Sashe 31
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*BAƘON YANAYI ne sunan Book ɗin don haka idan kin san baki karantashi ba to ki garzayo da gudunki don kar ayi babu ke, da 300 kacal zaki sameshi a complete ɗinshi ki yi yanda kike so, don ke da kanki zaki banbance tsakanin tea da shayi kada ki bari a yi babu ke salonshi daban ya ke da saura don tun daga sunan zaku gane cewa fa shi ɗin na daban ne, ga mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09032685442 sai na ji ku👍🏻😅*
*Lamba ta 32*
Dije kam kwana biyu da zuwanta Yola Hajiya Mama ta sa Safwan ya fara yi mata lesson, saboda a cewarta don ta sami ƙarfin gwiwar tunkarar makarantar da za'a sakata da kyau, aiko sai ga shi duk da kyarar da yake yi mata hakan bai hanata fahimtar karatun da yake koya mata ba, don wannan karon ma ta ci Sa'a da Hausa ya ke fahimtar da ita duk wani abund bata gane ba, don wani zubin ma Hajiya Mama a gabanta ake karatun saboda cin zalin Dije da yake yi, duk da aranta wani lokaci sai ta ƙudurta ramawa sau kuma ta tuno huɗubar da Baffah'nta ya yi mata sai ta fasa, sai dai ta yi ta binshi da harara tana cizon yatsa saboda kullum cikin dare sai ta yi kukan rashin ganinsu.
Sai dai ta samu Surry da Hajiya Mama suna ina ka aza da ita komi take buƙata ko da bata faɗa ba yi mata ake yi, abinci ma kala kala ake baje mata ta ci wanda take so, Fiddo kam yanzu tsakaninta da Dije sai harara da murguɗar baki saboda faɗan da Hajiya Mama ta yi mata sosai akan Dijen, tare da gargaɗi mai tsanani akan duk ta sake yi wa Dije gori ko ta ci zarafinta sai ta saɓa mata.
A yau ma sati ɗaya da zuwan Dije gidan Garin suna babban falon gidan ne suna karatun kamar kullum, Safwan yana koya mata karatun tana gyangyaɗin Bacci don daman cen Dije ba gwanar firar dare ba ce, jin haushin baccin da take so ta yi bayan Hajiyar ta hana shi fita zuwa inda ya so ya je yasa ya fakaici idon Hajiya Mamar, ya janyo mata dogon tsoronta da ya fito cikin hular da ke saman kanta, cikin ƙeta ya janyo tsoron da ƙarfi ba shiri Dije ta ƙwallah ƙara tare da dunƙulewa tana kuka mai cike da takaicin hanata baccin da yake yi da muguntarshi kala kala.
Hajiya Mama ta yi saurin faɗin,. "Ka kiyayeni Sawan me ta yi maka yanzu kuma?"
Safwan ya sosa kanshi cikin sauri yace,. "Bacci fa take yi Hajiya Mama don ta renani ga shi ƙiri ƙiri ta sa an hanani fita kuma ta zo tana yi wa mutane baccin renin wayo"
Hajiya Mama ta tashi cikin sauri ta riƙo hannunta tace,. "Tashi mu je ki yi baccinki tunda karatun na mugunta ne ake yi"
Dije ta miƙe tsaye sai ga zobenta da Lawi ya bata ya faɗo ƙasa don ana karatun ta cire shi tana wasa da shi, bayan wucewarsu ne ya miƙe da nufin barin wajen sai ga shi ya hango Zoben, cikin ko in kula ya duƙa ya ɗauki Zoben ya saka aljihunshi ya nufi ɗakinshi, zuciyarshi cike da tunanin ina ta samo zobe mai kyau haka? Wata zuciyar tace da shi maybe Hajiya Mama ce ta bata shi, sai kuma cen ya tuno da zasu zo garin ya hango Zoben a hannunta, to wa ya bata? Haka ya yi ta yiwa kanshi tambayar da babu mai amsa masa, amman ya ci alwashin sai ya tambayeta ya ji ina ta samo zoben don yasan da sanin cewa kaf garinsu babu mai wayewar da zai iya bata kyautar Zoben.
Haka kawai ya ji zuciyarshi ta kasa natsuwa don wata zuciyar tana sanar da shi cewa ƙila Lawi ne ya bata shi, haka ya kwana cike da takaicin da shi kanshi baisan mafarinshi ba.
Shiyasa ko da safiya ma ta waye ƙin fitowa ya yi ayi break da shi kamar yanda aka saba kullum, sau biyu ana turo kiranshi yana faɗin zai zo amman yaƙi fitowa, dole Hajiya Mama bayan sun ƙare ta ce da Dije ta ɗauki nashi ta je ta kai masa,amman idan ta ga zai daketa ta dawo abunta kar ta zure ya yi mata dukan banza.
Aiko cike da Sa'a tana ƙwanƙwasa ɗakin ya ce a shigo, ta tura ƙofar ta shiga tana ƙoƙarin ajiye wa ne ya galla mata harara ta ja baya kaɗan cikin tsoro ta ajiye zata fita ya yi saurin fisgota da ƙarfi sai gata ko ta faɗo jikinshi saboda kasancewarta lange lange ba wani kumarin kirki, cikin masifa ya yi saurin tureta ta faɗi ƙasa sai ga ta da saurin faɗin
"Wayyo hannuna"
Ya wurga mata harara sannan ya fito da zoben yace,. "Uban wa ya baki wannan Zoben???"
Dije ta yi saurin kai kallonta ga zoben ta washe baki ta ce
"Laaa ina ka ganshi?? Tun dazu nike ta nemanshi WALLAHI"
Cike da takaicin rashin amsa masa tambayar da bata yi ba yace,. "Ina kika samo shi ko sata kika fara yi a gidan namu bamu sani ba??"
Dije ta zaro Ido tare da rufe bakinta alamun firgici ta ce,. "Sata????"
Ya ɗaga mata kai ya ce "Eh sata saboda wannan Zoben kaf ƙauyenku babu wanda ya isa ya yi maki kyautarshi"
Dije ta miƙe tsaye cikin fushi ta riƙe ƙugu tace,. "Kam balasi me kake nufi da hakan? Ai billahillazi Ni ba ɓarauniya ba ce ka je ka tambayi Hajiyar taka idan na taɓa ɗaukar maku wani abu ka ji, kuma WALLAHI idan har ta rufeni kace da ita ban yafe ba......."
Karaf ta ji saukar mari akan fuskarta ta yi saurin dafe kumatu cike da mamaki tace,. "Laaa! Laaa! Laaa! Ni ka mara? Me na yi maka da zaka mareni?"
Safwan yana wani muzurai ya taso mata a harzuƙe yace,. "An mareki ke ɗin ɗiyar waye da ba za'a mareki ba WALLAHI idan baki faɗa man inda kika samo zoben nan ba dukan tsiya ne zan yi maki, ƙaramar mara kunya ko an faɗa maki ke wata tsiya ce da har za'a ji shayin sakin ƙwanji a jibgi abun banza?, Kwaɗayayyun banza kawai don masifa irinta baƙin ƙauyen naku ace wai mijin da zai aureki a siyeshi da kuɗi don bala'i kuma ya amince, to ki sani ni ba wai don ina sonki na auroki ba kar ki zargi hakan ki zo wa mutane da renin hankali, zaki faɗa ko ba zaki faɗa ba sai na kakkaryaki a gun yanzun nan?"
Dije ta kawo iya wuya saboda baƙaƙen maganganun da yake ta jifarta da su, cikin fushi ta nunashi da yatsa tace
"Ka daina gangancin sukar garinmu don Ni ma ba sonka nake yi ba tun farko da Malam Lawi ka nemo ya aureni da nafi farin ciki sau dubu da wannan cin zarafin da kake yi mani a cikin gidanku, Zobe kuma mai sona tsakani da ALLAH ya bani wanda nake hango da ace shine tsaye a gabana yanzu ba zai taɓa yi man gori ba, kai ma ɗin ka je kai da ALLAH don ba yafe maka ƙazafin satar da ka yi man na yi ba"
Tana ƙare maganar ta zo zata fita saboda kukan da ya zo mata, Safwan ya riƙo hannunta da sauri ya dawo da ita gabanshi ido cikin ido suke kallon juna ya zare mata idanuwa tare faɗar
"Uban wa ya baki Zoben na ce ko ba zaki faɗa ba??"
Dije ta fisge hannunta cikin fushi da hayagaga tace,. "Masoyi na na gaskiya Abokinka Malam Lawi shine ya bani, idan kuma kana tamtama ka je ka tambayeshi ka ji kuma WALLAHI idan har baka bani abuna ba akan shi zaka janyo in in yi maka abunda kaf garin nan sai an tsine mani"
Tana ƙare maganar ta fice tana wani irin kuka gwanin ban tausayi, saboda ba ƙaramin zafi ta ji ba akan ƙazafin satar da ya yi mata, uwa uba da cin zarafin mutanen ƙauyensu da ya yi.
Safwan kam ba shiri ya dafe kai saboda abunda ya ji ta faɗa akan Zoben da wanda ya bata shi ya sa ya ji duniyar tana juyawa da shi, ya yi shiru na ɗan lokaci sannan ya furzar da iska a bakinshi yace
"Lawi hmmmmm!"
Yana cikin nazarin abun yi ne sai ga Hajiya Mama ta zo tana rufeshi da faɗa kamar zata dakeshi ba tare da ma ta jira taji ba'asin maganar daga Bakinshi ba, ta ce ya bata Zoben dole ba yanda ya iya ya fiddoshi aljihu ya miƙa mata, sai dai kam damuwar da yake ciki ta janyo ƙanzil ya kasa cewa bale har ya yi yunƙurin kare kanshi, har ta yi faɗanta ta gama ta fita bai ce da ita komi ba, cikin tsananin fushi yace
"Dole ma ne in tattara inawa inawa in bar mata gidan don WALLAHI ba zan zauna takaicin Black Cat ya janyo in mussure ba, ina ba zai yiwu ba WALLAHI zan bar maki ita Hajiya tunda kinfi sonta da ni"
A gurguje ya shirya ya fice gidan yanata cuku cukun barin garin zuwa makarantar da yake son yin applying zuwa U.S sai ko ga shi cikin nasara ya harhaɗa komi da ya dace sati biyu a tsakani ya ɗage ya bar ƙasar gaba ɗaya.
*Lamba ta 32*
Dije kam kwana biyu da zuwanta Yola Hajiya Mama ta sa Safwan ya fara yi mata lesson, saboda a cewarta don ta sami ƙarfin gwiwar tunkarar makarantar da za'a sakata da kyau, aiko sai ga shi duk da kyarar da yake yi mata hakan bai hanata fahimtar karatun da yake koya mata ba, don wannan karon ma ta ci Sa'a da Hausa ya ke fahimtar da ita duk wani abund bata gane ba, don wani zubin ma Hajiya Mama a gabanta ake karatun saboda cin zalin Dije da yake yi, duk da aranta wani lokaci sai ta ƙudurta ramawa sau kuma ta tuno huɗubar da Baffah'nta ya yi mata sai ta fasa, sai dai ta yi ta binshi da harara tana cizon yatsa saboda kullum cikin dare sai ta yi kukan rashin ganinsu.
Sai dai ta samu Surry da Hajiya Mama suna ina ka aza da ita komi take buƙata ko da bata faɗa ba yi mata ake yi, abinci ma kala kala ake baje mata ta ci wanda take so, Fiddo kam yanzu tsakaninta da Dije sai harara da murguɗar baki saboda faɗan da Hajiya Mama ta yi mata sosai akan Dijen, tare da gargaɗi mai tsanani akan duk ta sake yi wa Dije gori ko ta ci zarafinta sai ta saɓa mata.
A yau ma sati ɗaya da zuwan Dije gidan Garin suna babban falon gidan ne suna karatun kamar kullum, Safwan yana koya mata karatun tana gyangyaɗin Bacci don daman cen Dije ba gwanar firar dare ba ce, jin haushin baccin da take so ta yi bayan Hajiyar ta hana shi fita zuwa inda ya so ya je yasa ya fakaici idon Hajiya Mamar, ya janyo mata dogon tsoronta da ya fito cikin hular da ke saman kanta, cikin ƙeta ya janyo tsoron da ƙarfi ba shiri Dije ta ƙwallah ƙara tare da dunƙulewa tana kuka mai cike da takaicin hanata baccin da yake yi da muguntarshi kala kala.
Hajiya Mama ta yi saurin faɗin,. "Ka kiyayeni Sawan me ta yi maka yanzu kuma?"
Safwan ya sosa kanshi cikin sauri yace,. "Bacci fa take yi Hajiya Mama don ta renani ga shi ƙiri ƙiri ta sa an hanani fita kuma ta zo tana yi wa mutane baccin renin wayo"
Hajiya Mama ta tashi cikin sauri ta riƙo hannunta tace,. "Tashi mu je ki yi baccinki tunda karatun na mugunta ne ake yi"
Dije ta miƙe tsaye sai ga zobenta da Lawi ya bata ya faɗo ƙasa don ana karatun ta cire shi tana wasa da shi, bayan wucewarsu ne ya miƙe da nufin barin wajen sai ga shi ya hango Zoben, cikin ko in kula ya duƙa ya ɗauki Zoben ya saka aljihunshi ya nufi ɗakinshi, zuciyarshi cike da tunanin ina ta samo zobe mai kyau haka? Wata zuciyar tace da shi maybe Hajiya Mama ce ta bata shi, sai kuma cen ya tuno da zasu zo garin ya hango Zoben a hannunta, to wa ya bata? Haka ya yi ta yiwa kanshi tambayar da babu mai amsa masa, amman ya ci alwashin sai ya tambayeta ya ji ina ta samo zoben don yasan da sanin cewa kaf garinsu babu mai wayewar da zai iya bata kyautar Zoben.
Haka kawai ya ji zuciyarshi ta kasa natsuwa don wata zuciyar tana sanar da shi cewa ƙila Lawi ne ya bata shi, haka ya kwana cike da takaicin da shi kanshi baisan mafarinshi ba.
Shiyasa ko da safiya ma ta waye ƙin fitowa ya yi ayi break da shi kamar yanda aka saba kullum, sau biyu ana turo kiranshi yana faɗin zai zo amman yaƙi fitowa, dole Hajiya Mama bayan sun ƙare ta ce da Dije ta ɗauki nashi ta je ta kai masa,amman idan ta ga zai daketa ta dawo abunta kar ta zure ya yi mata dukan banza.
Aiko cike da Sa'a tana ƙwanƙwasa ɗakin ya ce a shigo, ta tura ƙofar ta shiga tana ƙoƙarin ajiye wa ne ya galla mata harara ta ja baya kaɗan cikin tsoro ta ajiye zata fita ya yi saurin fisgota da ƙarfi sai gata ko ta faɗo jikinshi saboda kasancewarta lange lange ba wani kumarin kirki, cikin masifa ya yi saurin tureta ta faɗi ƙasa sai ga ta da saurin faɗin
"Wayyo hannuna"
Ya wurga mata harara sannan ya fito da zoben yace,. "Uban wa ya baki wannan Zoben???"
Dije ta yi saurin kai kallonta ga zoben ta washe baki ta ce
"Laaa ina ka ganshi?? Tun dazu nike ta nemanshi WALLAHI"
Cike da takaicin rashin amsa masa tambayar da bata yi ba yace,. "Ina kika samo shi ko sata kika fara yi a gidan namu bamu sani ba??"
Dije ta zaro Ido tare da rufe bakinta alamun firgici ta ce,. "Sata????"
Ya ɗaga mata kai ya ce "Eh sata saboda wannan Zoben kaf ƙauyenku babu wanda ya isa ya yi maki kyautarshi"
Dije ta miƙe tsaye cikin fushi ta riƙe ƙugu tace,. "Kam balasi me kake nufi da hakan? Ai billahillazi Ni ba ɓarauniya ba ce ka je ka tambayi Hajiyar taka idan na taɓa ɗaukar maku wani abu ka ji, kuma WALLAHI idan har ta rufeni kace da ita ban yafe ba......."
Karaf ta ji saukar mari akan fuskarta ta yi saurin dafe kumatu cike da mamaki tace,. "Laaa! Laaa! Laaa! Ni ka mara? Me na yi maka da zaka mareni?"
Safwan yana wani muzurai ya taso mata a harzuƙe yace,. "An mareki ke ɗin ɗiyar waye da ba za'a mareki ba WALLAHI idan baki faɗa man inda kika samo zoben nan ba dukan tsiya ne zan yi maki, ƙaramar mara kunya ko an faɗa maki ke wata tsiya ce da har za'a ji shayin sakin ƙwanji a jibgi abun banza?, Kwaɗayayyun banza kawai don masifa irinta baƙin ƙauyen naku ace wai mijin da zai aureki a siyeshi da kuɗi don bala'i kuma ya amince, to ki sani ni ba wai don ina sonki na auroki ba kar ki zargi hakan ki zo wa mutane da renin hankali, zaki faɗa ko ba zaki faɗa ba sai na kakkaryaki a gun yanzun nan?"
Dije ta kawo iya wuya saboda baƙaƙen maganganun da yake ta jifarta da su, cikin fushi ta nunashi da yatsa tace
"Ka daina gangancin sukar garinmu don Ni ma ba sonka nake yi ba tun farko da Malam Lawi ka nemo ya aureni da nafi farin ciki sau dubu da wannan cin zarafin da kake yi mani a cikin gidanku, Zobe kuma mai sona tsakani da ALLAH ya bani wanda nake hango da ace shine tsaye a gabana yanzu ba zai taɓa yi man gori ba, kai ma ɗin ka je kai da ALLAH don ba yafe maka ƙazafin satar da ka yi man na yi ba"
Tana ƙare maganar ta zo zata fita saboda kukan da ya zo mata, Safwan ya riƙo hannunta da sauri ya dawo da ita gabanshi ido cikin ido suke kallon juna ya zare mata idanuwa tare faɗar
"Uban wa ya baki Zoben na ce ko ba zaki faɗa ba??"
Dije ta fisge hannunta cikin fushi da hayagaga tace,. "Masoyi na na gaskiya Abokinka Malam Lawi shine ya bani, idan kuma kana tamtama ka je ka tambayeshi ka ji kuma WALLAHI idan har baka bani abuna ba akan shi zaka janyo in in yi maka abunda kaf garin nan sai an tsine mani"
Tana ƙare maganar ta fice tana wani irin kuka gwanin ban tausayi, saboda ba ƙaramin zafi ta ji ba akan ƙazafin satar da ya yi mata, uwa uba da cin zarafin mutanen ƙauyensu da ya yi.
Safwan kam ba shiri ya dafe kai saboda abunda ya ji ta faɗa akan Zoben da wanda ya bata shi ya sa ya ji duniyar tana juyawa da shi, ya yi shiru na ɗan lokaci sannan ya furzar da iska a bakinshi yace
"Lawi hmmmmm!"
Yana cikin nazarin abun yi ne sai ga Hajiya Mama ta zo tana rufeshi da faɗa kamar zata dakeshi ba tare da ma ta jira taji ba'asin maganar daga Bakinshi ba, ta ce ya bata Zoben dole ba yanda ya iya ya fiddoshi aljihu ya miƙa mata, sai dai kam damuwar da yake ciki ta janyo ƙanzil ya kasa cewa bale har ya yi yunƙurin kare kanshi, har ta yi faɗanta ta gama ta fita bai ce da ita komi ba, cikin tsananin fushi yace
"Dole ma ne in tattara inawa inawa in bar mata gidan don WALLAHI ba zan zauna takaicin Black Cat ya janyo in mussure ba, ina ba zai yiwu ba WALLAHI zan bar maki ita Hajiya tunda kinfi sonta da ni"
A gurguje ya shirya ya fice gidan yanata cuku cukun barin garin zuwa makarantar da yake son yin applying zuwa U.S sai ko ga shi cikin nasara ya harhaɗa komi da ya dace sati biyu a tsakani ya ɗage ya bar ƙasar gaba ɗaya.