Sashe 51
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin ikon Allah Asubar farin suna isa Kano, bayan an saukesu mutane da yawa suka fara arwallah domin su yi SALLAH, itama ta bi sahun mutanen ta siyi ruwan ta yi arwallah ta yi SALLAH duk da masifar ciyon da kanta take ji, sannan ta tambayi wani ina ake shiga motar Katsina, ya yi mata jagora har zuwa inda motocin suke ta ƙara ce da shi "don ALLAH Malam ina zan samu abinci inci WALLAHi yunwa nike ji sosai" ya ce ta zo su je ya nuna mata wani shagon sayar da abinci, aiko ta bishi har zuwa wani ƙaramin shagon, yace da ita ta shiga ta zauna ta jirashi ya kawo mata abincin, ba wani tunani ta shige shagon ta zauna tana kallon mutanen da ke wulgawa ta Kofar shagon, ƴan mintuna a sai gashi ya dawo yana wata dariyar rashin gaskiya, yana zuwa ba wani jinkiri ya rufe shagon, cikin tsoro Dije ta ce
"Ina abincin ?"
Ya sosa kanshi yace
"Ki fara bani naki abincin sannan sai in je in kawo maki nawa kafin lokacin ma mai abincin ta kammala"
Dije cikin mamaki tace
"Ni ina naga abincin da zan baka?da ina da shi ai bazan tambayeka ba"
Ya yi sake yin wata dariyar shakiyanci yace
"Ke ko kike da abincin ci ki natsu kawai mu gama komi cikin lokaci kafin mutane su fara cika tashar"
Dije ta zaro ido cikin tsoro tace, "WALLAHi ko ka bani hanya in fita ko yanzun nan in yi maka sanadin barin duniya"
Cikin dariya ya nufota zai cafkota ta zille ya sake yunkurin kamota ta ɗaga jakarta ta buga masa ita iya ƙarfinta, aiko cike da jin haushi ya damƙota ta fasa wata uwar ƙara, shi ko ba kunya sai ƙoƙarin mannata da jikinshi yake yi, ganin da gaske keta mata haddi yake so ya yi ta fasa wata uwar kuwwa bakinta a sake sai ihu take yi, suna cikin kokawar ne aka banko Ƙofar shagon da ƙarfi ta buɗe ya yi saurin kallon ƙofar yana muzurai, Dije ta yi waje da gudu a firgice ko ɗankwali babu bale takalmi, jikinta sai rawa yake yi tana faɗin
"WALLAHi sai na kasheka azzalumi shegen banza ɗan'iska"
Mutane suka taru a kanta saboda ganin yanda take ta kuka tana tsine masa, sai tambayarta ake ba ɓata lokaci ta yi bayanin duk abunda ya haɗa su, aiko nan take mutane suka yi ta tsine masa suna aibatashi, wani ya shiga ya ɗauko mata jakarta da talkami da ɗankwalinta ya bata ta saka, sannan wasu matasa suka rufeshi da duka, cikin tausayinta wani bawan ALLAH ya je ya siyo mata tea da biredi ya kaita wani waje ta raɓa ta sha, sai dai tana gama sha amai ya biyo baya ba shiri ta fara rawar sanyi, mutumin ya siyo mata magani ta sha sannan ya sakata motar katsina sai da motar ta tashi sannan ya tafi yana jinjina halin wasu iyaye masu yiwa ƴaƴa riƙon sakainar kashi, su yi ta sakin ƴaƴansu duk inda suka ga dama.
A galabaice Dije ta isa babban birnin garinsu ta shiga motar da zata kaita ƙauyensu, har ƙofar gida Direban ya kaita saboda babu ko sisi a hannunta duk mota ta cenye kuɗin, asalima ko kuɗin zuwa katsinar ma sai da wata mata ta cika mata da nata basu kai ba, cikin tsananin galabaita ta faɗa gidansu yaran da suka biyo motar suka bita suna ihun ga Dije ga Dije amman ko ta kansu bata bi ba.
Tana shiga kai tsaye ɗakin Inna ta faɗa ta haye gado ta dunƙule cikin zane tana rawar sanyi, Inna daga bayi ta jiyo muryar yara suna ta kuwwar zuwan Dijen, jikinta yana rawa ta nufi ƙofar gidan inda suka ci karo da Hansai da itama ta fito daga sashenta aguje cikin murna da ɗokin ganin Dijen.
Amman basu ganta ba sai Direban da ya kawota kawai da ke ƙofar gidan yana bada saƙon a karɓo masa kuɗinshi tafiya zai yi, Inna ta tambayi yaran ina Dijen suka ce tana cikin gidan ta shige ɗaki, gaban Inna ya ƙire ya faɗi saboda jikinta ya bata cewa ba zuwan lafiya ne Dijen ta yo ba, cikin sauri ta kwance ƙullin da ke haɓar zanenta ta re da tambayar nawa ne kuɗin?
Direban ya faɗa ta bashi ta yi masa godiya cike da rawar jiki ta koma cikin gidan gabanta sai faɗuwa yake yi, sai dai tun kafin ta isa gadon ta jiyo sautin nishin Dijen, da ke ta rawar sanyi haƙoranta suna haɗuwa suna karkarwa, cikin sauri Inna ta zauna ta re da yaye rufar da ta yi ta taɓa wuyanta ta ji zafi zau!, Cikin faɗuwar gaba tace
"Dije lafiyarki ku wa?ina Hajiyar? Ya aka yi kika zo ke kaɗai bayan kuma nasan buki kuke yi?"
Dije cikin rawar baki hawaye suna zuba gefen idonta tace,. "Ni kaɗai nake ai"
Hansai ta shigo jiki a sanyaye ta zauna gefen Dijen tace, "Sannu Dije baki da lafiya ne?"
Dije ta ɗaya Kai Inna ta miƙe ta je ta ɗauko mata magunguna ta matsa mata sai da ta sha sannan ta koma ta dunƙule, Inna ta kalli Hansai tace
"A sami yaro a aikashi gidan Maigari ki ce ya zo gida ana nemanshi"
Hansai ta fita Inna ta dawo ta sassafta murya tace, "Dije faɗa man gaskiya kafin malam ya zo shin Mijinki rabuwa ya yi dake ne ko yaya?"
Dije ta yi saurin girgiza kai tace,
"A'ah Inna ba ma wanda yasan na tafo"
Inna ta sake jin wani sabon fargaba, ta tada ita zaune tace "Kallanni da kyau Dije bana son Baffahnki ya shigo baki sanar da Ni gaskiyar abunda yake faruwa ba"
Dije ta ja jikinta ta jingina da bango tace,
"Ba rabuwa ya yi dani ba Inna amman WALLAHi ni na gaji da aurenshi tunda yake son ya lalace mani rayuwa"
Inna ta zaro ido waje tace "bangane ya lalace maki rayuwa ba? ki yi man bayani dalla dalla yanda zan gane"
Dije ta share hawayenta tace
"Inna jikina yake taɓawa WALLAHi har kayana ya tuɓe yanata yi man wani iskanci a jiki........"
Ba shiri Inna ta kai mata wani bahagon mari a baki cikin fushi ta nunata da hannu tace, "au Wai daman akan wannan dalilin ne kika gudo tun daga Yola har zuwa garin nan? To buɗe kunnuwanki da kyau kiji WALLAHI matuƙar kika ce bazaki iya yiwa Mijinki biyayya akan duk abunda ya zo maki da shi ba, to Ni Ko ko kaɗan ba zamu shirya da ke ba"
Dije dafe da gefen da ta sha marin cike da mamaki tace, "Inna WALLAHi har ƙirjina yake taɓawa yana ƙoƙarin cire mani ɗan kamfai, kuma ma har dukana yake yi fa"
Inna ta wurga mata wata ƙatuwar harara tace, "abunda ya fi duka ma idan ya yi maki kin cancanta ai, to bari kiji duk abunda kika ga ya yi maki ko yana ƙoƙarin yi dake to tuni Baffahnki yayi hakan dani, kuma gani daram har yanzu kin ganni ba abunda ya sameni, don haka tun wuri WALLAHi ki shiga taitayinki miye amfanin karatun da kike yi?, Saboda haka tun kafin ki janyo wa kanki abun gori cikin mutane, sannan ki tsallake Hajiya ki nufo gidan nan ke kaɗai ko tsoron abunda zai sameki a hanyar baki ji ba, yanzu da wane ido kike so mu kalleta ace kin tsallaketa akan wannan guntuwar matsala kin nufo gida?. "
Dije ta zumɓuro Baki tace, "kedai Inna don baki san me yake yi mani bane shiyasa"
Inna ta buge mata baki tace "ina ko zan sani tunda ban taɓa yin auren ba, to bari kiji in baki sani ba ki sani shekarun baya akan wannan dalilin ne aka ɗaure Jummala, ke ma idan kina son ayi maki haka to WALLAHi ko a cikin ɗakin nan zamu iya ɗaure masa ke, ya yi duk abunda yake so da ke tunda ba zunubi ne zai aikata ba"
Dije ta zaro ido tace
"Inna yanzu daman akan haka ne aka ɗaure Jummalar? Cabɗi to WALLAHi gaskiya kam ba'a kyautawa rayuwarta ba, to ni dai WALLAHI bazan taɓa bari wani ƙaton banza ya yi iskanci da Ni ba ina kallo in ƙyaleshi ba"
Inna ta sake Kai mata wani marin wanda ya yi dai dai da shigowar Baffah tana faɗin
"Mu zaki tonawa asiri Dije?"
"Wane asiri zata tona bayan yanzun nan muka gama waya da Uwar mijinta an sanar da ita Dijen tana nan saboda ta ɗaga hankalinta sosai akan rashin ganinta, don haka ki bar yarinya ta huta da wahalar motar da ta kwaso sannan ki fara dukan nata tunda ke hannunki bai girma da bugunta"
Ya ƙaraso wajen Dijen ya shafo kanta yace, "Dijengalata me yasa kika baro cen ba tare da sanin Mijinki ba"
Dije ta fashe da wani sabon kuka, Inna ta ce da Baffahn ya zo ya ji suka fita tare har zuwa ɗakinshi, cikin ɓacin rai ta sanar da shi dalilin da ya dawo da Dijen, Baffah ya yi shiru yana nazari saboda shi tsammaninshi ma tuni an wuce wannan babin, ashe yanzu ake matsalar ya sauke ƙatuwar ajiyar zuciya yace
"A gaskiya yaron nan ya yi haƙuri da yawa WALLAHi, amman ita kuma a hankali zaki fahimtar da ita ba da duka ko faɗa ba, saboda yanzu haka mijinta yana kan hanyar zuwa garin nan, kuma da ya zo nike son ta bishi su koma don banga amfanin zaman da zata yi muna anan ba"
Inna ta sauke ajiyar zuciya tace, "ALLAH ya kawoshi lafiya amman kasan dai ko kaɗan bata kyautawa Hajiya ba ko?, Ace duk dawainiyar da take yi da ita amman ta tsallaketa ta zo wurinmu akan wannan guntuwar matsala"
Baffah yace
"Haƙuri za'a yi kuma yanzu tunda dai mai afkuwa ta riga da ta afku, sai a kira ita Hajiyar a bata haƙuri shi kuma idan yazo mu bashi haƙuri ya tafi da matarshi"
Inna sauke wata ajiyar zuciya tace "ALLAH ya kawoshi lafiya sai dai ni naso ace a barta ta yi kwana biyu anan, saboda in fahimtar da ita abubuwan da suka shige mata duhu"
Baffah ya ce "aganinki ba za'a ga munyi ƙaranta ba?"
"Ina abincin ?"
Ya sosa kanshi yace
"Ki fara bani naki abincin sannan sai in je in kawo maki nawa kafin lokacin ma mai abincin ta kammala"
Dije cikin mamaki tace
"Ni ina naga abincin da zan baka?da ina da shi ai bazan tambayeka ba"
Ya yi sake yin wata dariyar shakiyanci yace
"Ke ko kike da abincin ci ki natsu kawai mu gama komi cikin lokaci kafin mutane su fara cika tashar"
Dije ta zaro ido cikin tsoro tace, "WALLAHi ko ka bani hanya in fita ko yanzun nan in yi maka sanadin barin duniya"
Cikin dariya ya nufota zai cafkota ta zille ya sake yunkurin kamota ta ɗaga jakarta ta buga masa ita iya ƙarfinta, aiko cike da jin haushi ya damƙota ta fasa wata uwar ƙara, shi ko ba kunya sai ƙoƙarin mannata da jikinshi yake yi, ganin da gaske keta mata haddi yake so ya yi ta fasa wata uwar kuwwa bakinta a sake sai ihu take yi, suna cikin kokawar ne aka banko Ƙofar shagon da ƙarfi ta buɗe ya yi saurin kallon ƙofar yana muzurai, Dije ta yi waje da gudu a firgice ko ɗankwali babu bale takalmi, jikinta sai rawa yake yi tana faɗin
"WALLAHi sai na kasheka azzalumi shegen banza ɗan'iska"
Mutane suka taru a kanta saboda ganin yanda take ta kuka tana tsine masa, sai tambayarta ake ba ɓata lokaci ta yi bayanin duk abunda ya haɗa su, aiko nan take mutane suka yi ta tsine masa suna aibatashi, wani ya shiga ya ɗauko mata jakarta da talkami da ɗankwalinta ya bata ta saka, sannan wasu matasa suka rufeshi da duka, cikin tausayinta wani bawan ALLAH ya je ya siyo mata tea da biredi ya kaita wani waje ta raɓa ta sha, sai dai tana gama sha amai ya biyo baya ba shiri ta fara rawar sanyi, mutumin ya siyo mata magani ta sha sannan ya sakata motar katsina sai da motar ta tashi sannan ya tafi yana jinjina halin wasu iyaye masu yiwa ƴaƴa riƙon sakainar kashi, su yi ta sakin ƴaƴansu duk inda suka ga dama.
A galabaice Dije ta isa babban birnin garinsu ta shiga motar da zata kaita ƙauyensu, har ƙofar gida Direban ya kaita saboda babu ko sisi a hannunta duk mota ta cenye kuɗin, asalima ko kuɗin zuwa katsinar ma sai da wata mata ta cika mata da nata basu kai ba, cikin tsananin galabaita ta faɗa gidansu yaran da suka biyo motar suka bita suna ihun ga Dije ga Dije amman ko ta kansu bata bi ba.
Tana shiga kai tsaye ɗakin Inna ta faɗa ta haye gado ta dunƙule cikin zane tana rawar sanyi, Inna daga bayi ta jiyo muryar yara suna ta kuwwar zuwan Dijen, jikinta yana rawa ta nufi ƙofar gidan inda suka ci karo da Hansai da itama ta fito daga sashenta aguje cikin murna da ɗokin ganin Dijen.
Amman basu ganta ba sai Direban da ya kawota kawai da ke ƙofar gidan yana bada saƙon a karɓo masa kuɗinshi tafiya zai yi, Inna ta tambayi yaran ina Dijen suka ce tana cikin gidan ta shige ɗaki, gaban Inna ya ƙire ya faɗi saboda jikinta ya bata cewa ba zuwan lafiya ne Dijen ta yo ba, cikin sauri ta kwance ƙullin da ke haɓar zanenta ta re da tambayar nawa ne kuɗin?
Direban ya faɗa ta bashi ta yi masa godiya cike da rawar jiki ta koma cikin gidan gabanta sai faɗuwa yake yi, sai dai tun kafin ta isa gadon ta jiyo sautin nishin Dijen, da ke ta rawar sanyi haƙoranta suna haɗuwa suna karkarwa, cikin sauri Inna ta zauna ta re da yaye rufar da ta yi ta taɓa wuyanta ta ji zafi zau!, Cikin faɗuwar gaba tace
"Dije lafiyarki ku wa?ina Hajiyar? Ya aka yi kika zo ke kaɗai bayan kuma nasan buki kuke yi?"
Dije cikin rawar baki hawaye suna zuba gefen idonta tace,. "Ni kaɗai nake ai"
Hansai ta shigo jiki a sanyaye ta zauna gefen Dijen tace, "Sannu Dije baki da lafiya ne?"
Dije ta ɗaya Kai Inna ta miƙe ta je ta ɗauko mata magunguna ta matsa mata sai da ta sha sannan ta koma ta dunƙule, Inna ta kalli Hansai tace
"A sami yaro a aikashi gidan Maigari ki ce ya zo gida ana nemanshi"
Hansai ta fita Inna ta dawo ta sassafta murya tace, "Dije faɗa man gaskiya kafin malam ya zo shin Mijinki rabuwa ya yi dake ne ko yaya?"
Dije ta yi saurin girgiza kai tace,
"A'ah Inna ba ma wanda yasan na tafo"
Inna ta sake jin wani sabon fargaba, ta tada ita zaune tace "Kallanni da kyau Dije bana son Baffahnki ya shigo baki sanar da Ni gaskiyar abunda yake faruwa ba"
Dije ta ja jikinta ta jingina da bango tace,
"Ba rabuwa ya yi dani ba Inna amman WALLAHi ni na gaji da aurenshi tunda yake son ya lalace mani rayuwa"
Inna ta zaro ido waje tace "bangane ya lalace maki rayuwa ba? ki yi man bayani dalla dalla yanda zan gane"
Dije ta share hawayenta tace
"Inna jikina yake taɓawa WALLAHi har kayana ya tuɓe yanata yi man wani iskanci a jiki........"
Ba shiri Inna ta kai mata wani bahagon mari a baki cikin fushi ta nunata da hannu tace, "au Wai daman akan wannan dalilin ne kika gudo tun daga Yola har zuwa garin nan? To buɗe kunnuwanki da kyau kiji WALLAHI matuƙar kika ce bazaki iya yiwa Mijinki biyayya akan duk abunda ya zo maki da shi ba, to Ni Ko ko kaɗan ba zamu shirya da ke ba"
Dije dafe da gefen da ta sha marin cike da mamaki tace, "Inna WALLAHi har ƙirjina yake taɓawa yana ƙoƙarin cire mani ɗan kamfai, kuma ma har dukana yake yi fa"
Inna ta wurga mata wata ƙatuwar harara tace, "abunda ya fi duka ma idan ya yi maki kin cancanta ai, to bari kiji duk abunda kika ga ya yi maki ko yana ƙoƙarin yi dake to tuni Baffahnki yayi hakan dani, kuma gani daram har yanzu kin ganni ba abunda ya sameni, don haka tun wuri WALLAHi ki shiga taitayinki miye amfanin karatun da kike yi?, Saboda haka tun kafin ki janyo wa kanki abun gori cikin mutane, sannan ki tsallake Hajiya ki nufo gidan nan ke kaɗai ko tsoron abunda zai sameki a hanyar baki ji ba, yanzu da wane ido kike so mu kalleta ace kin tsallaketa akan wannan guntuwar matsala kin nufo gida?. "
Dije ta zumɓuro Baki tace, "kedai Inna don baki san me yake yi mani bane shiyasa"
Inna ta buge mata baki tace "ina ko zan sani tunda ban taɓa yin auren ba, to bari kiji in baki sani ba ki sani shekarun baya akan wannan dalilin ne aka ɗaure Jummala, ke ma idan kina son ayi maki haka to WALLAHi ko a cikin ɗakin nan zamu iya ɗaure masa ke, ya yi duk abunda yake so da ke tunda ba zunubi ne zai aikata ba"
Dije ta zaro ido tace
"Inna yanzu daman akan haka ne aka ɗaure Jummalar? Cabɗi to WALLAHi gaskiya kam ba'a kyautawa rayuwarta ba, to ni dai WALLAHI bazan taɓa bari wani ƙaton banza ya yi iskanci da Ni ba ina kallo in ƙyaleshi ba"
Inna ta sake Kai mata wani marin wanda ya yi dai dai da shigowar Baffah tana faɗin
"Mu zaki tonawa asiri Dije?"
"Wane asiri zata tona bayan yanzun nan muka gama waya da Uwar mijinta an sanar da ita Dijen tana nan saboda ta ɗaga hankalinta sosai akan rashin ganinta, don haka ki bar yarinya ta huta da wahalar motar da ta kwaso sannan ki fara dukan nata tunda ke hannunki bai girma da bugunta"
Ya ƙaraso wajen Dijen ya shafo kanta yace, "Dijengalata me yasa kika baro cen ba tare da sanin Mijinki ba"
Dije ta fashe da wani sabon kuka, Inna ta ce da Baffahn ya zo ya ji suka fita tare har zuwa ɗakinshi, cikin ɓacin rai ta sanar da shi dalilin da ya dawo da Dijen, Baffah ya yi shiru yana nazari saboda shi tsammaninshi ma tuni an wuce wannan babin, ashe yanzu ake matsalar ya sauke ƙatuwar ajiyar zuciya yace
"A gaskiya yaron nan ya yi haƙuri da yawa WALLAHi, amman ita kuma a hankali zaki fahimtar da ita ba da duka ko faɗa ba, saboda yanzu haka mijinta yana kan hanyar zuwa garin nan, kuma da ya zo nike son ta bishi su koma don banga amfanin zaman da zata yi muna anan ba"
Inna ta sauke ajiyar zuciya tace, "ALLAH ya kawoshi lafiya amman kasan dai ko kaɗan bata kyautawa Hajiya ba ko?, Ace duk dawainiyar da take yi da ita amman ta tsallaketa ta zo wurinmu akan wannan guntuwar matsala"
Baffah yace
"Haƙuri za'a yi kuma yanzu tunda dai mai afkuwa ta riga da ta afku, sai a kira ita Hajiyar a bata haƙuri shi kuma idan yazo mu bashi haƙuri ya tafi da matarshi"
Inna sauke wata ajiyar zuciya tace "ALLAH ya kawoshi lafiya sai dai ni naso ace a barta ta yi kwana biyu anan, saboda in fahimtar da ita abubuwan da suka shige mata duhu"
Baffah ya ce "aganinki ba za'a ga munyi ƙaranta ba?"