Sashe 14
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ganin halin da yake ciki ne yasa Maigarin yaji tsoro yasa Lawi ya d'auki motarsu aka saka Safwan da wasu mutum biyu suka nufi Asibitin babban garin da suke karkashinshi, cikin gaggawa aka shiga dashi emergency room, Lawi da sauran mutanen duka sun yi jugum jugum saboda sun ji tsoron halin da Suka ga Safwan d'in ya shiga cikin kankanin lokaci.
Team Safwan ku garzayo ni kam nayi nan🏃🏻♀️🏃🏻♀️
Akafta🤾🏻♂️
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*ALHMDLLH Lalle dole ne in godewa ALLAH saboda Littafin Dije k'arangiya ya Kai in da Ni din ban isa in je ba, Na gode sosai mutanen Dije Ina yinku all dinku wallah💃🏻💃🏻💃🏻*
*Jinjinar ban girma gareki Kanwata ta gefen awazar damata waton HAJIYA DUDUWA Ina godiya da soyayyarki ga Littafin K'arangiya ALLAH ya bar zumunci tawan🥰🤝🏻*
*Lamba ta 14*
An d'auki lokaci kafin ayi nasarar dawo da numfashin Safwan dai dai, sannan aka kaishi d'akin hutu tare da makala masa ruwa in da shi yake ta barcinshi sharkaf yana ta sauke numfashi a hankali.
Daga Lawi har mutanen da suka zo da su sai a lokaciin hankalinsu ya kwanta, ganin ya dawo cikin natsuwarshi duk da har lokacin bai farfado ba, amman alamun nasarar da suka bayyana ne yasa suka ji natsuwa ta zo masu, a k'arshe dai Lawi ne ya kwana da shi su kuma suka juya suka koma kauyensu domin su sanarwa da Maigarin halin da ake ciki.
***
Dije kam ko da ta saka turaren ba gida ta yi ba lab'ewa tayi tana jiran taga ta ya abun zai kasance, aiko sai gashi tana jikin gini mak'e ta sha jinin jikinta ta fara jin yana ta dukan k'ofa, ta rufe bakinta saboda dariyar da ta sub'uce mata cike da jin dad'i ta k'ara bud'e kunnuwa domin ta ji me yake fad'a, jin yanata atishaya yasa ta fara tsallen jin dad'i ta nufi k'ofar da nufin ta bud'e katakon da ta rufe d'akin dashi ne ta jiyo takun talkami za'a zo, cikin firgici ta koma maboyarta cikin duhu ta lafe luf jikin ginin, sai dai abunda ya firgitata shine ganin an fito da Safwan rangai rangai yana wani numfashi sama sama, nan take jikinta ya d'auki rawa tare da gwalalo ido cikin tsananin tsoro ta biyo bayansu Lawi da sauran mutanen, ganin an sakashi a mota ana shawarar a kaishi Asibiti yasa ta zunduma aguje cikin tashin hankali ta nufi gidansu.
Aiko shigarta ke da wuya Inna ta fara balbaleta da fad'a akan ina ta fito cikin daren? kuma me ya fitar da ita?.
Dije ta yi tsuru tsuru tana warar idanuwa cikin tsoron abunda zai je ya dawo in har wani abin ya sami Safwan d'in, aiko ba shiri ta fashe da wani irin kukan tausayin su Innar, don tasan muddin ya mutu to daga ita har su sun shiga Uku don zaman duniyar ma sai ya gagaresu bale garin nadu, cikin Kuka ta fara fad'in
"WALLAHI Ni ban yi komi ba Inna don ALLAH ki yafe mani"
INNA Hasiya ta bita da kallo cikin duhun daren ta cafko hannunta cike da rud'ewa da jin tsoron in ba wani abu miyagun garin suka yi wa Dijenta ba, sai da ta d'auki wuk'a a kitchen sannan ta jata har kuryar d'akinta ta jefar da ita a tsakiyar d'akin, fuskarta a had'e ta nuna mata wuk'ar tace
"Zaki fad'a man abunda ya fitar da ke gidan nan ko ba zaki fad'a ba sai na kasheki an huta?"
Dije ta zaro ido tare da ja da baya tana kumshe kukanta Inna ma tana biyarta da wuk'ar zare da idanuwa kamar da gaske yankatan zata yi, Dije ta kai jikin bango ta fara kyarma tana fad'in
"WALLAHI Inna ban yi komi ba ki yarda dani"
Cikin b'acin rai Inna tace,. "Baki yi komi ba kika fita? Bayan kin San cewa Baffahnki ya hanaki fitar daren?yanzu haka ga Abincin Inna Gambo nan ajiye ina jiran Usman ya dawo ya kai mata, in da ina b'ukatar ki fitan ai sai a baki kije ki kai mata, zaki fad'a ko sai na yankaki d'in?? "
Inna ta nufota da wuk'ar saitin wuyanta Dije ta zaro Ido tare da fasa k'ara tace
"Wayyo Inna ki yi hak'uri wajen Dan birni naje na yi masa
turaren hayakin toshhi da kuka"
INNA ta dafe kirji tace
"La'ilaha illallahu Muhammadur'rasulullahi Dije kashemu zaki sa ayi a garin nan ne?me yayi maki kuma ya zu da zaki yi masa turaren mayu?"
Dije ta Sha jinin jikinta tana ajiyar zuciyar kuka tace,. "To Inna ba shi bane ya dakeni ranar"
Inna cikin fushi ta kai mata wani mangari tare da wata muguwar faka a baya tana fad'in,. "Ba sai da nace ki kyaleshi kar ki yi masa komi ba? Ashe duk nasihar da nayi maki ta bayan kunnuwanki ta bi ta wuce?, To ai kin kyauta kije ki yi abunda duk kika ga yafi maki tunda Ni kin maida maganata ba komi"
Tana k'are maganar ta fice ranta a matuk'ar bace tana fyace majinar kukan da ya zo mata ba shiri, Dije ta dunkule itama sai kukan take yi saboda har ga ALLAH taji tsoron halin da taga Safwan a ciki.
Ko da Baffah da Usman suka dawo Inna bata yi k'asa a gwiwa ba wajen zayyane masu komi, hankalin Baffah a tashe ya garzaya gidan Maigarin, in da ya taradda k'ofar gidan dank'am! Ana ta bi da zancen abunda ya faru, sai dai duk kashe kunnuwan da yayi bai ji ance Dije ce silar abun ba, hakan yasa shi sakin jiki ya baje anata cecekuce akan binciko wanene mai hannu akan faruwar lamarin, don har kwanon da Dije ta debo garwashin da shi sai da ya gani anata tuhumar inda kwanon ya fito, tare da zayyana irin abunda aka yi masa kwana biyu da suka wuce da Beraye, Wanda a iya bincike duk an bincika an tabbatar d'akin babu wani bera ko d'aya kafin faruwar hakan, ALLAH ya taimaka Safwan da Lawi basu fad'i cewa Dije ce ta aikata ba, to sai gashi yanzu ma ta sake kwatawa don kawai k'ok'arinta na rama abunda aka yi mata, don bata yafiya kuma bata manta ranar d'aukar fansa.
Baffah dai haka ya baje k'ofar Gidan Maigarin har wad'anda suka je kai Safwan Asibiti suka dawo, jin ba'asin samun nasara akan matsalar yasa ya yi sallama da su ya mamayi idanuwan Mutane ya dauke kwanon ya nufo gida da shi , Ko da ya shigo ranshi a b'ace ya wurgar da kwanon ya kalli Inna da ke cika tulunta da ruwan da Usman ya debo mata, yayi kwafa sannan yace
"Ki gaggauta jefa kwanon cen masai tun kafin bincike ya sa a gano Dije ce ta aikata wannan bak'in halin, don WALLAHI wannan karon kam ta jangwalo muna k'aton jidali, saboda yanzu haka fa yaron yana Asibiti sai da naji yanayin jikin nashi sannan na baro wajen"
Inna ta daina zuba ruwan ta yi tagumi tace,. "Ni WALLAHI na fara tunanin ko dai ayi wa Dije aure ne a huta?"
Baffah ya maka mata wata harara yace,
"WALLAHI ba wani aure da zan yi wa Dije yanzu tana yar shekara sha Uku, addu'ar nan dai da muke yi mata kullum to ita za mu ci gaba da yi ko yanzu, ina da tabbacin komi yayi tsanani to maganinshi ALLAH sarki, don haka yanzu ki yi gaggawar jefa kwanon cen a Masai mu huta da fad'uwar gaba"
Har ya fara tafiya ya waigo ya kalli Inna da tayi tagumi ta yi shiru tana nazarin mafita, cikin damuwa yace
"Ina ita Dijen?"
Inna ta yi masa nuni da hannunta akan cewa tana d'aki, Baffah ya nufi d'akin, Inna ta ja kafafuwanta ta d'auki kwanon ta nufi bayi ta jefashi sannan ta dawo cikin sanyin jiki ta k'arasa zuba ruwan ta nufo d'akinta, in da ta taradda Baffah ya ke ta balbale Dijen da ruwan fad'a kamar ya daketa, Dije kam sai kukanta take ta sharba tana ajiyar zuciya wata bayan wata.
Ranar dai haka mutanen gidan suka kwana kowane da abunda yake damunshi, Inna kam kwana ta yi tana rokarwa Dije shiriya tare da rokon ALLAH akan ya bata Miji nagari.
***
Malam Safwan kam sai da ya kwashi awanni sannan ya dawo cikin hankalinshi, in da ya kurawa Abokinshi Lawi idanuwa yana son ya gano tantagaryar abunda ya faru dashi, aiko sai gashi take yanke ya dinga kallon abun a cikin idanuwanshi in da Kai tsaye bayan k'are tunanin nashi zuciyarshi ta tabbatar masa da cewa Dije ce ta yi masa wanna aikin, cikin k'unar zuciya ya gyara kwanciyarshi ya kalli Lawi yace
"Yarinyar nan ko kad'an bata da imani kasheni take so ta yi abokina"
Lawi ya gyara zamanshi yace,. "Me yasa kake son d'orawa yarinyar nan laifin da ba ita ce ta aikata ba?"
Safwan ya k'ara b'ata fuskarshi yace,. "Yarinyar nan ko da ace kanwarka ce iya abunda zaka yi akanta kenan, ban san me yasa kake son kare yarinyar cen ba wai ko dai sonta kake yi ne Abokina?"
Lawi ya yi saurin girgiza kai yace,. "Ko d'aya Ni dai bana son ka dinga zarginta akan abunda ba ita ce ta yi ba, don takamar kaji cewa ta saka maka Beraye to ai wannan baka ji ta fad'a a bakin kowa ba, don haka ka daina zarginta kuma ka ajiye zaton cewa ita ce ka bi a hankali in har ita d'in ce zaka gano ai idan mun koma"
Safwan ya zaro Ido waje yace,. "Mu koma ina? Ai ni kam daga nan sai Gida don kam bazan koma bak'in kauyen nan ba, don na tsani ganin fuskar bak'ar shegiyar yarinyar nan, na tsaneta na tsaneta WALLAHI muddin ina ganinta to ko nine Nan zan yi ajalinta"
Lawi ya zaro ida cikin tsoron lafazin Safwan d'in, sannan ya kyalkyale da wata arniyar dariya yace
"Lalle ashe ko gaba da gabanta waton dai da gaske tsoronta kake ji Abokina, tunda har akanta zaka ajiye aikinka mai Muhimmanci"
Team Safwan ku garzayo ni kam nayi nan🏃🏻♀️🏃🏻♀️
Akafta🤾🏻♂️
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*ALHMDLLH Lalle dole ne in godewa ALLAH saboda Littafin Dije k'arangiya ya Kai in da Ni din ban isa in je ba, Na gode sosai mutanen Dije Ina yinku all dinku wallah💃🏻💃🏻💃🏻*
*Jinjinar ban girma gareki Kanwata ta gefen awazar damata waton HAJIYA DUDUWA Ina godiya da soyayyarki ga Littafin K'arangiya ALLAH ya bar zumunci tawan🥰🤝🏻*
*Lamba ta 14*
An d'auki lokaci kafin ayi nasarar dawo da numfashin Safwan dai dai, sannan aka kaishi d'akin hutu tare da makala masa ruwa in da shi yake ta barcinshi sharkaf yana ta sauke numfashi a hankali.
Daga Lawi har mutanen da suka zo da su sai a lokaciin hankalinsu ya kwanta, ganin ya dawo cikin natsuwarshi duk da har lokacin bai farfado ba, amman alamun nasarar da suka bayyana ne yasa suka ji natsuwa ta zo masu, a k'arshe dai Lawi ne ya kwana da shi su kuma suka juya suka koma kauyensu domin su sanarwa da Maigarin halin da ake ciki.
***
Dije kam ko da ta saka turaren ba gida ta yi ba lab'ewa tayi tana jiran taga ta ya abun zai kasance, aiko sai gashi tana jikin gini mak'e ta sha jinin jikinta ta fara jin yana ta dukan k'ofa, ta rufe bakinta saboda dariyar da ta sub'uce mata cike da jin dad'i ta k'ara bud'e kunnuwa domin ta ji me yake fad'a, jin yanata atishaya yasa ta fara tsallen jin dad'i ta nufi k'ofar da nufin ta bud'e katakon da ta rufe d'akin dashi ne ta jiyo takun talkami za'a zo, cikin firgici ta koma maboyarta cikin duhu ta lafe luf jikin ginin, sai dai abunda ya firgitata shine ganin an fito da Safwan rangai rangai yana wani numfashi sama sama, nan take jikinta ya d'auki rawa tare da gwalalo ido cikin tsananin tsoro ta biyo bayansu Lawi da sauran mutanen, ganin an sakashi a mota ana shawarar a kaishi Asibiti yasa ta zunduma aguje cikin tashin hankali ta nufi gidansu.
Aiko shigarta ke da wuya Inna ta fara balbaleta da fad'a akan ina ta fito cikin daren? kuma me ya fitar da ita?.
Dije ta yi tsuru tsuru tana warar idanuwa cikin tsoron abunda zai je ya dawo in har wani abin ya sami Safwan d'in, aiko ba shiri ta fashe da wani irin kukan tausayin su Innar, don tasan muddin ya mutu to daga ita har su sun shiga Uku don zaman duniyar ma sai ya gagaresu bale garin nadu, cikin Kuka ta fara fad'in
"WALLAHI Ni ban yi komi ba Inna don ALLAH ki yafe mani"
INNA Hasiya ta bita da kallo cikin duhun daren ta cafko hannunta cike da rud'ewa da jin tsoron in ba wani abu miyagun garin suka yi wa Dijenta ba, sai da ta d'auki wuk'a a kitchen sannan ta jata har kuryar d'akinta ta jefar da ita a tsakiyar d'akin, fuskarta a had'e ta nuna mata wuk'ar tace
"Zaki fad'a man abunda ya fitar da ke gidan nan ko ba zaki fad'a ba sai na kasheki an huta?"
Dije ta zaro ido tare da ja da baya tana kumshe kukanta Inna ma tana biyarta da wuk'ar zare da idanuwa kamar da gaske yankatan zata yi, Dije ta kai jikin bango ta fara kyarma tana fad'in
"WALLAHI Inna ban yi komi ba ki yarda dani"
Cikin b'acin rai Inna tace,. "Baki yi komi ba kika fita? Bayan kin San cewa Baffahnki ya hanaki fitar daren?yanzu haka ga Abincin Inna Gambo nan ajiye ina jiran Usman ya dawo ya kai mata, in da ina b'ukatar ki fitan ai sai a baki kije ki kai mata, zaki fad'a ko sai na yankaki d'in?? "
Inna ta nufota da wuk'ar saitin wuyanta Dije ta zaro Ido tare da fasa k'ara tace
"Wayyo Inna ki yi hak'uri wajen Dan birni naje na yi masa
turaren hayakin toshhi da kuka"
INNA ta dafe kirji tace
"La'ilaha illallahu Muhammadur'rasulullahi Dije kashemu zaki sa ayi a garin nan ne?me yayi maki kuma ya zu da zaki yi masa turaren mayu?"
Dije ta Sha jinin jikinta tana ajiyar zuciyar kuka tace,. "To Inna ba shi bane ya dakeni ranar"
Inna cikin fushi ta kai mata wani mangari tare da wata muguwar faka a baya tana fad'in,. "Ba sai da nace ki kyaleshi kar ki yi masa komi ba? Ashe duk nasihar da nayi maki ta bayan kunnuwanki ta bi ta wuce?, To ai kin kyauta kije ki yi abunda duk kika ga yafi maki tunda Ni kin maida maganata ba komi"
Tana k'are maganar ta fice ranta a matuk'ar bace tana fyace majinar kukan da ya zo mata ba shiri, Dije ta dunkule itama sai kukan take yi saboda har ga ALLAH taji tsoron halin da taga Safwan a ciki.
Ko da Baffah da Usman suka dawo Inna bata yi k'asa a gwiwa ba wajen zayyane masu komi, hankalin Baffah a tashe ya garzaya gidan Maigarin, in da ya taradda k'ofar gidan dank'am! Ana ta bi da zancen abunda ya faru, sai dai duk kashe kunnuwan da yayi bai ji ance Dije ce silar abun ba, hakan yasa shi sakin jiki ya baje anata cecekuce akan binciko wanene mai hannu akan faruwar lamarin, don har kwanon da Dije ta debo garwashin da shi sai da ya gani anata tuhumar inda kwanon ya fito, tare da zayyana irin abunda aka yi masa kwana biyu da suka wuce da Beraye, Wanda a iya bincike duk an bincika an tabbatar d'akin babu wani bera ko d'aya kafin faruwar hakan, ALLAH ya taimaka Safwan da Lawi basu fad'i cewa Dije ce ta aikata ba, to sai gashi yanzu ma ta sake kwatawa don kawai k'ok'arinta na rama abunda aka yi mata, don bata yafiya kuma bata manta ranar d'aukar fansa.
Baffah dai haka ya baje k'ofar Gidan Maigarin har wad'anda suka je kai Safwan Asibiti suka dawo, jin ba'asin samun nasara akan matsalar yasa ya yi sallama da su ya mamayi idanuwan Mutane ya dauke kwanon ya nufo gida da shi , Ko da ya shigo ranshi a b'ace ya wurgar da kwanon ya kalli Inna da ke cika tulunta da ruwan da Usman ya debo mata, yayi kwafa sannan yace
"Ki gaggauta jefa kwanon cen masai tun kafin bincike ya sa a gano Dije ce ta aikata wannan bak'in halin, don WALLAHI wannan karon kam ta jangwalo muna k'aton jidali, saboda yanzu haka fa yaron yana Asibiti sai da naji yanayin jikin nashi sannan na baro wajen"
Inna ta daina zuba ruwan ta yi tagumi tace,. "Ni WALLAHI na fara tunanin ko dai ayi wa Dije aure ne a huta?"
Baffah ya maka mata wata harara yace,
"WALLAHI ba wani aure da zan yi wa Dije yanzu tana yar shekara sha Uku, addu'ar nan dai da muke yi mata kullum to ita za mu ci gaba da yi ko yanzu, ina da tabbacin komi yayi tsanani to maganinshi ALLAH sarki, don haka yanzu ki yi gaggawar jefa kwanon cen a Masai mu huta da fad'uwar gaba"
Har ya fara tafiya ya waigo ya kalli Inna da tayi tagumi ta yi shiru tana nazarin mafita, cikin damuwa yace
"Ina ita Dijen?"
Inna ta yi masa nuni da hannunta akan cewa tana d'aki, Baffah ya nufi d'akin, Inna ta ja kafafuwanta ta d'auki kwanon ta nufi bayi ta jefashi sannan ta dawo cikin sanyin jiki ta k'arasa zuba ruwan ta nufo d'akinta, in da ta taradda Baffah ya ke ta balbale Dijen da ruwan fad'a kamar ya daketa, Dije kam sai kukanta take ta sharba tana ajiyar zuciya wata bayan wata.
Ranar dai haka mutanen gidan suka kwana kowane da abunda yake damunshi, Inna kam kwana ta yi tana rokarwa Dije shiriya tare da rokon ALLAH akan ya bata Miji nagari.
***
Malam Safwan kam sai da ya kwashi awanni sannan ya dawo cikin hankalinshi, in da ya kurawa Abokinshi Lawi idanuwa yana son ya gano tantagaryar abunda ya faru dashi, aiko sai gashi take yanke ya dinga kallon abun a cikin idanuwanshi in da Kai tsaye bayan k'are tunanin nashi zuciyarshi ta tabbatar masa da cewa Dije ce ta yi masa wanna aikin, cikin k'unar zuciya ya gyara kwanciyarshi ya kalli Lawi yace
"Yarinyar nan ko kad'an bata da imani kasheni take so ta yi abokina"
Lawi ya gyara zamanshi yace,. "Me yasa kake son d'orawa yarinyar nan laifin da ba ita ce ta aikata ba?"
Safwan ya k'ara b'ata fuskarshi yace,. "Yarinyar nan ko da ace kanwarka ce iya abunda zaka yi akanta kenan, ban san me yasa kake son kare yarinyar cen ba wai ko dai sonta kake yi ne Abokina?"
Lawi ya yi saurin girgiza kai yace,. "Ko d'aya Ni dai bana son ka dinga zarginta akan abunda ba ita ce ta yi ba, don takamar kaji cewa ta saka maka Beraye to ai wannan baka ji ta fad'a a bakin kowa ba, don haka ka daina zarginta kuma ka ajiye zaton cewa ita ce ka bi a hankali in har ita d'in ce zaka gano ai idan mun koma"
Safwan ya zaro Ido waje yace,. "Mu koma ina? Ai ni kam daga nan sai Gida don kam bazan koma bak'in kauyen nan ba, don na tsani ganin fuskar bak'ar shegiyar yarinyar nan, na tsaneta na tsaneta WALLAHI muddin ina ganinta to ko nine Nan zan yi ajalinta"
Lawi ya zaro ida cikin tsoron lafazin Safwan d'in, sannan ya kyalkyale da wata arniyar dariya yace
"Lalle ashe ko gaba da gabanta waton dai da gaske tsoronta kake ji Abokina, tunda har akanta zaka ajiye aikinka mai Muhimmanci"