Sashe 15
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Safwan yayi masa wani kallo yace,. "Tsoro??? Duk in rasa wa zan yi tsoro sai wannan bak'ar magen? Cabd'i aiko kayi kuskure Abokina amman tunda har kace haka Zan koma Makarantar inci gaba da karantarwar amman anan garin zan sami wurin zama sai in dinga zuwa ina dawowa"
Lawi ya k'umshe dariyarshi yace,. ,"Har yanzu da tsoron dai to ALLAh yasa hakan shine alkhairi amman Ni kam ina cen kauyen don a gaskiya naji dad'inshi"
Safwan ya yi masa wani mere yace,. "Kaji da rashin hankalinka amman Ni kam na k'are kwana garin daga yau"
🤣🤣🤣🤣🤣
Akafta😹
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*BAK'ON YANAYI LITTAFI NE MAI ZAFI 300 KACAL ZA TA MALLAKA MAKI SHI MAI BUKATA TA TUNTUB'E NI TA WANNAN NUMBER 09032685442*
*Lamba ta 15*
Tun daga Ranar Dije ta yi sukuku da ita don daga Baffah har Inna sun daina sakewa da ita, daman cen shi Usman ba wani shiri suke yi da ita Sosai ba, Dije cikin dabara ta dinga makalewa gidan Inna Gambo, don wani zubin ma dawowarta Makarantar bokon ke da wuya take tafiyarta gidanta ko Makarantar allonsu daga cen ta ke zuwa, INNA kanta ta fi sha'awar zuwanta Gidan da dai ace taje ta yi ta janyo masu abun magana, duk da ko ita Inna Gambon ana nuna mata halin watarana, saboda muddin ta kawo mata Abinci bata bata nera biyar d'in da take bata kullum ta kawo mata tuwon ba, to ko ko da ta ajiye tuwon sai ta dawo tace
"Inna Gambo kinji Innata tace in babu biyar d'in to a bada tuwon"
Wani zubin ta hanata d'aukar tuwon watarana kuma tace da ita,. "D'auki tuwonku ki kaiwa duk wanda kike so tunda daman cen ba don ALLAH kike kawo man ba"
Watarana kuma ta jefa mata nera biyar d'in tace,. " D'auki gata nan amman ki sani gobe kar ma ki kawo man tuwon don bana so "
Dije sai ta d'auke biyar d'in sannan ta dawo tana kalailameta da dad'in baki, Sabida gyaran hanya har shara da wanke wanke sai ta yi mata, sannan ta dinga debo mata ruwa tana cika mata tukanenta da tulunanta na ruwa.
Inna Gambo da Dije in sun had'u wajibi ne ma sai ka yi dariya saboda yanda suke tsarguwar junansu, musamman dai ita Gambo da kullum ta ke yiwa Dije kirari da cewa
"Alhudahuda Sarkin karatu sillen kara ta Ummaru Sanda, sarka mai rikicin gan gan, in kin so ayi ta morarki in kuma kin k'i ki fad'i ki rikice a rasa gano kanki, Dijengala ta megari Dije ba auren talaka ba talaka noma da sassabe, ALLAH ya kai mu inga aurenki ko don in baiwa Mijinki gudunmuwar bulala"
Dije kam in Gambo tana yi mata kirarin har wani tsallen jin dad'i take yi tana rufe ido wai ita kunya, to dai kam wannan karon ko ita Gambon ta gano damuwar da Dijen take ciki, saboda zaunenta ta ke yi ta yi ta karatunta duk wata kiriniya ajiyeta ta yi ta koma sukuku da ita.
Hankalinta bai kwanta ba sai ranar da ta je Makarantar ta hango Malam Safwan, cikin sanyin jiki ta isa wurinshi ta gayar da shi ta wuce ajinsu, duk da bai amsa ba amman ta ji dad'in ganin ya mirmije daga ciyon dolen da ta sakashi.
SAFWAN kam binta yayi da kallon tsana tamkar ya janyota yayi ta jibga yake ji, amman tsoron sharrin da zata sake kulla masa yasashi yin alk'awalin ba zai sake biyeta ba, ballantana har watarana ta janyo masa bala'in da bai san ta inda zai taroshi ba, karatu dai ne ya zama dole to zai yi masu amman kam yasa a ranshi ba zai sake shiga shirginta ba.
Ta bangarenta ne da kawayenta suka yanke shawarar kai kararshi wajen shugaban Makarantar, saboda basu fahimtar karatunshi sabida tsagwaron turancin da yake ta zuba masu, har za su fita Dije wani tunani ya zo mata a rai tace da su
"Ku tsaya kuji wata shawara in kun amince mu ma mu dinga buga masa turancinmu na hauka ko da ba dai dai muka yi ba, ya fi dai da ace mu kai kararshi ya zo ya kara renamu"
Ladiyo ta rik'e hab'a tace,. "Ke Dije to in ke kin iya turancin mu ai bamu iya komi ba"
Dijen ta kyalkyale da wata dariya sannan tace,. "In kun amince Littafin da nake dubawa ina hardace sunayen abubuwa zan fara koya maku shi ku ma, ko don mu dinga haukatashi da turancinmu saboda if you had'a turanci da Hausa to no body kan k'ureka da shi"
Mune da ke cen rakub'e tana kallonsu ta yi wani tsalle tace,. "Yee! Su Dije anji dad'i an kware da turanci"
Dije ta galla mata harara tace,. "Ba nace kar ki sake shiga shirgina ba?? Ai Ni WALLAHI tun da kike da baki irin na aku kuturu bazan sake huldata da ke ba, ke kenan yawon gulma da tsegumi ko kin d'auka bansan kece kika fad'awa Malam nice na saka masa Beraye ba?, To bari kiji ko kusa dani na sake ganinki sai na shikka maki rashin mutunci mai matsayin monita a Makarantar nan"
Mune ta yi rau rau da Ido ta dunkule tana kuka, Dije ta ja su Ladiyo suka fita sunata shawarwarinsu akan baturen Malamin nasu.
Ai kuwa sai gashi cikin kwana biyu Dije ta fara koyawa su Ladiyo Littafin, cikin ikon ALLAH har sun fara ganewa suka watsar da karatun don daman cen ba wani son bokon suke yi ba, Dije Kam ta fita iskansu tana ta ci gaba da nacin bin kalmomin tana tantance su, don shi kanshi ganin ta fara catching d'in abubuwa ya fara rage nauyin tsanar da yake yi mata, wasa wasa sai gashi har lesson yake yi mata na daban ita kad'ai duk da a cikin class yake yi gaban sauran Yan ajin, amma kamar ita kadaice yake yiwa karatun, Sabida su iya kacinsu ido don basu fahimtar komi a darasin nashi.
Cikin ikon ALLAH sai ga Safwan da sakarwa Dije fuska wani zubin ma har da su murmushi idan ta buga masa wani kalar turancinta mai had'e da Hausa.
Lawi kam ganin yanda suke d'asawa ya fara jinshi yana kishin hakan, duk da dai bai tab'a nuna wani Abu da zai nuna matsayin da ya dauki Dijen ba, amman a zahirin gaskiya ba k'aramin so yake yiwa Dijen ba, yak'i furtawa ne don ya fahimci ita ba wannan ne a gabanta ba, don sai da ya bincika sosai ya tabbatar da Dije bata kula kowa sannan hankalinshi ya kwanta, to amman sai ga shi ya fara ganin canji a wurin Abokin nashi dangane da ita Dijen, cikin dabara ya shirya bugun cikinshi domin yaji gaskiyar lamarin.
Aiko ranar suna d'akinsu na gidan Maigarin don tuni Safwan d'in ya baro cen garin ya dawo nan d'in saboda wahalar go and come d'in da yake yi kullum tsakanin garin da kauyensu Dijen.
Lawi ya kalleshi yaga yanda yake ta marking d'in papers d'in Test d'in da yayiwa yaran Makarantar, ya yi gyaran murya yace
"Abokina wai fa kwanan nan naga sai wani kawance kuke yi da mutuniyar taka, ko dai ka rufta ne kai ma kamar Ni?"
Safwan bai daina marking papers d'in ba yace,. "Wace mutunniyar?"
Lawi ya yi masa hararar gefe yace,. "Wace fa bayan Dije abokiyar rigimarka"
Safwan ya d'aga kafada yace,. "No ba wani abun kawai dai don naga tana da jajircewa akan karatun ne shiyasa"
Lawi ya k'ura masa Ido saboda son tabbatar da gaskiyar zancen, sannan ya sauke ajiyar zuciya yace,
"Da dai ka sanar dani gaskiya Abokina don bana son mu zo mu mato a soyayyarta daga Ni har kai"
Ba shiri Safwan ya d'ago kanshi ya kai kallonshi ga Lawin baki a bud'e zuciyarshi sai bugawa take yi da sauri da sauri, cikin b'acin Rai yace
"Kai ko ance maka zan so black cat zaka amince? Me Zan yi da karamar Yarinya irinta kuma don rashin mafadi Yar k'auye"
Lawi ya yi saurin fad'in
"Me zai hana ita din ba mace bace halan?"
Safwan cikin zafin Rai ya ajiye takardun ya mike ranshi a b'ace yace,. "Kai dai da kaga zaka iya to ka je ka yi ta yi, amman Ni kam matsayina ya girmi in lalace Kan duk wata ''ya da ke Cikin kauyen nan, musamman dai ita d'in da baka banbance komi a fuskarta sai hak'oranta da kwayar idanuwanta saboda tsabar bak'in da take dashi, cab! ALLAH ya rabani WALLAHI ku je cen ku k'arata"
Cike da jin dad'i Lawi ya bi bayan abokin na shi da kallo har ya fice, sannan ya mike tsaye cikin wani tsantsar farin ciki yace
"Gareka Lawi lokaci yayi da zaka fara farauto soyayyarka"
Aiko a gurguje ya shirya ya nufi wurin Maigari bayan sun gaisa ne ya dan sosa kanshi yana so yayi magana yana tunanin ta ina ma zai fara?, Maigarin ya kalli yanda bakinshi yake rawa alamun akwai maganar da yake so su yi amman nauyi ya hanashi fad'a, shiyasa ya sallami sauran mutanen da ke wajen sannan ya kalli Lawi yana murmushi yace,
"Lafiya yarona na ganka haka? Ga dukkan alamu dai akwai zancen da ka zo man da shi, to kar ka ji komi nasha gaya maka ka d'auka tamkar cewa Ni din Mahaifinka ne, don haka kar ka ji shakkun tunkarata da kowace irin magana ce "
Lawi ya kara sunne kanshi yace,. "Wata yarinya ce na gani Ina so a garin nan, to shine nike jin tsoron bayyana kaina gareta gashi bansan al'adar garin ba"
Maigarin ya washe bakinshi yace
"A'ah to Masha ALLAHU ita ko wace mai sa'a ce wannan ???"
Lawi cikin zumudinshi yace,. "Wata yarinya ce naji ana kiranta Dije"
Ba Maigarin ba harta Liman da ke zaune da carbinshi yana ja sai da ya zaro Ido, cikin fargaba Maigarin yace
"Wace Dijen ba dai ta gidan Malam Sanda ba?"
Lawi cikin jin nauyi yace "Eh ita ranka ya dad'e"
Maigarin ya sauke ajiyar zuciya yace,. "To dai lamarin aure bincike ake so a fara yi kafin a tsunduma kan lamarin, yana da kyau ka fara binciken halinta kafin ka fito da bukatarka gareta"
Lawi ya k'umshe dariyarshi yace,. ,"Har yanzu da tsoron dai to ALLAh yasa hakan shine alkhairi amman Ni kam ina cen kauyen don a gaskiya naji dad'inshi"
Safwan ya yi masa wani mere yace,. "Kaji da rashin hankalinka amman Ni kam na k'are kwana garin daga yau"
🤣🤣🤣🤣🤣
Akafta😹
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*BAK'ON YANAYI LITTAFI NE MAI ZAFI 300 KACAL ZA TA MALLAKA MAKI SHI MAI BUKATA TA TUNTUB'E NI TA WANNAN NUMBER 09032685442*
*Lamba ta 15*
Tun daga Ranar Dije ta yi sukuku da ita don daga Baffah har Inna sun daina sakewa da ita, daman cen shi Usman ba wani shiri suke yi da ita Sosai ba, Dije cikin dabara ta dinga makalewa gidan Inna Gambo, don wani zubin ma dawowarta Makarantar bokon ke da wuya take tafiyarta gidanta ko Makarantar allonsu daga cen ta ke zuwa, INNA kanta ta fi sha'awar zuwanta Gidan da dai ace taje ta yi ta janyo masu abun magana, duk da ko ita Inna Gambon ana nuna mata halin watarana, saboda muddin ta kawo mata Abinci bata bata nera biyar d'in da take bata kullum ta kawo mata tuwon ba, to ko ko da ta ajiye tuwon sai ta dawo tace
"Inna Gambo kinji Innata tace in babu biyar d'in to a bada tuwon"
Wani zubin ta hanata d'aukar tuwon watarana kuma tace da ita,. "D'auki tuwonku ki kaiwa duk wanda kike so tunda daman cen ba don ALLAH kike kawo man ba"
Watarana kuma ta jefa mata nera biyar d'in tace,. " D'auki gata nan amman ki sani gobe kar ma ki kawo man tuwon don bana so "
Dije sai ta d'auke biyar d'in sannan ta dawo tana kalailameta da dad'in baki, Sabida gyaran hanya har shara da wanke wanke sai ta yi mata, sannan ta dinga debo mata ruwa tana cika mata tukanenta da tulunanta na ruwa.
Inna Gambo da Dije in sun had'u wajibi ne ma sai ka yi dariya saboda yanda suke tsarguwar junansu, musamman dai ita Gambo da kullum ta ke yiwa Dije kirari da cewa
"Alhudahuda Sarkin karatu sillen kara ta Ummaru Sanda, sarka mai rikicin gan gan, in kin so ayi ta morarki in kuma kin k'i ki fad'i ki rikice a rasa gano kanki, Dijengala ta megari Dije ba auren talaka ba talaka noma da sassabe, ALLAH ya kai mu inga aurenki ko don in baiwa Mijinki gudunmuwar bulala"
Dije kam in Gambo tana yi mata kirarin har wani tsallen jin dad'i take yi tana rufe ido wai ita kunya, to dai kam wannan karon ko ita Gambon ta gano damuwar da Dijen take ciki, saboda zaunenta ta ke yi ta yi ta karatunta duk wata kiriniya ajiyeta ta yi ta koma sukuku da ita.
Hankalinta bai kwanta ba sai ranar da ta je Makarantar ta hango Malam Safwan, cikin sanyin jiki ta isa wurinshi ta gayar da shi ta wuce ajinsu, duk da bai amsa ba amman ta ji dad'in ganin ya mirmije daga ciyon dolen da ta sakashi.
SAFWAN kam binta yayi da kallon tsana tamkar ya janyota yayi ta jibga yake ji, amman tsoron sharrin da zata sake kulla masa yasashi yin alk'awalin ba zai sake biyeta ba, ballantana har watarana ta janyo masa bala'in da bai san ta inda zai taroshi ba, karatu dai ne ya zama dole to zai yi masu amman kam yasa a ranshi ba zai sake shiga shirginta ba.
Ta bangarenta ne da kawayenta suka yanke shawarar kai kararshi wajen shugaban Makarantar, saboda basu fahimtar karatunshi sabida tsagwaron turancin da yake ta zuba masu, har za su fita Dije wani tunani ya zo mata a rai tace da su
"Ku tsaya kuji wata shawara in kun amince mu ma mu dinga buga masa turancinmu na hauka ko da ba dai dai muka yi ba, ya fi dai da ace mu kai kararshi ya zo ya kara renamu"
Ladiyo ta rik'e hab'a tace,. "Ke Dije to in ke kin iya turancin mu ai bamu iya komi ba"
Dijen ta kyalkyale da wata dariya sannan tace,. "In kun amince Littafin da nake dubawa ina hardace sunayen abubuwa zan fara koya maku shi ku ma, ko don mu dinga haukatashi da turancinmu saboda if you had'a turanci da Hausa to no body kan k'ureka da shi"
Mune da ke cen rakub'e tana kallonsu ta yi wani tsalle tace,. "Yee! Su Dije anji dad'i an kware da turanci"
Dije ta galla mata harara tace,. "Ba nace kar ki sake shiga shirgina ba?? Ai Ni WALLAHI tun da kike da baki irin na aku kuturu bazan sake huldata da ke ba, ke kenan yawon gulma da tsegumi ko kin d'auka bansan kece kika fad'awa Malam nice na saka masa Beraye ba?, To bari kiji ko kusa dani na sake ganinki sai na shikka maki rashin mutunci mai matsayin monita a Makarantar nan"
Mune ta yi rau rau da Ido ta dunkule tana kuka, Dije ta ja su Ladiyo suka fita sunata shawarwarinsu akan baturen Malamin nasu.
Ai kuwa sai gashi cikin kwana biyu Dije ta fara koyawa su Ladiyo Littafin, cikin ikon ALLAH har sun fara ganewa suka watsar da karatun don daman cen ba wani son bokon suke yi ba, Dije Kam ta fita iskansu tana ta ci gaba da nacin bin kalmomin tana tantance su, don shi kanshi ganin ta fara catching d'in abubuwa ya fara rage nauyin tsanar da yake yi mata, wasa wasa sai gashi har lesson yake yi mata na daban ita kad'ai duk da a cikin class yake yi gaban sauran Yan ajin, amma kamar ita kadaice yake yiwa karatun, Sabida su iya kacinsu ido don basu fahimtar komi a darasin nashi.
Cikin ikon ALLAH sai ga Safwan da sakarwa Dije fuska wani zubin ma har da su murmushi idan ta buga masa wani kalar turancinta mai had'e da Hausa.
Lawi kam ganin yanda suke d'asawa ya fara jinshi yana kishin hakan, duk da dai bai tab'a nuna wani Abu da zai nuna matsayin da ya dauki Dijen ba, amman a zahirin gaskiya ba k'aramin so yake yiwa Dijen ba, yak'i furtawa ne don ya fahimci ita ba wannan ne a gabanta ba, don sai da ya bincika sosai ya tabbatar da Dije bata kula kowa sannan hankalinshi ya kwanta, to amman sai ga shi ya fara ganin canji a wurin Abokin nashi dangane da ita Dijen, cikin dabara ya shirya bugun cikinshi domin yaji gaskiyar lamarin.
Aiko ranar suna d'akinsu na gidan Maigarin don tuni Safwan d'in ya baro cen garin ya dawo nan d'in saboda wahalar go and come d'in da yake yi kullum tsakanin garin da kauyensu Dijen.
Lawi ya kalleshi yaga yanda yake ta marking d'in papers d'in Test d'in da yayiwa yaran Makarantar, ya yi gyaran murya yace
"Abokina wai fa kwanan nan naga sai wani kawance kuke yi da mutuniyar taka, ko dai ka rufta ne kai ma kamar Ni?"
Safwan bai daina marking papers d'in ba yace,. "Wace mutunniyar?"
Lawi ya yi masa hararar gefe yace,. "Wace fa bayan Dije abokiyar rigimarka"
Safwan ya d'aga kafada yace,. "No ba wani abun kawai dai don naga tana da jajircewa akan karatun ne shiyasa"
Lawi ya k'ura masa Ido saboda son tabbatar da gaskiyar zancen, sannan ya sauke ajiyar zuciya yace,
"Da dai ka sanar dani gaskiya Abokina don bana son mu zo mu mato a soyayyarta daga Ni har kai"
Ba shiri Safwan ya d'ago kanshi ya kai kallonshi ga Lawin baki a bud'e zuciyarshi sai bugawa take yi da sauri da sauri, cikin b'acin Rai yace
"Kai ko ance maka zan so black cat zaka amince? Me Zan yi da karamar Yarinya irinta kuma don rashin mafadi Yar k'auye"
Lawi ya yi saurin fad'in
"Me zai hana ita din ba mace bace halan?"
Safwan cikin zafin Rai ya ajiye takardun ya mike ranshi a b'ace yace,. "Kai dai da kaga zaka iya to ka je ka yi ta yi, amman Ni kam matsayina ya girmi in lalace Kan duk wata ''ya da ke Cikin kauyen nan, musamman dai ita d'in da baka banbance komi a fuskarta sai hak'oranta da kwayar idanuwanta saboda tsabar bak'in da take dashi, cab! ALLAH ya rabani WALLAHI ku je cen ku k'arata"
Cike da jin dad'i Lawi ya bi bayan abokin na shi da kallo har ya fice, sannan ya mike tsaye cikin wani tsantsar farin ciki yace
"Gareka Lawi lokaci yayi da zaka fara farauto soyayyarka"
Aiko a gurguje ya shirya ya nufi wurin Maigari bayan sun gaisa ne ya dan sosa kanshi yana so yayi magana yana tunanin ta ina ma zai fara?, Maigarin ya kalli yanda bakinshi yake rawa alamun akwai maganar da yake so su yi amman nauyi ya hanashi fad'a, shiyasa ya sallami sauran mutanen da ke wajen sannan ya kalli Lawi yana murmushi yace,
"Lafiya yarona na ganka haka? Ga dukkan alamu dai akwai zancen da ka zo man da shi, to kar ka ji komi nasha gaya maka ka d'auka tamkar cewa Ni din Mahaifinka ne, don haka kar ka ji shakkun tunkarata da kowace irin magana ce "
Lawi ya kara sunne kanshi yace,. "Wata yarinya ce na gani Ina so a garin nan, to shine nike jin tsoron bayyana kaina gareta gashi bansan al'adar garin ba"
Maigarin ya washe bakinshi yace
"A'ah to Masha ALLAHU ita ko wace mai sa'a ce wannan ???"
Lawi cikin zumudinshi yace,. "Wata yarinya ce naji ana kiranta Dije"
Ba Maigarin ba harta Liman da ke zaune da carbinshi yana ja sai da ya zaro Ido, cikin fargaba Maigarin yace
"Wace Dijen ba dai ta gidan Malam Sanda ba?"
Lawi cikin jin nauyi yace "Eh ita ranka ya dad'e"
Maigarin ya sauke ajiyar zuciya yace,. "To dai lamarin aure bincike ake so a fara yi kafin a tsunduma kan lamarin, yana da kyau ka fara binciken halinta kafin ka fito da bukatarka gareta"