Sashe 47
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Safwan kam shigewar su Zee ciki yayi dai dai da dawowar natsuwarshi, ya kai kallonshi ga inda yake tsammanin ganin Dijen sai dai kuma wayam bata nan, ya wara idanuwanshi a masifance domin ya hango ta ina zai ganta ya sauke fushinshi akanta, sai dai kuma bata ba dalilinta a falon duka, a harzuƙe ya yi wurin Surayya yace
"Ina magen yarinyar cen ta tafi???"
Sury cikin firgici tace
"WALLAHi Ni ma bansan inda ta je ba yayanmu"
Safwan ya kaiwa iska duka sannan ya bar wajen ya sake dawowa ya ce da ita, "to ki yi gaggawar dubo man ita yanzun nan idan ba haka ba WALLAHi yau daga ke har ita sai kun san dani kuke zance"
Cikin rawar jiki Surry ta miƙe ta yi ɗakinsu domin ta gani Dijen tana cen ko kuwa, sai dai ta duba ko'ina Dijen bata gidan take ta sanar da shi yana huci ya yi wurin Hajiya, sai dai tuno ɗakin da mutane yasa ya ja ribas dole tare da furzo iska mai zafi a bakinshi yana wani bubbuga kanshi alamun ta saka shi a tension da yawa.
Yana nan tsaye sai ga Fiddo ta fito tare da su Zee tana ganinshi ta yi saurin zuwa wurinshi tace, "big bros WALLAHi yau idan ka kama yarinyar nan ka ci ubanta da kyau da kyau, don ni kaina yau sai na tayaka mun ci uban shegiya......"
Kallon da Safwan ɗin ya yi mata ne yasa ta yi saurin cewa da su Zee "Aunty ku zo mu je ku ci abincin kafin mu je wajen da za'a yi event ɗin"
Zee ta yatsina fuska ta kalli Safwan tace,
"Barshi kawai Ƙanwata ni yanzu ma zamu koma gida"
Safwan ya yi saurin zaro ido cikin wani sabon tashin hankali ya marairece fuska yace, "Sorry Unique ke ma kinsan ke ce dream ɗina safe da rana, ke ce wadda nike mafalkin aure a kowane lokaci, wannan yarinyar ba kowa ba ce a wurinmu face ƴar aiki kamar yanda kika ji Fiddo ta sanar da ke tun farko"
Zee ta yi masa wani arnen kallo mai cike da ma'anoni sannan ta nufi hanyar fita ƙawarta ta riƙo hannunta, cikin wayancewa ta ce da Fiddo mu je ki kaimu wajen da za'a yi bikin, Fiddo cike da damuwa ta ce "to ku yi haƙuri ku ci abincin mana kunga kun kwaso tafiya ga shi ko ruwa ma baku sha ba"
Ƙawarta Ruma ta yi murmushi ta ce "ok to mu je mu ɗin ai sai mu yi sauri mu kammala"
Fiddo cike da jin daɗi ta kai su ɗakinsu da ta riga da ta shirya shi tsaf saboda tarbonsu, ta nuna masu toilet sannan ta fito zuwa kwaso masu kayan abincin, Safwan da ke tsaye jiki ba kuzari damuwa fal ranshi yace
"Zo nan ki ji"
Fiddo ta ƙaraso wajenshi cikin sassauta murya yace,. "Don Allah ki yi duk yanda zaki yi ki nuna mata cewa ba wani abu tsakaninmu da yarinyar cen, don WALLAHi idan bata amince ba yau sai na ci uban yarinyar nan a gidan nan"
Hajiya da ke bayansu cikin shirinta na fita zuwa bikin ta ce,
"Wa za'a ci wa Uba kuma a gidan nan yau?"
Safwan ya gyara tsayuwarshi tare da sosai kai yace,
"Wata ce Hajiyarmu"
Hajiya ta ce "ALLAH ya taimakeka to tunda ba Khadijah kake nufi ba don WALLAHi idan har da ita kake ka kuskura naji ka daketa akan wata sai na baka mamaki"
Tana ƙare faɗar haka ta sa kai ta tafiyarta, Safwan da Fiddo suka bita da kallo har ta wuce, sannan ya nufi ɗakinsu Fiddon ranshi a matuƙar ɓace saboda jin haushin taka masa burkin da Hajiya Mama take yi akan Dije.
Yana shiga ya taradda Zee dunƙule tana kuka ƙawarta tana lallashinta tana bata baki, tana ganinshi ta yi saurin zuwa ta cakumo rigarshi cikin kuka tace
"Daman abunda ka shirya man kenan Shiyasa ka matsa akan in zo bikin ƙanwarka??, To na zo na gani tabbas kana da matar da zaka aura ƴar Uwarka ALLAH ya baku zaman lafiya Ni na haƙura na bar mata ALLAH ya bani dangana, amman ka sani sonka shine ajalina idan ka ji saƙon mutuwa to shine sila"
Safwan ya dafe goshinshi cike da wani takaici da ruɗewa yace, "ki yi haƙuri my fiance na gaya maki yar aikin gidan nan ce, tukunna ma ina wadda na taɓa sanar da ke an so a haɗamu aure da ita to ai itace wannan"
Ta yi masa wani kallo mai cike da tuhuma tace, "eh kam lalle yar uwar taku ce yanzu ta zama yar aikin naku ko? Hmm! To bari ka ji bazan ja abun da tsauri ba na haƙura na bar mata kai kawai"
Tana ƙare faɗar maganar ta fisgo gyalenta da ƙarfi zata fita ya yi saurin riƙo hannunta cikin damuwa yace "plsss Zee ki fahimceni mana, wallahil'azim a shirye nike da in aureki a kowane lokaci, ki bani dama domin in tabbatar maki da hakan idan kin aminta yanzu ma kafin mu koma ayi auren kawai mu tafi abun mu cen mu zauna idan kinsan hakan zai kwantar maki da hankali"
Zee ta kalleshi zuciyarta cike da jin daɗi tace, "promise?"..
Yace "promise"
Sannan ta rufe fuskarta tana dariyar jin daɗi, Safwan ma ba shiri ya mayar mata da martanin dariyarta zuciyarshi fess saboda ganin ya tufke abunda Dije ta warware masa.
Fiddo ta shigo ta ajiye kayan abincin tana wasar bakin jin daɗin ganin Zee ta washe tace, "masha ALLAH Auntynmu har naji daɗi da kika saki fuskarki, yayanmu ba shi da wata matar da zai aura a yanzu face ke, don wannan munafukar yarinyar da kika gani itace take sonshi sai dai shi ko kaɗan ba ya sonta, ta yi masa haka ne a gabanki don kawai ta haɗaku faɗa, daman gurinta bai wuce ki yi zuciya ki bar mata big bros, to don ALLAh Auntynmu ki bata kunya kada ki bari ta rabaki da yayanmu kinji"
Zee ta washe baki tace, "na gode ƙanwata ina jin daɗin yanda kike sona ke da yayanki, kuma insha ALLAHu bazan taɓa nuna damuwata akan wani abu da zata sake yi ba, matuƙar ba my soul ne ya nuna kulawarshi akanta ba, to agaskiya anan kam bazan taɓa jura ba don Ina kishin inga wata mace ta raɓeshi bayan ni WALLAHi"
Fiddo ta fara zuba masu abincin tace, ",kwantar da hankalinki don ba ma zai kulatan ba saboda daman cen itace kawai da baƙin nacinta"
Haka dai Fiddo ta yi ta basu kulawa tana wanke zuciyar Zee daga tsatsar da Dije ta sakawa ruhinta, har suka ƙare komi cikin kulawar Fiddo sannan suka ajiye motarta da suka zo da ita Safwan ya ɗaukesu suka tafi bikin.
Shigarsu hall ɗin ke da wuya Safwan ya hango Dije tsakiyar fili tana ta cashewa abunta, zuciyarshi a take ta zo wuya saboda ganin yanda ƙaton hall ɗin ya cika ya batse tsakanin maza da mata.
Fiddo ta wuce da su Zee tana ta gabatar da ita ga ƴan'uwa da abokan arziƙi, sai dai abinda bata sani ba mutanen da yawa wadañda basu san da zancen auren ba sunyi mamakin auren da Safwan ɗin zai sake yi, bayan ga Dije dake hannun Hajiya kuma itama tana amsa sunan Matarshi.
Safwan kam cikin dubara ya fice ya sa wata ƙawar Surayya ta kira masa Dijen, sai dai cikin rashin Sa'a Dijen ta ƙi biyo ƙawar Surryn saboda gargaɗin da Hajiya ta yi mata akan kada ta biyewa Safwan ɗin ya daketa a banza, ƙiri ƙiri tace da ƙawar Surryn Hajiya tace kada ta fita ko'ina, dole haka ƙawar taje ta sanar da shi, aiko ya ƙara hawa akan fushin da Dijen ta saka shi, ya yi ƙwafa ya koma hall ɗin
Sai dai rawar da ya ga tana ta cisga ne yasa shi dafe goshinshi ba shiri, ranshi a ɓace ya kasa haƙuri ya nufi wurinta gadan gadan da nufin kai mata wani bahagon mari, tana hangoshi ta yi saurin ficewa filin ta nufi wurin Hajiyar tana haki, ya wayance ya fara zubawa Surry likin kuɗi daga nan ƴan'uwa suka cika filin suna yi masa liƙi yana yi masu shi ma, ta ko'ina sai zubo kuɗi ake yi har sai da mc ya bada umurnin kowa ya koma ya zauna abar Amarya kawai a tsakar fili.
Ganin hakan ya baiwa Zee damar fitowa ita da ƙawarta suka fara watsawa Surry farfaru bugun Abuja, Hajiya Mama ta ciro kuɗi a jakarta ta miƙa wa Dije tace itama ta je ta watsa, cikin jin daɗi ta karɓa ta isa wurin ta fara mannawa Surryn kuɗin sannan ta dawo tana mannawa Zee cikin murya ƙasa ƙasa tace
"Da kin daina wannan zaƙewa tunda dai har yanzu baki riga da kin shigo familyn ba, amman kuma ba komi a hakan ma muna godiya, sai dai kuma ga shawara ki adana sauran kuɗinki don rabawa malamai su ji daɗin yi maki addu'ar ƙwato zuciyar wanda ake yi dominshi"
Saboda salon yaudara irin na Dije tana liƙa mata kuɗin fuskarta a sake take maganar, wanda bai ji ba ba zai taɓa fahimtar cewa wai wata baƙar magana ce take faɗa mata ba, don shi kanshi Safwan ɗin ya yi mamakin ganin Dijen tana wasar baki ga Zee, uwa uba ma har da su watsa kuɗi don a ɗauka cewa bata san zafin kishi ba.
Har aka watse taron Zee maganganun Dije suna yawo cikin kwanyar kanta, sai dai idan ta tuno da zancen aurensu da Safwan ɗin da ya zo mata da shi sai ta ji wani sassafci a ranta, duk da tasan cewa itama za'a sha fama da ita kafin a janye zancen auren wani da ke kanta.
Dije kam har aka shiga bacci bata bari sun haɗu da Safwan ba, saboda ma tunda ya fita raka Zee gidan ƴan'uwasu da suka sauka a cen, bai dawo gidan ba har sai da dare ya tsala sannan ya dawo ya shige zuciyarshi cike da jin daɗin shima ya kusa angwancewa, sai dai wani sashe na zuciyarshi yana ingizashi akan ya koyawa Dije hankali kafin ya bar garin, amman yana jin tsoron abunda zai janyowa kanshi wajen Hajiya Mama.
"Ina magen yarinyar cen ta tafi???"
Sury cikin firgici tace
"WALLAHi Ni ma bansan inda ta je ba yayanmu"
Safwan ya kaiwa iska duka sannan ya bar wajen ya sake dawowa ya ce da ita, "to ki yi gaggawar dubo man ita yanzun nan idan ba haka ba WALLAHi yau daga ke har ita sai kun san dani kuke zance"
Cikin rawar jiki Surry ta miƙe ta yi ɗakinsu domin ta gani Dijen tana cen ko kuwa, sai dai ta duba ko'ina Dijen bata gidan take ta sanar da shi yana huci ya yi wurin Hajiya, sai dai tuno ɗakin da mutane yasa ya ja ribas dole tare da furzo iska mai zafi a bakinshi yana wani bubbuga kanshi alamun ta saka shi a tension da yawa.
Yana nan tsaye sai ga Fiddo ta fito tare da su Zee tana ganinshi ta yi saurin zuwa wurinshi tace, "big bros WALLAHi yau idan ka kama yarinyar nan ka ci ubanta da kyau da kyau, don ni kaina yau sai na tayaka mun ci uban shegiya......"
Kallon da Safwan ɗin ya yi mata ne yasa ta yi saurin cewa da su Zee "Aunty ku zo mu je ku ci abincin kafin mu je wajen da za'a yi event ɗin"
Zee ta yatsina fuska ta kalli Safwan tace,
"Barshi kawai Ƙanwata ni yanzu ma zamu koma gida"
Safwan ya yi saurin zaro ido cikin wani sabon tashin hankali ya marairece fuska yace, "Sorry Unique ke ma kinsan ke ce dream ɗina safe da rana, ke ce wadda nike mafalkin aure a kowane lokaci, wannan yarinyar ba kowa ba ce a wurinmu face ƴar aiki kamar yanda kika ji Fiddo ta sanar da ke tun farko"
Zee ta yi masa wani arnen kallo mai cike da ma'anoni sannan ta nufi hanyar fita ƙawarta ta riƙo hannunta, cikin wayancewa ta ce da Fiddo mu je ki kaimu wajen da za'a yi bikin, Fiddo cike da damuwa ta ce "to ku yi haƙuri ku ci abincin mana kunga kun kwaso tafiya ga shi ko ruwa ma baku sha ba"
Ƙawarta Ruma ta yi murmushi ta ce "ok to mu je mu ɗin ai sai mu yi sauri mu kammala"
Fiddo cike da jin daɗi ta kai su ɗakinsu da ta riga da ta shirya shi tsaf saboda tarbonsu, ta nuna masu toilet sannan ta fito zuwa kwaso masu kayan abincin, Safwan da ke tsaye jiki ba kuzari damuwa fal ranshi yace
"Zo nan ki ji"
Fiddo ta ƙaraso wajenshi cikin sassauta murya yace,. "Don Allah ki yi duk yanda zaki yi ki nuna mata cewa ba wani abu tsakaninmu da yarinyar cen, don WALLAHi idan bata amince ba yau sai na ci uban yarinyar nan a gidan nan"
Hajiya da ke bayansu cikin shirinta na fita zuwa bikin ta ce,
"Wa za'a ci wa Uba kuma a gidan nan yau?"
Safwan ya gyara tsayuwarshi tare da sosai kai yace,
"Wata ce Hajiyarmu"
Hajiya ta ce "ALLAH ya taimakeka to tunda ba Khadijah kake nufi ba don WALLAHi idan har da ita kake ka kuskura naji ka daketa akan wata sai na baka mamaki"
Tana ƙare faɗar haka ta sa kai ta tafiyarta, Safwan da Fiddo suka bita da kallo har ta wuce, sannan ya nufi ɗakinsu Fiddon ranshi a matuƙar ɓace saboda jin haushin taka masa burkin da Hajiya Mama take yi akan Dije.
Yana shiga ya taradda Zee dunƙule tana kuka ƙawarta tana lallashinta tana bata baki, tana ganinshi ta yi saurin zuwa ta cakumo rigarshi cikin kuka tace
"Daman abunda ka shirya man kenan Shiyasa ka matsa akan in zo bikin ƙanwarka??, To na zo na gani tabbas kana da matar da zaka aura ƴar Uwarka ALLAH ya baku zaman lafiya Ni na haƙura na bar mata ALLAH ya bani dangana, amman ka sani sonka shine ajalina idan ka ji saƙon mutuwa to shine sila"
Safwan ya dafe goshinshi cike da wani takaici da ruɗewa yace, "ki yi haƙuri my fiance na gaya maki yar aikin gidan nan ce, tukunna ma ina wadda na taɓa sanar da ke an so a haɗamu aure da ita to ai itace wannan"
Ta yi masa wani kallo mai cike da tuhuma tace, "eh kam lalle yar uwar taku ce yanzu ta zama yar aikin naku ko? Hmm! To bari ka ji bazan ja abun da tsauri ba na haƙura na bar mata kai kawai"
Tana ƙare faɗar maganar ta fisgo gyalenta da ƙarfi zata fita ya yi saurin riƙo hannunta cikin damuwa yace "plsss Zee ki fahimceni mana, wallahil'azim a shirye nike da in aureki a kowane lokaci, ki bani dama domin in tabbatar maki da hakan idan kin aminta yanzu ma kafin mu koma ayi auren kawai mu tafi abun mu cen mu zauna idan kinsan hakan zai kwantar maki da hankali"
Zee ta kalleshi zuciyarta cike da jin daɗi tace, "promise?"..
Yace "promise"
Sannan ta rufe fuskarta tana dariyar jin daɗi, Safwan ma ba shiri ya mayar mata da martanin dariyarta zuciyarshi fess saboda ganin ya tufke abunda Dije ta warware masa.
Fiddo ta shigo ta ajiye kayan abincin tana wasar bakin jin daɗin ganin Zee ta washe tace, "masha ALLAH Auntynmu har naji daɗi da kika saki fuskarki, yayanmu ba shi da wata matar da zai aura a yanzu face ke, don wannan munafukar yarinyar da kika gani itace take sonshi sai dai shi ko kaɗan ba ya sonta, ta yi masa haka ne a gabanki don kawai ta haɗaku faɗa, daman gurinta bai wuce ki yi zuciya ki bar mata big bros, to don ALLAh Auntynmu ki bata kunya kada ki bari ta rabaki da yayanmu kinji"
Zee ta washe baki tace, "na gode ƙanwata ina jin daɗin yanda kike sona ke da yayanki, kuma insha ALLAHu bazan taɓa nuna damuwata akan wani abu da zata sake yi ba, matuƙar ba my soul ne ya nuna kulawarshi akanta ba, to agaskiya anan kam bazan taɓa jura ba don Ina kishin inga wata mace ta raɓeshi bayan ni WALLAHi"
Fiddo ta fara zuba masu abincin tace, ",kwantar da hankalinki don ba ma zai kulatan ba saboda daman cen itace kawai da baƙin nacinta"
Haka dai Fiddo ta yi ta basu kulawa tana wanke zuciyar Zee daga tsatsar da Dije ta sakawa ruhinta, har suka ƙare komi cikin kulawar Fiddo sannan suka ajiye motarta da suka zo da ita Safwan ya ɗaukesu suka tafi bikin.
Shigarsu hall ɗin ke da wuya Safwan ya hango Dije tsakiyar fili tana ta cashewa abunta, zuciyarshi a take ta zo wuya saboda ganin yanda ƙaton hall ɗin ya cika ya batse tsakanin maza da mata.
Fiddo ta wuce da su Zee tana ta gabatar da ita ga ƴan'uwa da abokan arziƙi, sai dai abinda bata sani ba mutanen da yawa wadañda basu san da zancen auren ba sunyi mamakin auren da Safwan ɗin zai sake yi, bayan ga Dije dake hannun Hajiya kuma itama tana amsa sunan Matarshi.
Safwan kam cikin dubara ya fice ya sa wata ƙawar Surayya ta kira masa Dijen, sai dai cikin rashin Sa'a Dijen ta ƙi biyo ƙawar Surryn saboda gargaɗin da Hajiya ta yi mata akan kada ta biyewa Safwan ɗin ya daketa a banza, ƙiri ƙiri tace da ƙawar Surryn Hajiya tace kada ta fita ko'ina, dole haka ƙawar taje ta sanar da shi, aiko ya ƙara hawa akan fushin da Dijen ta saka shi, ya yi ƙwafa ya koma hall ɗin
Sai dai rawar da ya ga tana ta cisga ne yasa shi dafe goshinshi ba shiri, ranshi a ɓace ya kasa haƙuri ya nufi wurinta gadan gadan da nufin kai mata wani bahagon mari, tana hangoshi ta yi saurin ficewa filin ta nufi wurin Hajiyar tana haki, ya wayance ya fara zubawa Surry likin kuɗi daga nan ƴan'uwa suka cika filin suna yi masa liƙi yana yi masu shi ma, ta ko'ina sai zubo kuɗi ake yi har sai da mc ya bada umurnin kowa ya koma ya zauna abar Amarya kawai a tsakar fili.
Ganin hakan ya baiwa Zee damar fitowa ita da ƙawarta suka fara watsawa Surry farfaru bugun Abuja, Hajiya Mama ta ciro kuɗi a jakarta ta miƙa wa Dije tace itama ta je ta watsa, cikin jin daɗi ta karɓa ta isa wurin ta fara mannawa Surryn kuɗin sannan ta dawo tana mannawa Zee cikin murya ƙasa ƙasa tace
"Da kin daina wannan zaƙewa tunda dai har yanzu baki riga da kin shigo familyn ba, amman kuma ba komi a hakan ma muna godiya, sai dai kuma ga shawara ki adana sauran kuɗinki don rabawa malamai su ji daɗin yi maki addu'ar ƙwato zuciyar wanda ake yi dominshi"
Saboda salon yaudara irin na Dije tana liƙa mata kuɗin fuskarta a sake take maganar, wanda bai ji ba ba zai taɓa fahimtar cewa wai wata baƙar magana ce take faɗa mata ba, don shi kanshi Safwan ɗin ya yi mamakin ganin Dijen tana wasar baki ga Zee, uwa uba ma har da su watsa kuɗi don a ɗauka cewa bata san zafin kishi ba.
Har aka watse taron Zee maganganun Dije suna yawo cikin kwanyar kanta, sai dai idan ta tuno da zancen aurensu da Safwan ɗin da ya zo mata da shi sai ta ji wani sassafci a ranta, duk da tasan cewa itama za'a sha fama da ita kafin a janye zancen auren wani da ke kanta.
Dije kam har aka shiga bacci bata bari sun haɗu da Safwan ba, saboda ma tunda ya fita raka Zee gidan ƴan'uwasu da suka sauka a cen, bai dawo gidan ba har sai da dare ya tsala sannan ya dawo ya shige zuciyarshi cike da jin daɗin shima ya kusa angwancewa, sai dai wani sashe na zuciyarshi yana ingizashi akan ya koyawa Dije hankali kafin ya bar garin, amman yana jin tsoron abunda zai janyowa kanshi wajen Hajiya Mama.