Sashe 20
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Safwan yana shirin sake yi mata magana ne ya hango Lawi zai shigo Makarantar ya yi saurin fad'in,. "Oya go to your class"
Dije ta tafi tana ta k'umshe dariyarta saboda gargadin da yayi mata ya bata dariya, don ganin renin wayon nashi ma ya yi yawa ashe ma ya iya hausa amman kullum yake ta zuba masu zallar turanci, sannan zagin da tasha yi mashi da Hausa ita da su Lanti ashe duk yana ji amman yake yi kamar bai san me suke fad'a ba, sai dai laifi kad'an zai sa ya yi ta harararsu yana muzurai, k'arshe ma haka zai k'are karatun ba tare da sun fahimci komi ba.
Lawi kam tun daga nesa da ya hango Dije yake ta sauri sai gashi kafin ya k'araso har ta wuce, cikin damuwa ya isa wurin Safwan ya zauna ya na bin class d'in su Dijen da kallo, Safwan ya yi masa wani kallo ya yi wani mere yace
"To yarinyar nan dai ka d'aga mata k'afa don yanzu ta ke sanar dani Mahaifinta ya hanata zuwa Makaranta ne saboda kai, idan har da gaske kana sonta to ka barta ta yi karatunta, don an gargad'eta a gida duk ranar da aka sake ganinta da kai za'a cireta daga school d'in gaba d'aya"
Lawi ya yi saurin fad'in
"Innalilahi wa'Inna ilairraji'un kai wannan bala'i da me yayi Kama?? WALLAHI kwana biyun nan da ban ganta ba jinsu nayi tamkar shekara biyu, Abokina ka taimaki rayuwata WALLAHI mutuwa zanyi idan har ban auri yarinyar nan ba"
Safwan ya yi saurin mik'ewa tare da buga wani uban tsaki ya barshi a nan ya shige Ofishin Malammai, Lawi ya bishi da kallon mamaki sannan ya yu shiru yana nazarin mood d'in abokin nashi akan matsalar, da kullum baya bashi goyon baya akan soyayyarshi da Dijen, asali ma sai Kara dakushe masa karsashi yake yi kullum safiya, a ranshi yace
_"shin wai shi baya da imani ne da har ba zai taimakeni na samu abunda yafi soyuwa agareni ba?, Ko don shi har yanzu bai San zafin son bane?"_.
Ya furzar da iska mai zafi a bakinshi ya mike ya nufi office d'in ranshi a b'ace, saboda damuwowin da suka yi masa yawa ga rashin goyon bayan Safwan akan masoyiyarshi Dije, ga kuma wata bakuwar matsalar da aka kunno masa da ita, don rashin magana da Dije a wurin ba k'aramin purnishmen ne aka bashi ba, yarinyar da har gizo take masa a ido baya da wani mafalki a Yan kwanakin nan sai nata, lokaci d'aya a rabashi da ita irin haka ai an ci da zalinshi.
Ranar har aka tashi ba wata walwala ko wata huld'a mai k'arfi da ta shiga tsakanin Abokan biyu, abun takaicinma lokacin da aka tashin k'iri K'iri Dije ta ki tsayawa ta ji uzurin Lawi da ke son yin magana da ita, saboda tsoron a ganta aje a fad'awa Baffanta Safwan kam ba k'aramin dad'i hakan ya yi masa ba, ya sake girmama lamarinta saboda ganin ashe rashin kunyarta da sauk'i tunda har tana jin maganar iyayenta.
Lawi kam ko dakinsu bai nufa ba ya isa wurin Maigarin cikin damuwar da ta kasa boyuwa akan fuskarshi, Maigarin ya kalleshi cikin tausayawa don yasan labarin gizo baya wuce na koki, amman duk da hakan sai da ya wayance yace dashi
"Yarona lafiya Na ganka haka? ko wani abun ne ya faru cen Gida? "
Lawi ya kara sunne kai yace,. "A'a Baba akan dai matsalar nan ne"
Maigarin ya ce,. "Wace matsala Kuma? Ko ta Yar Gidan Malam Sanda?"
Lawi ya d'aga kanshi yace,. "Eh ita to yanzu abun ya Kara rikicewa saboda ko magana ma an hanata tsayawa ta yi dani"
Maigarin ya yi shiru sannan yace,. "Ka yi hak'uri yarona Ni zan ga Malam Sanda duk yanda muka yi zan neme ka"
Lawi ya mike tare da yi masa godiya ya yi d'akinsu, zuciyarshi cike da takaicin bala'in da ya janyowa kanshi yana zaman zamanshi.
Maigarin kam bai yi k'asa a gwiwa ba dakanshi bayan magrib ya yi tattaki tare da mukarrabanshi suka nufi gidansu Dije, cike da mamaki Baffah'n ya shimfida masu tabarma suka zauna tare da yi masu sannu da zuwa.
Bayan an k'are gaggaisawa ne Maigarin ya yi gyaran murya yace,. "Malam Sanda nasan zaka yi mamakin abunda yasa na yo tattaki zuwa wajenka?, To ba komi ba ne akan matsalar Bakon yaron cen ne da Yar wajenka Dije, a zahirin gaskiya yaron nan dai na gano ba k'aramin so yake yi mata ba, shiyasa nace bari in zo in jaddada maka zancenshi da muka yi a kwanakin baya, shin har yanzu kana kan bakanka akan bazaka baiwa mutumen nesa yarka ba Koko ya abun yake?"
Baffah kam Nan take wani sabon b'acin Rai ya ziyartoshi amman cikin dariyar yake yace,. "Ranka shi dad'e ina mai jin kunyar sanar da Kai cewa na yiwa Dije Miji, kuma insha ALLAHu wata mai kamawa Zan auradda Dije ga Bala dan Gidan Mariganyi Mamman jikan Inna Duduwa"
To fa rigiji Gabji😳 lalle akwai kwacagiya😝
Akafta🤣
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*MUTANEN DIJE K'ARANGIYA INA GAIDA KOWA ALL ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MAKU HAR GADON BACCINKU👍🏻*
*Lamba ta 21*
Gaba d'aya jikin kowa na wurin ya yi sanyi sai cen Maigarin ya yi jarumtar fad'in,. "A komi ALLAH Ubangiji yasa hakan shine alkhairin"
Ya yunkura ya mike tsaye yana saka talkaminshi yace da abokan tafiyarshi,. "Ki tashi muje sai mu yi masa bayani idan har ALLAH zai sa ya fahimcemu"
Haka suka bar k'ofar gidan kowa jiki ba kuzari saboda ganin duk girman Maigarin ya zo neman abu wajen Baffah amman ya rufe idonshi ya kasa yi masa wannan alfarma, shi Kam Baffah ko a jikinshi hasali ma hankalinshi kwance ya nad'e tabamar ya shige cikin gida, inda kai tsaye ya kira Usman ya ce ya je ya kira masa Balan Duduwar, sannan ya shige d'aki abunshi Inna ta bishi da kallon mamaki jin aiken da ya yi na neman Bala, cikin sanyin jiki ta bishi d'akin tace
"Malam ALLAH dai yasa lafiya?? Naga Maigari ya zo wajenka kuma ga shi na ji yanzu ka ce a kira Bala"
Baffah ya yi saurin fadada fuskarshi da murmushin yace,. "Abunda kike so ne za'a yi maki tunda na hango hakan shine mafita akan matsalolin da suke son kunno man kai cikin gida"
Inna ta bishi da kallo Baki sake tace,. "Ka yi man bayani yanda Zan gane Malam"
Baffah ya fito d'akin tare da d'auko buta ya fara sabuwar arwallah har ya k'are ba tare da yace kanzil ba, sannan ya mike ya kalleta yace
"Wata mai kamawa Zan yiwa Dije aure da Balan Duduwa tunda har yana sonta"
Inna ta zaro ido waje tace,. "A'a Malam gaggawa fa aikin shedan ce, ka bari abi komi a hankali kar a zo ayi abu don neman mafita wata sabuwar matsalar ta bullo"
Baffah ya kalli Inna shekeke sannan ya nufi hanyar fita yace,. "Alkhairi muke fata kuma shi zamu gani"
Ya fice ranshi a b'ace Dije da ke k'ofar Inna ta k'araso wajen da Innar take tsaye cikin kokwanto tace,. "INNA naji Baffah yana zancen aurena da Balan Duduwa da gaske yake yi ko wasa???"
Inna ta maka mata wata Uwar harara ta nufi madafi tace,. "Ki jira idan har ya dawo sai ya amsa maki tambayar da bakinshi tunda ai ba Ni kika ji na fad'a ba"
Dije ta ja buta ta yi bayi tana gungunin cewa,. "Ai na rantse da ALLAH ni Malam Danbirni zan aura cabd'i! Haka kawai in aureshi ya hanani zuwa Makarantar koyon Likitanci hum! lalle ma ko"
**
Baffah Kam tare da Bala da Usman suka yi sallahr Isha sannan suka garzayo gida, Baffah yasa Usman ya shimfida masu tabarma a zauren gidan, sannan yasa aka kawo masa tuwonshi ya yi wa Bala tayi Bala cike da jin nauyin surukuta yace,. "Alhmdllh"
Baffah ya kalli Balan yace,. "Naji labarin cewa kana son Dije ko?"
Bala ya sunne kai cike da jin kunyarshi, Baffah ya ce
"Magana zamu yi mai Muhimmanci saboda auradda ita nike son yi idan har kashirya aurenta to ka fito da karfinka Ni zan aura maka Dije duk lokacin da ka shirya"
Cike da tsananin farin ciki yace
"Na gode Baffah" Balan kam bakinshi ya kasa rufuwa saboda tsabar murnar ganin nesa ta zo masa kusa, cikin jin nauyi ya nunawa Baffah amincewarshi tare da godiya akan wannan karamci da ya yi masa, sannan ya yi masa alk'awalin zai turo iyayenshi kurkusa ayi komi a gama cikin kankanin lokaci.
Haka suka rabu zuciyarshi cike da farin ciki uwa uba ma da Baffah'n ya bashi damar ya fara zuwa zance wajen Dijen don su fahimci juna kafin lokacin auren ya zo.
Baffah kam bai shigo Gida ba har sai da ya tabbatar Dije ta yi bacci don ba ya son ta janyo abunda zai sa ya jibgeta a banza, don tunda ya dawo masallacin ya ga yanda ta makure jikin gini tana sharar hawaye yasan akwai magana, don baya raba d'aya biyu yasan taji zancen aurenta Balan shiyasa, sai dai a mamakinshi ko da ya shiga cikin Gidan ya taradda ita idonta biyu jikin ginin har lokacin tana gyangyadi, jin shigowarshi yasa ta yi saurin mik'ewa ta nufoshi tana fad'in
"WALLAHI Ni Baffah ban son Bala ba zan aureshi ba"
Baffahn ya yi mata wani kallo yace,. "Baki sonshi wa kike so??"
Dije ta yi saurin kamo gefen dankwalinta tana wasa dashi tace,. "Ni Baffah ba wanda nike so WALLAHI Ni gurina kawai inje Makarantar gaba in zama likita"
Baffah ya zaro Ido waje yace,. "Au shirmen ya kitsa maki kenan ko? To ai kwanan nan zanyi maganin abun, ai WALLAHI ko bani so dole ne in auradda ke cikin gaggawa tun kafin su kaini ga maganar banza"
Yana kare maganar ya shige d'akinshi zuciyarshi cike da jin tsoron sharrin wad'annan bak'in Yan bokon ga Yar guda gudar yarshi Dije, wadda ko kuda baya so ya tab'a masa ita matuk'ar yana da ikon hakan.
Dije ta tafi tana ta k'umshe dariyarta saboda gargadin da yayi mata ya bata dariya, don ganin renin wayon nashi ma ya yi yawa ashe ma ya iya hausa amman kullum yake ta zuba masu zallar turanci, sannan zagin da tasha yi mashi da Hausa ita da su Lanti ashe duk yana ji amman yake yi kamar bai san me suke fad'a ba, sai dai laifi kad'an zai sa ya yi ta harararsu yana muzurai, k'arshe ma haka zai k'are karatun ba tare da sun fahimci komi ba.
Lawi kam tun daga nesa da ya hango Dije yake ta sauri sai gashi kafin ya k'araso har ta wuce, cikin damuwa ya isa wurin Safwan ya zauna ya na bin class d'in su Dijen da kallo, Safwan ya yi masa wani kallo ya yi wani mere yace
"To yarinyar nan dai ka d'aga mata k'afa don yanzu ta ke sanar dani Mahaifinta ya hanata zuwa Makaranta ne saboda kai, idan har da gaske kana sonta to ka barta ta yi karatunta, don an gargad'eta a gida duk ranar da aka sake ganinta da kai za'a cireta daga school d'in gaba d'aya"
Lawi ya yi saurin fad'in
"Innalilahi wa'Inna ilairraji'un kai wannan bala'i da me yayi Kama?? WALLAHI kwana biyun nan da ban ganta ba jinsu nayi tamkar shekara biyu, Abokina ka taimaki rayuwata WALLAHI mutuwa zanyi idan har ban auri yarinyar nan ba"
Safwan ya yi saurin mik'ewa tare da buga wani uban tsaki ya barshi a nan ya shige Ofishin Malammai, Lawi ya bishi da kallon mamaki sannan ya yu shiru yana nazarin mood d'in abokin nashi akan matsalar, da kullum baya bashi goyon baya akan soyayyarshi da Dijen, asali ma sai Kara dakushe masa karsashi yake yi kullum safiya, a ranshi yace
_"shin wai shi baya da imani ne da har ba zai taimakeni na samu abunda yafi soyuwa agareni ba?, Ko don shi har yanzu bai San zafin son bane?"_.
Ya furzar da iska mai zafi a bakinshi ya mike ya nufi office d'in ranshi a b'ace, saboda damuwowin da suka yi masa yawa ga rashin goyon bayan Safwan akan masoyiyarshi Dije, ga kuma wata bakuwar matsalar da aka kunno masa da ita, don rashin magana da Dije a wurin ba k'aramin purnishmen ne aka bashi ba, yarinyar da har gizo take masa a ido baya da wani mafalki a Yan kwanakin nan sai nata, lokaci d'aya a rabashi da ita irin haka ai an ci da zalinshi.
Ranar har aka tashi ba wata walwala ko wata huld'a mai k'arfi da ta shiga tsakanin Abokan biyu, abun takaicinma lokacin da aka tashin k'iri K'iri Dije ta ki tsayawa ta ji uzurin Lawi da ke son yin magana da ita, saboda tsoron a ganta aje a fad'awa Baffanta Safwan kam ba k'aramin dad'i hakan ya yi masa ba, ya sake girmama lamarinta saboda ganin ashe rashin kunyarta da sauk'i tunda har tana jin maganar iyayenta.
Lawi kam ko dakinsu bai nufa ba ya isa wurin Maigarin cikin damuwar da ta kasa boyuwa akan fuskarshi, Maigarin ya kalleshi cikin tausayawa don yasan labarin gizo baya wuce na koki, amman duk da hakan sai da ya wayance yace dashi
"Yarona lafiya Na ganka haka? ko wani abun ne ya faru cen Gida? "
Lawi ya kara sunne kai yace,. "A'a Baba akan dai matsalar nan ne"
Maigarin ya ce,. "Wace matsala Kuma? Ko ta Yar Gidan Malam Sanda?"
Lawi ya d'aga kanshi yace,. "Eh ita to yanzu abun ya Kara rikicewa saboda ko magana ma an hanata tsayawa ta yi dani"
Maigarin ya yi shiru sannan yace,. "Ka yi hak'uri yarona Ni zan ga Malam Sanda duk yanda muka yi zan neme ka"
Lawi ya mike tare da yi masa godiya ya yi d'akinsu, zuciyarshi cike da takaicin bala'in da ya janyowa kanshi yana zaman zamanshi.
Maigarin kam bai yi k'asa a gwiwa ba dakanshi bayan magrib ya yi tattaki tare da mukarrabanshi suka nufi gidansu Dije, cike da mamaki Baffah'n ya shimfida masu tabarma suka zauna tare da yi masu sannu da zuwa.
Bayan an k'are gaggaisawa ne Maigarin ya yi gyaran murya yace,. "Malam Sanda nasan zaka yi mamakin abunda yasa na yo tattaki zuwa wajenka?, To ba komi ba ne akan matsalar Bakon yaron cen ne da Yar wajenka Dije, a zahirin gaskiya yaron nan dai na gano ba k'aramin so yake yi mata ba, shiyasa nace bari in zo in jaddada maka zancenshi da muka yi a kwanakin baya, shin har yanzu kana kan bakanka akan bazaka baiwa mutumen nesa yarka ba Koko ya abun yake?"
Baffah kam Nan take wani sabon b'acin Rai ya ziyartoshi amman cikin dariyar yake yace,. "Ranka shi dad'e ina mai jin kunyar sanar da Kai cewa na yiwa Dije Miji, kuma insha ALLAHu wata mai kamawa Zan auradda Dije ga Bala dan Gidan Mariganyi Mamman jikan Inna Duduwa"
To fa rigiji Gabji😳 lalle akwai kwacagiya😝
Akafta🤣
D/AUTA CE✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*MUTANEN DIJE K'ARANGIYA INA GAIDA KOWA ALL ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MAKU HAR GADON BACCINKU👍🏻*
*Lamba ta 21*
Gaba d'aya jikin kowa na wurin ya yi sanyi sai cen Maigarin ya yi jarumtar fad'in,. "A komi ALLAH Ubangiji yasa hakan shine alkhairin"
Ya yunkura ya mike tsaye yana saka talkaminshi yace da abokan tafiyarshi,. "Ki tashi muje sai mu yi masa bayani idan har ALLAH zai sa ya fahimcemu"
Haka suka bar k'ofar gidan kowa jiki ba kuzari saboda ganin duk girman Maigarin ya zo neman abu wajen Baffah amman ya rufe idonshi ya kasa yi masa wannan alfarma, shi Kam Baffah ko a jikinshi hasali ma hankalinshi kwance ya nad'e tabamar ya shige cikin gida, inda kai tsaye ya kira Usman ya ce ya je ya kira masa Balan Duduwar, sannan ya shige d'aki abunshi Inna ta bishi da kallon mamaki jin aiken da ya yi na neman Bala, cikin sanyin jiki ta bishi d'akin tace
"Malam ALLAH dai yasa lafiya?? Naga Maigari ya zo wajenka kuma ga shi na ji yanzu ka ce a kira Bala"
Baffah ya yi saurin fadada fuskarshi da murmushin yace,. "Abunda kike so ne za'a yi maki tunda na hango hakan shine mafita akan matsalolin da suke son kunno man kai cikin gida"
Inna ta bishi da kallo Baki sake tace,. "Ka yi man bayani yanda Zan gane Malam"
Baffah ya fito d'akin tare da d'auko buta ya fara sabuwar arwallah har ya k'are ba tare da yace kanzil ba, sannan ya mike ya kalleta yace
"Wata mai kamawa Zan yiwa Dije aure da Balan Duduwa tunda har yana sonta"
Inna ta zaro ido waje tace,. "A'a Malam gaggawa fa aikin shedan ce, ka bari abi komi a hankali kar a zo ayi abu don neman mafita wata sabuwar matsalar ta bullo"
Baffah ya kalli Inna shekeke sannan ya nufi hanyar fita yace,. "Alkhairi muke fata kuma shi zamu gani"
Ya fice ranshi a b'ace Dije da ke k'ofar Inna ta k'araso wajen da Innar take tsaye cikin kokwanto tace,. "INNA naji Baffah yana zancen aurena da Balan Duduwa da gaske yake yi ko wasa???"
Inna ta maka mata wata Uwar harara ta nufi madafi tace,. "Ki jira idan har ya dawo sai ya amsa maki tambayar da bakinshi tunda ai ba Ni kika ji na fad'a ba"
Dije ta ja buta ta yi bayi tana gungunin cewa,. "Ai na rantse da ALLAH ni Malam Danbirni zan aura cabd'i! Haka kawai in aureshi ya hanani zuwa Makarantar koyon Likitanci hum! lalle ma ko"
**
Baffah Kam tare da Bala da Usman suka yi sallahr Isha sannan suka garzayo gida, Baffah yasa Usman ya shimfida masu tabarma a zauren gidan, sannan yasa aka kawo masa tuwonshi ya yi wa Bala tayi Bala cike da jin nauyin surukuta yace,. "Alhmdllh"
Baffah ya kalli Balan yace,. "Naji labarin cewa kana son Dije ko?"
Bala ya sunne kai cike da jin kunyarshi, Baffah ya ce
"Magana zamu yi mai Muhimmanci saboda auradda ita nike son yi idan har kashirya aurenta to ka fito da karfinka Ni zan aura maka Dije duk lokacin da ka shirya"
Cike da tsananin farin ciki yace
"Na gode Baffah" Balan kam bakinshi ya kasa rufuwa saboda tsabar murnar ganin nesa ta zo masa kusa, cikin jin nauyi ya nunawa Baffah amincewarshi tare da godiya akan wannan karamci da ya yi masa, sannan ya yi masa alk'awalin zai turo iyayenshi kurkusa ayi komi a gama cikin kankanin lokaci.
Haka suka rabu zuciyarshi cike da farin ciki uwa uba ma da Baffah'n ya bashi damar ya fara zuwa zance wajen Dijen don su fahimci juna kafin lokacin auren ya zo.
Baffah kam bai shigo Gida ba har sai da ya tabbatar Dije ta yi bacci don ba ya son ta janyo abunda zai sa ya jibgeta a banza, don tunda ya dawo masallacin ya ga yanda ta makure jikin gini tana sharar hawaye yasan akwai magana, don baya raba d'aya biyu yasan taji zancen aurenta Balan shiyasa, sai dai a mamakinshi ko da ya shiga cikin Gidan ya taradda ita idonta biyu jikin ginin har lokacin tana gyangyadi, jin shigowarshi yasa ta yi saurin mik'ewa ta nufoshi tana fad'in
"WALLAHI Ni Baffah ban son Bala ba zan aureshi ba"
Baffahn ya yi mata wani kallo yace,. "Baki sonshi wa kike so??"
Dije ta yi saurin kamo gefen dankwalinta tana wasa dashi tace,. "Ni Baffah ba wanda nike so WALLAHI Ni gurina kawai inje Makarantar gaba in zama likita"
Baffah ya zaro Ido waje yace,. "Au shirmen ya kitsa maki kenan ko? To ai kwanan nan zanyi maganin abun, ai WALLAHI ko bani so dole ne in auradda ke cikin gaggawa tun kafin su kaini ga maganar banza"
Yana kare maganar ya shige d'akinshi zuciyarshi cike da jin tsoron sharrin wad'annan bak'in Yan bokon ga Yar guda gudar yarshi Dije, wadda ko kuda baya so ya tab'a masa ita matuk'ar yana da ikon hakan.