← Book details Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 69 OF 84

Sashe 69

Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Am happy to see you my Husby, your welcome key to my life"

Daga Safwan ɗin har su Zee kasa ɗauke idonsu suka yi gareta saboda tsabar mamakin da ta ba su, duk da wani sashe na zuciyarshi yasan fiye da hakan ma zata iya aikatawa tunda har yasan kalar koyarwar da ya yi mata, sai dai ita Zee mamakinta ya Sha bambam da na shi don kuwa ita ƙarfin halin yarinyar take mamaki musamman da ta kirata ƙanwarta, amman kasancewar itama ɗin ba baya ba wajen kishi shiyasa ta yi saurin ɓoye kukan da ya zo mata ta nufi sashenta su Ruma suka dafe mata baya suka barsu anan ko waiwayensu bata sake yi ba.

Ganin hakan ya sa Safwan ɗin sakin jikin ya mayar mata da martanin sumbar da ta yi masa a leɓenta, sannan ya ɗora kanshi saman wuyanta ya kai mata wani zazzafan kiss ta yi saurin zullewa tare da riƙo hannunshi tana dariya ta ce

"Oya mu je daga ciki kada ka janyo muna abun magana gaban mutane"

Saboda yanda ma'aikatan suke ta satar kallonsu a fakaice ga kuma fiddo da ke tsaye itama, lura da hakan yasa ta hilatoshi suka shige sashenta, wanda shi biye da ita kawai yake amman sam gaba ɗaya ya manta kowa da komi sai ita, yana jin wani daɗi yana huda ko'ina na jikinshi saboda farin cikin ganinta, yau ga shi ga ma'ul hayatynshi Dijengalar Baffah kuma Black cat ɗin shi ada, wadda yanzu ta zamo masa fitilar da yake amfani da haskenta matuƙar yana son ya gane gabanshi.

Surayya da su Husnah da sauran wasu ma'aikatan gidan tuni suka kwashi kayan da Direba yake fitowa suka fara shigarwa sashen Zee, sannan suka koma sashen Dijen inda ita kam tuni ta shige da Mijinta ɗakin da yake mallakinshi a cikin sashen nata ta fara ɗorashi a saiti, don tun shigarsu ya janyota jikinshi ya fara yamutsata tare da aika mata da saƙunan kisses tamkar wani zautaccen mayen ƙarfe, ganin in ta biyeshi za su ɓata lokuta masu yawa yasa ta yi dubarar riƙe hannunshi cikin wani kallo ta ce

"Plss mu je ka yi wanka ku ci abinci kai da Amaryarka kada ta ɗaukeni mai rowa, don na tabbata dukanku kuna buƙatar abincin"

Ta mairaire fuska har da riƙe kunne alamun ban haƙuri sannan ya miƙe tare da dafe goshi yana yi mata kallon mamakin irin wayewar da ta yi masa ta bazata, sannan ya riƙo hannunta ya ce

"Wayo ko? To ai mu je ɗin sai ki tayani wankan don na fahimci so kike ma ki nuna kin fini girma"

Dije ta yi yar dariya sannan ta rufe fuska da hannu ɗaya ta ce

"Ni dai mu je ɗin kada ta ga an ƙyaleta"

Sannan suka je toilet ta haɗa masa komai zata fito ya ce ta jirashi amman daga nesa don baya son ta ɓata masa kwalliyar, ita ko ganin hakan yasa ta yi nazarin kawai ta taimaka masa tunda Surayya ta sanar da ita hakan ma yana ƙara shaƙuwa tsakanin ma'aurata, aiko ta saki jiki ta ajiye kunyar ta taimaka masa sai gata itama ya janyota suka faɗa ruwan ya yi nasarar cire mata kayan ya dinga mammatsewa tare da tanɗewa da lashe abubuwan da ya fi so a rayuwarshi, duk da take jin zafin zafin abunda ya ke yi amman ta nuna masa lalle itama ɗin yanzu ba da bace, da ƙyar ta lallaboshi suka fito toilet ɗin bayan dukansu sun tsalkake jikinsu.

Yana rama sallolin da suka kubce masa ne ta sulale ta wata ƙofar da ke sadata da ɗakinta ta sake yin wani sabon shiri cikin wani danƙareren less bulue black, Wanda aka yi wa ɗinkin riga da siket ya hau jikinta sosai, saboda ɗinkunan takanas Aunty Ummi ta ɗinka mata su Abuja don kawai ta ji daɗin tarbon Angonta, bayan ta kimtsa fess abunta sannan ta sake feshe jiki da turarukanta masu daɗin ƙamshin sannan ta koma wurinshi, yanda ya lalace da kallonta ne yasa ta ƙaraso wurinshi tare da hure masa ido da iskan bakinta ta ce

"It's time for lunch my dear"

Ya rungumota jikinshi yana lakuce mata dogon hancinta ya ce

"Ki godewa ALLAH idan har kinsa Malaminki ya zauce a kanki"

Ta yi wani yarr da ido ta ce "rufani ka saya ai sai ka janyo ace wannan ɗaliba ta wuce gona da iri idan har ta zarta sanin malaminta"

Ya sauke mata wani kiss a goshi sannan ya shirya cikin wasu kayanshi da aka ajiye a ɗakin, sannan ya riƙo hannunta suka fito suka nufi sashenshi da yake tsakiyar na su ita da Zee, inda acen ne ma suka kai komi da suka dafa saboda kawai a nunawa Zee cewa su sun san me suke yi, kuma wannan duk yana cikin shawarar Aunty Ummin da take ta baiwa Dijen akan neman zaman lafiyarta ita da abokiyar zamsnta, har zasu zauna kan diny ɗin Dije ta yi saurin ce wa

"Malam plss ka fito da Amarya ta zo mu haɗu ayi lunch don cikina har ya fara kiran ciroma"

Safwan yana ƴar dariya ya ce "sannu acici to jirani in zo minti ɗaya"

Sannan ya bi wata ƙofa ya yi sashen Zee inda ya taradda ita tare da ƴan uwanta biyun da ƙawarta Ruma da suka zo tarbarta, bayan sun sake gaisa ne ya ke cewa da ita ta zo su je aci abincin, ta nuna cewa ita sam bazata je ba ta riga da ta ci wanda su Ruma suka dafa mata, Ruma ta yi mata signal da ido sannan ta miƙe ta biyoshi ranta a haɗe saboda takaicinshi da take ji a zuciyarta tare da munafukar Matarshi a cewarta, wadda ta sha alwashin ko da bala'i sai ta fiddata gidan ta ƙarfin tsiya, tunda har ita zata nunawa kissa da kitifiri don salon kawo mata reni har da kiranta ƙanwarta wai, haka ta yi ta saƙe saƙen zucinta har suka shiga falon nashi, sai dai hango Dijen da ta yi tana ta Saving abinci a plates kala kala yasa ta ji wani bala'a'en kishi ya taso mata, musamman yanda ta ga har da wani sabon wankan ta sake yi don ta nuna mata cewa sunyi wani abu da Safwan ɗin, tunanin hakan yasa ta ja ta tsaya ta ƙi ƙarasawa wajen diny ɗin, ta rungume hannu tana yi mata wani kallo sai wani girgizar jiki take yi saboda a wuya take ƙiris take jira ayi wadda za'a yi.

Safwan ya ja kujera ya zauna Dijen ta janyo masa abinci a gabanshi tana dariya ta kalli Zee ta ce

"Ƙamshin girkina zai yi maki illa Amarya matuƙar baki yi gaggawar ƙarasowa ki ka fara cinshi ba"

Zee ta yi mata wani kallo sama da ƙasa mai cike da reni sannan ta buga wani uban tsaki tace

"Wahainiyarki ta kiyayi ramata tun wuri WALLAhi, ke ce matsiyaciya wadda abinci ya dama saboda haka ki je ki tambayo wacece Zee kafun ki fara yiwa mutane iyayin tsiya, baƙar munafukar banza annamimiya mai shiga tsakanin mata da mijinta, WALLAhi tun kafin in nuna maki wacece Ni ki kama kanki da ni"

Tana ƙare faɗar maganar ta yi masu wani mugun kallo sannan ta buga wani uban tsaki ta juya cikin fushi ta koma inda ta fito, Safwan kam sai cin abincinshi yake yi ba tare da ma ya nuna damuwarshi akan duk abunda ta faɗa ba, ya ɗago fuskarshi ya kalli Dijen ya wayance tare da faɗar

"Sakin bakin na minene? Ko zaki bita ki bata haƙuri ne? Saki jiki ki ci abincinki in har kina son farin cikina, to ki tattara komi ki ajiye a gefe ki fuskanci gabanki tare da Mijinki da ke kusa da ke, saboda haka dawo nan kusa da ni sai mun fi jin daɗin cin abincinmu"

Dije ta yi shiru sannan ta goge guntuwar ƙwallah da ta cika mata ido
ta dawo kujerar da ya ce, yana dariyar da iyakacinta fuska ya ciko spoon da abincin ya nufo bakinta, ta yi masa wani kallo zuciyarta cike da takaici ya girgiza mata kai ta yi saurin haɗiye kukanta.

Haka suka ci abincin kowane zuciya ba daɗi sai dai ba laifi sun ciyar da junansu sosai, sannan ya ja abarshi suka yi ɗakinshi inda ba ɓata lokaci ya fara saitata a hanya, kafin ka ce me shima ya fara rikicewa tare da zaucewa akan Dijenshi, don kuwa tun haɗuwar fatar jikinsu ya gano akwai banbanci tsakaninta da Zee sosai haka ma akwai tazara mai yawa a tsakaninsu, to balle da ya sami sa'ar shigewa fadar gwamnatinta sai ga shi da fasa wani ihun daɗi yana kuwwa, saboda gaba ɗaya ya zauce mata ni'imarta tasa ya kiɗime babu abunda ke fita bakinshi sai ihu da sambatun daɗi.

Zee kam tana cen su Ruma suna lallashinta ne ta jiyo ihunshi, cike da mamaki ta yi saurin dawowa falon sai dai fahimtar abinda yakewa ihun ne yasa ta dafe ƙirji ba shiri, tare da zuwa ƙofar ɗakin tana dukan ƙofar a haukace tana tsine masu dukansu.

Ganin kamar ba su ma san tana yi ba yasa ta bazama aguje ta yi ɗakin ajiyar fetur ta kinkimo jarkar ta fito da gudu kamar wata mahaukaciya, ma'aikatan gidan suka bita da kallo cike da mamaki duk da duhun magriba ya kawo jiki a lokacin.

Tana zuwa ta fara watsa fetur ɗin ta ko'ina cikin falon da ƙofar ɗakin tana surutan faɗin

"Sai na kasheku dukanku yau yan bura'uba azzulumai macuta, ALLAH ya tsine maku gaba ɗayanku WALLAHI yau sai na kasheku"

Ta yi sashenta aguje gudu ta ɗauko ashana su Ruma suka biyota da gudunsu don su ga abunda yake faruwa, tana zuwa ta kunna ashanar cikin bushewar zuciya ta cillata ƙofar ɗakin.

Wayyo ALLAHna😳🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️wuta 🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️wuta ku yo agaji🏃🏻‍♀️.

Akafta😝

D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*

*NA HADIZA D/AUTA*

*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
Chapter 69 · 0% Book details