuwar WALLAhi bana son ganinta a fuskarka ni dai"
Safwan ya kallota da jajayen idonshi da suka rine saboda tsabar ɓacin rai ya ce "Ta ya bazan yi damuwa ba? Bayan Hajiyarmu ta sani mayar da wannan matar bala'i cikin rayuwarmu,yanzu ta sami damar yin haka ina ga abunda zata aikata a gaba? Hajiyarmu me yasa ta kasa gano Zainab ba alkhairi ce ga rayuwarmu ba? To Wallahi ko da ace zata dawo ɗin to ni kuma bazata taɓa jin daɗin zama da ni ba, sai ta bar gidan nan da ƙafafuwanta ba tare da ta shirya ba"
Dije ta yi saurin kwantawa saman kafaɗarshi cikin muryar kuka ta ce
"Ni dai ka yi haƙuri don ALLAH Malam saboda Hajiyarmu bazata taɓa cewa ka yi abunda bai dace ba kai ma ka sani?"
Safwan ya shafo kanta cikin tausayinta ya ce "wai waye malamin? Ni fa bana son wannan sunan na fara gajiya da shi, don bazan yarda ki mayar da ni tamkar wani tsoho ba, amman ki daina kukan nan bana sonshi"
Ya ƙare maganar tare da goge mata hawayen da ke ta kwaranya akan fuskarta, saboda zafin dawo da Zee ɗin da ya yi har cikin zuciyarta bata ji daɗin hakan ba, amman bata son ta nuna ne don kada aga rashin kyautawarta, amman ta ci alwashin duk ranar da ta dawo ita kuma a ranar zata bar gidan don bazata zauna ba ta kasheta a banza ba, Dijen ta ɗago fuskarta tare da saka hannu ta share hawayenta sannan ta ce
"Mu je mu ci abinci"
Ya bita da kallon mamaki ya ce " Ke kina jin yunwa ne?"
Ta ɗaga masa kai, ya ce "magana za ki yi" cikin siriryar murya ta ce "Eh" sannan ya miƙe suka fito ɗakin har zata cire hijabin da ke jikinta ya ce ta barshi fita za su yi, ta biyoshi a baya suka shiga Mota kai tsaye ya ja suka fice.