Sashe 76
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yace "to ki ajiye komi ki yi zaman aurenki tsakani da ALLAH, ki sa a ranki duk duniya babu wanda ya isa ya yi maki abunda ALLAH bai yi maki ba, haka ma kaf mutanen duniyar nan idan ymza su taru akan sai sun kasheki to basu isa su kasheki ba har sai kwananki ya ƙare, don haka ki ɗauka cewa duk abunda kika ga ya sameki daga ALLAH ne, abunda ma ya kuskure maki shi ma daga ALLAH ne da kin yi hakan shikenan kin ci maganin matsalarki, ALLAH ya saukeki lafiya ke da ƴar uwarki kuma ya baku zaman lafiya a gidajen aurenku"
Dije ta rufe fuska cike da jin kunya ta ce "Ameen" cikin maƙoshi, haka suka dinga nusar da ita abubuwa da yawa masu amfanarwa sannan ta saki jiki ta dawo dai dai aka ci gaba da fira cikin raha da annushuwa.
Dije ta ce su gayar mata da Gambo da su Ladiyo, ta ɗauko sako ta bayar ta ce akai masu ace in jita, don kuwa su Ladiyo kowa dubu bibbiyu ta bada akai masu Balan duduwa dubu biyar tare da Duduwar itama dubu biyu, sannan saƙon Maigari da Matanshi na shadda da atamfofi, Malaminta na makarantar allo ma da saƙonshi tare da ɗalibanta na makarantar da ta baiwa sababbin goma goma ta ce a raba masu su yi mata addu'a, abun dai masha ALLAH gwanin burgewa Dukansu kowane zuciya cike da tsantsar farin ciki da jin daɗi, tare da yi wa ALLAH godiya da ya baiwa Dije miji ɗaya tamkar da goma kuma ya haɗasu da mutanen kirki.
Tun cikin daren su Hajiya Mama suka zo suka yi sallama da juna shiyasa tun da sassafe suka fara shirin barin garin, Dije sai kuka take ci ana lallashinta har motarsu ta ɗaga ta faɗi ƙasa tana ta kuka gwanin ban tausayi, sai da Malaminta ya yi mata jan ido sannan ta fara shiga taitayinta, don ya yi mata alƙawarin in dai har ta bar kukan to itama zai kaita idan cikinta ya yi ƙwari ta je ta ganosu, sannan ne ya samo kanta ya koma aikin ban baki tare da daɗin baki kala kala.
Sati ɗaya a tsakani takardar samun aikinshi ta fito inda kai tsaye aka postershi Abuja, tare da zunzurutun albashi mai tsoka da kyautar sabuwar mota da gida a garin Abuja, mutane da yan uwa sai murna ake yi masu don Lawi kanshi sai da ya zo ta ya murna tun daga Gombe har Yola tare da Amaryarshi da tuni itama ta kusa zama Mama, don kuwa ɗauke take da cikinta ɗan wata biyar itama kyakkyawar bafulatana da ita masha ALLAH, kwanansu ɗaya a gidan suka koma cikin kewar juna, saboda jinin matar Lawin mai suna Maryam da ya haɗu cikin lokaci ƙanƙani da na Dijen Baffahn, saboda itama ba laifi akwai barkwanci da son wasa da dariya gata da saurin sabo.
Lokacin da aka ɗibar masa da ya cika ya fara zuwa aiki, fiddo da wasu dattijai biyu suka dawo gidan suna taya Dijen Baffah zama, atakure ya yi sati ɗaya ya dawo Yola cike da ɗokin Matarshi, don ba ƙaramin sabo ya yiwa kanshi da ita ba, shiyasa ya ji gaba ɗaya zama garin bai masa daɗi ba, dole ya kwashi Matarshi suka nufi garin Abuja a gidansu da aka basu, don ya so har sai ta haifu sannan su dawo nan ɗin , to amman ya ga hakan bazata samu ba don sabon da ta yi masa kanta, ga shi kuma shi matan banza basu gabanshi don ko na kwarai ɗin baya kula shirginsu bale har na banzan.
Aunty Ummi da su Husnah sai murna suke yi Dijen ta dawo kusa da su, shiyasa kullum suna tare basu wannan wurin shaƙatawa basu wurin ciye ciye da tanɗe tanɗe da lashe lashe, kafin ka ce me idon Dijen sun ƙara buɗewa cikin garin Abuja, don kuwa ita kanta tasan wurare da yawa.
Da zama ma ya yi daɗi sai ga shi da koya mata driving, tana jin tsoro tana fargaba haka yake koya mata ita duk da bata so, saboda bala'in tsoron da ta ke ji amman a hankali ko wata biyu basu rufa ba a garin ta fara iyawa, don ya ce da ta iya zai siya mata tata idan ALLAH ya sauke ta lfy, ko don ta fara zuwa makarantar da take kwaɗayi ba tare da takura ba, don saboda busyn da yake yi a wurin aikin nashi kullum, gashi kuma yana son ta yi karatun don shine babban gatan da zai mata a rayuwa, saboda akwai rayuwa akwai mutuwa in mune yau ba mune gobe ba, Yana da kyau mace ta dogara da kanta ko don ranar da kika rasa mai tallafa maki ki kula da kanki da yaranki da iyaye da ƴan uwanki duka.
****
ZEE Kam tun bata saba da aikin wahala ba har yanzu ya fara zame mata jiki, don ta yi ta tserewa tana zuwa gidajen yan uwa ana dawo da ita wurin Baabaah Asaben, don kowa cike yake da haushinta ba kaɗan ba musamman ƙin Aminu da ta yi tare da abun kunyar da ta janyo masu, Mahaifiyarta kanta da ta je gidan take korota ta fito tare da yi mata kashedi da gargadin cewa duk ta yarda Daddynta yasan halin da take ciki a gidan gwaggonta sai ta tsine mata, tana kuka take komawa yanzu har ta haƙura don kanta ta daina gudun, ganin hakan yasa Gwaggon ta fara sassafta mata daga matsin lambar da take yi mata, don kuwa ta ladaftu sosai kuma ta gano irin kuskuren da ta so aikatawa, ta yiwa ALLAH godiya da yasa Ruma bata bari ta aikata mugun abun da ta yi niyya ba, ga shi ta rasa Safwan ɗin kuma Aminun ma ta rasa shi don kuwa yanzu haka ƙawarta Sadiya yake aure, don Ruma ya so aura ta nuna masa amincinta da Zee bazata iya aurenshi ba, Sadiya kam hannu biyu ta karɓeshi yanzu haka da ƴarsu tana nan mai sunan Mahaifiyarshi.
Zee ta shiga damuwar rashin jin Safwan ɗin da kullum take tsumayin zuwanshi gareta ya ce ta dawo, amman shirun da ta jini yayi yawa ne ta fara tunanin binshi da kanta, don laifin da ta aikata masa ko ma wanene dole ne ya sallamata, kasancewar tasan numbarshi akanta yasa da Ruma ta zo ta ari wayarta ta kirashi, kasancewar baya da layin Rumar a lokacin shiyasa daga baya ya bi miss call ɗin da ya gani kusan goma sha bai ma san an kira ba, sai dai jin murya Ruma yasa ya yi saurin faɗin
"Wacece ??"
Jikinta yana rawa ta ce "Rumasa'u ce ƙawar Zee don ALLAH ka yi haƙuri da abunda ta aikata ita ce ta kiraka ɗazu da naje wurinta ta ari wayar ta kiraka baka ɗaga ba, saboda WALLAhi yanzu Zee ta canza sosai kuma ta yi nadamar abunda ta aikata"
Cike da mamaki ya ce
"Daga ke har ita kada ku sake nemana matuƙar kuna son kanku zaman lafiya"
Ƙittt! Ya kashe wayarshi gaba ɗaya cike da jin haushinsu duka, Dije da ke shigowa ɗakin da tiren coffee'nshi ta ajiye tiren akan stool ta ɗauki cup ɗin ta zauna tana kallonshi tare da nazarin yanayi shi, sannan ya zura hannu da nufin ya karɓi kofin ta riƙe gam idonta a kanshi ta ce
"Wa ya taɓo man Habibyna? Don haka na fita na barshi ba plss ka yi haƙuri ko ma mene saboda zama cikin mutane sai da kai zuciya nesa Mijina"
Cike da jin daɗin kalamanta ya duƙo ya kurɓi coffee'n sannan ya ce, "waɗannan ba irin mutanen da kike tunani bane, ki share da su kawai don na riga da na shafe babinsu a rayuwata"
Dije ta miƙa masa cup ɗin ya karɓa ya dinga sha a hankali har ya shanye, sannan ta karɓi cup ɗin ta ajiye ta kalle da kyau ta riƙo hannunshi ta haɗe da nata ta dunƙule waje ɗaya ta ce
"Wacece ta kiraka?"
Cikin diriricewa ya ce
"Ruma ce ƙawar Zee take rokona akan inyi haƙuri in yafe wa Zee wai ta yi nadamar abunda ta aikata"
Dije ta ji wani ɓacin rai ya ziyarci zuciyarta, amman ta yi dubarar ɓoye damuwarta ta ce
"To kai kuma me ka ce?"
Ya ɓata fuska tamkar a lokacin sannan ya sanar da ita abinda ya ce da ita, Dije ta ɗauko hannunshi ta ɗora a saman cikinta da ya fara turowa kaɗan, ya bita da kallon ƙarin ba'asi sannan ta kashe masa ido ɗaya ta ce
"Nasan kana sonshi ko?"
Ya maka mata wata harara, ta zunɓuro baki ta ce "Ni dai ka daina hararata amsa nake nema"
Ya yi saurin faɗin
"Yo idan ma ba don kina son kawo man reni ba ta ya zaki kalli tsabar idona ki tambayeni ina son abunda Ni da kaina sai da na zuba ƙarfi kafin in sameshi?, Kin fi kowa sani kaf duniya babu wanda zai fini son abunda ke cikinki ko da ko ke ɗin ce da zaki haifo man shi"
Dije ta ƙumshe dariyarta ta ce "au abun har ya kai cen?"
Yana dariya ya ce "ya ma wuce ai" tace "well yanzu idan na ce ka yi mani wata alfarma saboda son da kake masa zaka yi?"
Cikin sauri ya ce
",Me zai hana in dai har hakan zai faranta ranki da unborn ɗina"
Ta ce "to in ko haka ne bari in zube ƙasa in rok'i alfarmar don ina son ayi saurin amsa mani"
Ta sauko ƙasa zata durƙusa ya riƙo hannunta tare da dawo da ita kan gadon ta zauna ya ce
"Faɗi buƙatarki kawai ba sai kin cutar man da abun ciki ba"
Dije ta yi dariya cike da jin daɗi sannan ta riƙo hannunshi ta matse gam ido cikin ido ta ce
"Daga Ni har babynka Muna so ka dawo muna da Aunty Zee ko don mu sami abokiyar shawara tunda har an ce ta yi nadamar abunda ta aikata"
Cike da ƙunar zuciya ya ƙwace hannunshi tare da miƙewa tsaye ya kalleta ranshi a ɓace ya ce
"Wannan rana da wannan lokaci su zamo na ƙarshe da zaki sake tunkarata da wannan zance"
Dije ta rufe fuska cike da jin kunya ta ce "Ameen" cikin maƙoshi, haka suka dinga nusar da ita abubuwa da yawa masu amfanarwa sannan ta saki jiki ta dawo dai dai aka ci gaba da fira cikin raha da annushuwa.
Dije ta ce su gayar mata da Gambo da su Ladiyo, ta ɗauko sako ta bayar ta ce akai masu ace in jita, don kuwa su Ladiyo kowa dubu bibbiyu ta bada akai masu Balan duduwa dubu biyar tare da Duduwar itama dubu biyu, sannan saƙon Maigari da Matanshi na shadda da atamfofi, Malaminta na makarantar allo ma da saƙonshi tare da ɗalibanta na makarantar da ta baiwa sababbin goma goma ta ce a raba masu su yi mata addu'a, abun dai masha ALLAH gwanin burgewa Dukansu kowane zuciya cike da tsantsar farin ciki da jin daɗi, tare da yi wa ALLAH godiya da ya baiwa Dije miji ɗaya tamkar da goma kuma ya haɗasu da mutanen kirki.
Tun cikin daren su Hajiya Mama suka zo suka yi sallama da juna shiyasa tun da sassafe suka fara shirin barin garin, Dije sai kuka take ci ana lallashinta har motarsu ta ɗaga ta faɗi ƙasa tana ta kuka gwanin ban tausayi, sai da Malaminta ya yi mata jan ido sannan ta fara shiga taitayinta, don ya yi mata alƙawarin in dai har ta bar kukan to itama zai kaita idan cikinta ya yi ƙwari ta je ta ganosu, sannan ne ya samo kanta ya koma aikin ban baki tare da daɗin baki kala kala.
Sati ɗaya a tsakani takardar samun aikinshi ta fito inda kai tsaye aka postershi Abuja, tare da zunzurutun albashi mai tsoka da kyautar sabuwar mota da gida a garin Abuja, mutane da yan uwa sai murna ake yi masu don Lawi kanshi sai da ya zo ta ya murna tun daga Gombe har Yola tare da Amaryarshi da tuni itama ta kusa zama Mama, don kuwa ɗauke take da cikinta ɗan wata biyar itama kyakkyawar bafulatana da ita masha ALLAH, kwanansu ɗaya a gidan suka koma cikin kewar juna, saboda jinin matar Lawin mai suna Maryam da ya haɗu cikin lokaci ƙanƙani da na Dijen Baffahn, saboda itama ba laifi akwai barkwanci da son wasa da dariya gata da saurin sabo.
Lokacin da aka ɗibar masa da ya cika ya fara zuwa aiki, fiddo da wasu dattijai biyu suka dawo gidan suna taya Dijen Baffah zama, atakure ya yi sati ɗaya ya dawo Yola cike da ɗokin Matarshi, don ba ƙaramin sabo ya yiwa kanshi da ita ba, shiyasa ya ji gaba ɗaya zama garin bai masa daɗi ba, dole ya kwashi Matarshi suka nufi garin Abuja a gidansu da aka basu, don ya so har sai ta haifu sannan su dawo nan ɗin , to amman ya ga hakan bazata samu ba don sabon da ta yi masa kanta, ga shi kuma shi matan banza basu gabanshi don ko na kwarai ɗin baya kula shirginsu bale har na banzan.
Aunty Ummi da su Husnah sai murna suke yi Dijen ta dawo kusa da su, shiyasa kullum suna tare basu wannan wurin shaƙatawa basu wurin ciye ciye da tanɗe tanɗe da lashe lashe, kafin ka ce me idon Dijen sun ƙara buɗewa cikin garin Abuja, don kuwa ita kanta tasan wurare da yawa.
Da zama ma ya yi daɗi sai ga shi da koya mata driving, tana jin tsoro tana fargaba haka yake koya mata ita duk da bata so, saboda bala'in tsoron da ta ke ji amman a hankali ko wata biyu basu rufa ba a garin ta fara iyawa, don ya ce da ta iya zai siya mata tata idan ALLAH ya sauke ta lfy, ko don ta fara zuwa makarantar da take kwaɗayi ba tare da takura ba, don saboda busyn da yake yi a wurin aikin nashi kullum, gashi kuma yana son ta yi karatun don shine babban gatan da zai mata a rayuwa, saboda akwai rayuwa akwai mutuwa in mune yau ba mune gobe ba, Yana da kyau mace ta dogara da kanta ko don ranar da kika rasa mai tallafa maki ki kula da kanki da yaranki da iyaye da ƴan uwanki duka.
****
ZEE Kam tun bata saba da aikin wahala ba har yanzu ya fara zame mata jiki, don ta yi ta tserewa tana zuwa gidajen yan uwa ana dawo da ita wurin Baabaah Asaben, don kowa cike yake da haushinta ba kaɗan ba musamman ƙin Aminu da ta yi tare da abun kunyar da ta janyo masu, Mahaifiyarta kanta da ta je gidan take korota ta fito tare da yi mata kashedi da gargadin cewa duk ta yarda Daddynta yasan halin da take ciki a gidan gwaggonta sai ta tsine mata, tana kuka take komawa yanzu har ta haƙura don kanta ta daina gudun, ganin hakan yasa Gwaggon ta fara sassafta mata daga matsin lambar da take yi mata, don kuwa ta ladaftu sosai kuma ta gano irin kuskuren da ta so aikatawa, ta yiwa ALLAH godiya da yasa Ruma bata bari ta aikata mugun abun da ta yi niyya ba, ga shi ta rasa Safwan ɗin kuma Aminun ma ta rasa shi don kuwa yanzu haka ƙawarta Sadiya yake aure, don Ruma ya so aura ta nuna masa amincinta da Zee bazata iya aurenshi ba, Sadiya kam hannu biyu ta karɓeshi yanzu haka da ƴarsu tana nan mai sunan Mahaifiyarshi.
Zee ta shiga damuwar rashin jin Safwan ɗin da kullum take tsumayin zuwanshi gareta ya ce ta dawo, amman shirun da ta jini yayi yawa ne ta fara tunanin binshi da kanta, don laifin da ta aikata masa ko ma wanene dole ne ya sallamata, kasancewar tasan numbarshi akanta yasa da Ruma ta zo ta ari wayarta ta kirashi, kasancewar baya da layin Rumar a lokacin shiyasa daga baya ya bi miss call ɗin da ya gani kusan goma sha bai ma san an kira ba, sai dai jin murya Ruma yasa ya yi saurin faɗin
"Wacece ??"
Jikinta yana rawa ta ce "Rumasa'u ce ƙawar Zee don ALLAH ka yi haƙuri da abunda ta aikata ita ce ta kiraka ɗazu da naje wurinta ta ari wayar ta kiraka baka ɗaga ba, saboda WALLAhi yanzu Zee ta canza sosai kuma ta yi nadamar abunda ta aikata"
Cike da mamaki ya ce
"Daga ke har ita kada ku sake nemana matuƙar kuna son kanku zaman lafiya"
Ƙittt! Ya kashe wayarshi gaba ɗaya cike da jin haushinsu duka, Dije da ke shigowa ɗakin da tiren coffee'nshi ta ajiye tiren akan stool ta ɗauki cup ɗin ta zauna tana kallonshi tare da nazarin yanayi shi, sannan ya zura hannu da nufin ya karɓi kofin ta riƙe gam idonta a kanshi ta ce
"Wa ya taɓo man Habibyna? Don haka na fita na barshi ba plss ka yi haƙuri ko ma mene saboda zama cikin mutane sai da kai zuciya nesa Mijina"
Cike da jin daɗin kalamanta ya duƙo ya kurɓi coffee'n sannan ya ce, "waɗannan ba irin mutanen da kike tunani bane, ki share da su kawai don na riga da na shafe babinsu a rayuwata"
Dije ta miƙa masa cup ɗin ya karɓa ya dinga sha a hankali har ya shanye, sannan ta karɓi cup ɗin ta ajiye ta kalle da kyau ta riƙo hannunshi ta haɗe da nata ta dunƙule waje ɗaya ta ce
"Wacece ta kiraka?"
Cikin diriricewa ya ce
"Ruma ce ƙawar Zee take rokona akan inyi haƙuri in yafe wa Zee wai ta yi nadamar abunda ta aikata"
Dije ta ji wani ɓacin rai ya ziyarci zuciyarta, amman ta yi dubarar ɓoye damuwarta ta ce
"To kai kuma me ka ce?"
Ya ɓata fuska tamkar a lokacin sannan ya sanar da ita abinda ya ce da ita, Dije ta ɗauko hannunshi ta ɗora a saman cikinta da ya fara turowa kaɗan, ya bita da kallon ƙarin ba'asi sannan ta kashe masa ido ɗaya ta ce
"Nasan kana sonshi ko?"
Ya maka mata wata harara, ta zunɓuro baki ta ce "Ni dai ka daina hararata amsa nake nema"
Ya yi saurin faɗin
"Yo idan ma ba don kina son kawo man reni ba ta ya zaki kalli tsabar idona ki tambayeni ina son abunda Ni da kaina sai da na zuba ƙarfi kafin in sameshi?, Kin fi kowa sani kaf duniya babu wanda zai fini son abunda ke cikinki ko da ko ke ɗin ce da zaki haifo man shi"
Dije ta ƙumshe dariyarta ta ce "au abun har ya kai cen?"
Yana dariya ya ce "ya ma wuce ai" tace "well yanzu idan na ce ka yi mani wata alfarma saboda son da kake masa zaka yi?"
Cikin sauri ya ce
",Me zai hana in dai har hakan zai faranta ranki da unborn ɗina"
Ta ce "to in ko haka ne bari in zube ƙasa in rok'i alfarmar don ina son ayi saurin amsa mani"
Ta sauko ƙasa zata durƙusa ya riƙo hannunta tare da dawo da ita kan gadon ta zauna ya ce
"Faɗi buƙatarki kawai ba sai kin cutar man da abun ciki ba"
Dije ta yi dariya cike da jin daɗi sannan ta riƙo hannunshi ta matse gam ido cikin ido ta ce
"Daga Ni har babynka Muna so ka dawo muna da Aunty Zee ko don mu sami abokiyar shawara tunda har an ce ta yi nadamar abunda ta aikata"
Cike da ƙunar zuciya ya ƙwace hannunshi tare da miƙewa tsaye ya kalleta ranshi a ɓace ya ce
"Wannan rana da wannan lokaci su zamo na ƙarshe da zaki sake tunkarata da wannan zance"