Sashe 61
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"WALLAHI ina sonta Hajiya don ALLAH ki dawo man da matata hannuna, na yi maki alk'awali zan riƙeta in mata gata fiye da kowace mace mai gata a gidan Mijinta"
Ya ƙare maganar cikin muryar kuka tare da zuwa gaban Hajiyar ya durƙusa gwiwa bibbiyu ya haɗa hannu biyu waje ɗaya alamun roƙo ya sake cewa
"Na tuba Hajiyarmu ki yafe mani WALLAHIL'AZIM yanzu da gaske ina sonta, kuma a shirye nike da in zauna da ita a inuwa ɗaya a matsayin matar aurena"
Fiddo ta bi shi cike da kallon mamaki baki a sake tace, "Dijen kake so big Bros??"
Wani hargitsatstsen kallon da ya bi ta da shi da jajayen idanuwanshi yasa ta yi saurin rufe bakinta da hannu ta bar falon, Hajiya Mama ta ƙi kallonshi sai kallon tv'n take yi kamar kallon take yi da gaske, don bata son Kallonshi saboda gudun tausayinshi ya karya mata zuciya, Safwan ya riƙo ƙafarta tare da duƙewa ƙasa cikin wata murya mai cike da ban tausayi ya ce
"Ki gafarceni Hajiyarmu nasan na yi kuskure a baya plss ki dawo man da khadija don ALLAH Hajiyarmu"
Hajiya ta miƙe tsaye ta yi taku ɗaya biyu kamar zata bar falon sannan ta tsaya ta waigo ta ce
"Yanzu ba wurin budurwarka ka fito ba? Kuma ba aurenta ka ke so ka yi ba? To ka je na baka dama tuni ka yi aurenka ai, amman ka sani yanzu na fasa amincewa da tariyar khadija gidanka, zan barta cen wajen aikatau ɗin sai ka rubuta mata takardar sakinta idan ta sami mijinta a cen sai ta yi aurenta"
Tana ƙare faɗar maganar ta wuce abinta ta nufi ɗakinta, cikin sauri ya biyota cike da wani sabon tashin hankali yana faɗin
"Don girman ALLAH Hajiyarmu ki yi haƙuri ki yafe mani laifukana"
Sai dai yana kawowa bakin ƙofar ɗakin ta rufo ƙofar ɗakin da ƙarfi har saura ƙiris ta haɗa da kanshi, Safwan ya dawo baya cikin hanzari sannan ya durƙushe bakin ƙofar yana faɗin
"Zan mutu Hajiya idan har ba'a kawo man matata ba"
Daga cen cikin ɗakin Hajiyar ta ce "ka yi sauri ka mutun don ALLAH, kana da rai ma wani aure zata yi bale ka tafi ka bar duniyar?"
Safwan ya dafe saitin zuciyarshi yace
"Wayyo Hajiyarmu kada ki yi man irin wannan horon wallahil'azim ina sonta ke ma zaki sheda hakan"
Haka ya yi ta surutanshi har ya gaji Hajiyar bata sake tankashi ba, dole ya gaji ya miƙe ya nufi ɗaikinshi ya faɗa gado cikin ƙunar zuciya tare da yin nadama akan abunda ya aikatawa Dijen Baffah a farko, yanzu ga shi Hajiyar tana son horashi da laifin da har ya mance da ya aikata, saboda yanzu giyar sonta da ke walagigi da rayuwarshi yasa ya manta baya, haka ya yi ta kukan zucinshi cikin ɗaki cike baƙin cikin da ya mamaye masa zuciya, saboda Zee sai damunshi da kira take yi wani bayan wani ko gajiya bata yi amman yaƙi ɗaukar ko ɗaya, saboda damuwar da yake ciki a ganinshi ta shi ta shalle tunanin ta ta damuwar.
Haka ya yi ta yiwa Hajiya magiya akan ta dawo masa da Khadijarshi, da ya ga ma ta ƙi saurararsa ne ya kira Fiddo cikin sirri yana tambayarta inda aka kai khadijar, amman itama cike da jin haushinshi ta ce ita bata ma san Dijen bata gidan ba, dole ya koma tambayar ma'aikatan gidan sai dai su ma duka bakinsu ɗaya ne babu wanda yasan inda aka kaita, sai ga Safwan da biyar gidajen ƴan'uwa lungu da saƙo yana binciken ina aka kawo sabuwar ƴar'aiki, amman dai iya bincikenshi babu Dije babu mafarinta, dole ya dawo gida a jigace yana yi wa Hajiya kuka da hawayen da suke ta sauka a kan fuskarshi ba tare da sautin kukan ya fito ba, amman a hakan Hajiyar ta bushe fitilarta ta ce ba zata dawo da ita ba kuma sai ya bata takardar sakin Dijen dolenshi.
Damuwa goma da ashirin suka yi masa yawa a kai saboda izuwa lokacin Mahaifin Zee ma ya shiga cikin jerin sahun masu kiran nashi akan ya turo Iyayenshi, saboda danginsu sun yo masa caa! Akan rashin kyautawar da zai yi wa Aminu, shi
kuma ya kafe akan cewa duk abunda ƴarshi take so shi ma cen yake so, don har meeting aka yi akan matsalar ƙarshe kuma aka watse baram baram, saboda wasu da yawa sun ga laifinshi ya yin da wasu kuma suka goyi bayan Daddyn Zee ɗin saboda illolin auren dolen da ake hangowa, a ƙarshe dai Aminu da kanshi yake baiwa masu goyon bayanshi haƙuri akan lamarin, tare da sare masu gwiwa wajen sanar da su cewa shi fa ya janye, dole kowa ya haƙura aka zubawa Daddyn Zee ido aga iya gudun ruwansu shi da ƴarshi.
Kan haka ne ya yi ta samun Safwan ɗin da kira sai dai zance ɗaya ne yake yi masa na cewa wanda zai zo nema masa auren ya yi tafiya, da ma ya fahimci kamar zillewa yake son yi yasa su ji kunya ga ƴan'uwansu ya ce ya ce da shi
"Ya bashi number'r wakilin nashi shi zai kirashi ya yi masa bayanin abunda ke faruwa"
Dole Safwan ya saka masu ranar da zasu zo shi da Iyayenshi akai ƙarshe akan lamarin, sannan hankalin Daddyn Zee ya kwanta tare da kwantar na ƴarshi da ta ƙi ci ta ƙi sha akan damuwar rashin ɗaukar wayarta da Safwan ɗin baya yi.
Safwan ya je wa da Hajiya Mama da maganar tare da fayyace mata komi akan halin da ake ciki, sai dai duk da ta ji zafin abun aranta amman hakan bai sa ta hanashi auren ba, asali ma ta amince masa kamar farko yanda yasa mutane suka tursasata kan zancen auren, saboda tausayin yanda ya firgice cikin lokaci ɗaya saboda rashin Dijen, ya bi ya rame saboda damuwar da ya sakawa zuciyarshi akan rashin Matarshi, sannan ta san muddin ta hanashi auren bayan ta ɗauke masa Dijen ta cutar da rayuwar ɗanta, sai dai bata amince da auren ba ne sai da ta yi nazarinshi sosai akan damuwar rashin Dijen bazai barshi ya ji daɗin auren da zai yi ba, kuma ta hakan ne zata ƙara samun wata damar da babu wata ƴa mace da zata samu a wurinshi.
Safwan kam cike da tausayin kanshi da ita kan Zee ɗin ya tura Iyayenshi suka neme masa aurenta inda aka saka rana da lokaci sati biyu kacal masu zuwa, saboda su koma school su ci gaba da harƙallar karatunsu.
****
Biki sai ƙaratowa yake yi duk da ango kam ba wani jin daɗin auren ko zumuɗi irin na ango da yake yi, don a kullum dare ya kwanta baya baccin kirki saboda mafalkin Dijen da yake yi cikin yanayi kala kala, ta ɓangaren Zee Kam sai shirye shiryensu suke yi cike da alfahari, saboda su cusawa waɗanda basu son auren haushi, inda su kuma suka koma gefe suna kallon ta yanda za'a yi auren cin amana ya yi daɗi.
*****
Dijen Baffah kam duk da ta ji daɗin garin amman zuciyarta cike take da kewar Mijinta, bata da wani aiki sai na tunaninshi da kalamanshi waɗanda ada take hangosu a matsayin na yaudara, sai ga su a lokacin tana jinsu har cikin ruhinta, saboda ba ƙaramin daɗi suke yi mata a kunnuwa da gangar jikinta ba, waɗanda wani zubin bata san lokacin da wasu hawwyen kuka yake zuwar mata ba, don ita a son samunta a barta ta koma wurin Mijinta ta yi masa biyayyar da Inna take ta yi mata jan kunne akan ta yi masa, yanzu ta amince wa zuciyarta cewa itama fa tana son MALAM Safwan, ga shi ko waya babu a hannunta ba le ta kirashi ta ji daɗi, kuma kunyar idon Auntyn da kashedin Hajiyar yake sa ta ƙi tambayar a wane hali yake.
Ganin halin da take ciki ne yasa Aunty Ummi ta fara shiga damuwa duk da tana iya ƙoƙarinta wajen sakata nishaɗi saboda gurinta na son cire mata damuwa, shiyasa ko auren da ta ji ƙin nuna mata wani abu da zata gano ta yi, saboda jan kunnen da Hajiyar ta yi mata akan kada ta bari ta san da zancen, da ma lokacin auren ya matso ne ta yi mata ƙaryar wani biki ne daban zata je, da ma Dijen ta nuna tana son zuwan itama sai ta ce da ita ta yi haƙuri ba zata daɗe ba, don ma ta kwantar mata da hankali ta bar yaranta mata manya ta tafi da ƙananun saboda Maigidanta daman cen ba mazauni bane ba.
****
Biki bidiri bireɗe amfanin soyayya aure Zee ta angwance da masoyinta Safwan, zuciyarta cike da tsantsar farin ciki saɓaninshi da yake cikin ƙunci don duk wasu events ma ba da shi aka yi ba, an ɗauki Amarya daga Gombe zuwa Yola mahaifar Mijinta, inda aka wuce da ita gidan Hajiya Mama kai tsaye saboda ta kwashi tubarrakin uwar mijinta ta sawa aurensu albarka kafin akaita gidan angonta.
Sorry team Dije 🙇🏻♀️ku sani babu ruwana nidai 🙌🏻🏃🏻♀️
Akafta🙌🏻
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Mutanen Dije ina baku haƙuri🙏🏻dangane da auren Zee da Safwan ya yi, amman ina son ku sani ana yin book ne don faɗakarwa tare da wa'azantarwa sannan da kwatanta abunda ke faruwa a cikin al'ummarmu, saboda haka ku natsu tsaf ku bini sannu a hankali zan warware maku komi cikin tsarinshi😉*
*Lamba ta 58*
Har ƙuryar ɗakin Hajiya Mama aka kai Zee da ke ta rufe fuska tana ta wasar baki saboda daɗin da ya kasa ɓoyuwa a kan fuskarta, gaban kowa da mutanen da suka yi mata rakiya Hajiya Mama ta ce da Zee
"ALLAH ya baku haƙurin zama,
kuma albarkaci aurenku tare da zuri'a ɗayyaba gaba ɗaya, sannan da fatar zaman lafiya ke da abokiyar zamanki"
Dirim! dum! Shine bugun da zuciyar da Zee ta yi amman ta wayance tare da noƙe fuskarta tace "Ameen" Hajiya Mama ta ƙara da cewa
Ya ƙare maganar cikin muryar kuka tare da zuwa gaban Hajiyar ya durƙusa gwiwa bibbiyu ya haɗa hannu biyu waje ɗaya alamun roƙo ya sake cewa
"Na tuba Hajiyarmu ki yafe mani WALLAHIL'AZIM yanzu da gaske ina sonta, kuma a shirye nike da in zauna da ita a inuwa ɗaya a matsayin matar aurena"
Fiddo ta bi shi cike da kallon mamaki baki a sake tace, "Dijen kake so big Bros??"
Wani hargitsatstsen kallon da ya bi ta da shi da jajayen idanuwanshi yasa ta yi saurin rufe bakinta da hannu ta bar falon, Hajiya Mama ta ƙi kallonshi sai kallon tv'n take yi kamar kallon take yi da gaske, don bata son Kallonshi saboda gudun tausayinshi ya karya mata zuciya, Safwan ya riƙo ƙafarta tare da duƙewa ƙasa cikin wata murya mai cike da ban tausayi ya ce
"Ki gafarceni Hajiyarmu nasan na yi kuskure a baya plss ki dawo man da khadija don ALLAH Hajiyarmu"
Hajiya ta miƙe tsaye ta yi taku ɗaya biyu kamar zata bar falon sannan ta tsaya ta waigo ta ce
"Yanzu ba wurin budurwarka ka fito ba? Kuma ba aurenta ka ke so ka yi ba? To ka je na baka dama tuni ka yi aurenka ai, amman ka sani yanzu na fasa amincewa da tariyar khadija gidanka, zan barta cen wajen aikatau ɗin sai ka rubuta mata takardar sakinta idan ta sami mijinta a cen sai ta yi aurenta"
Tana ƙare faɗar maganar ta wuce abinta ta nufi ɗakinta, cikin sauri ya biyota cike da wani sabon tashin hankali yana faɗin
"Don girman ALLAH Hajiyarmu ki yi haƙuri ki yafe mani laifukana"
Sai dai yana kawowa bakin ƙofar ɗakin ta rufo ƙofar ɗakin da ƙarfi har saura ƙiris ta haɗa da kanshi, Safwan ya dawo baya cikin hanzari sannan ya durƙushe bakin ƙofar yana faɗin
"Zan mutu Hajiya idan har ba'a kawo man matata ba"
Daga cen cikin ɗakin Hajiyar ta ce "ka yi sauri ka mutun don ALLAH, kana da rai ma wani aure zata yi bale ka tafi ka bar duniyar?"
Safwan ya dafe saitin zuciyarshi yace
"Wayyo Hajiyarmu kada ki yi man irin wannan horon wallahil'azim ina sonta ke ma zaki sheda hakan"
Haka ya yi ta surutanshi har ya gaji Hajiyar bata sake tankashi ba, dole ya gaji ya miƙe ya nufi ɗaikinshi ya faɗa gado cikin ƙunar zuciya tare da yin nadama akan abunda ya aikatawa Dijen Baffah a farko, yanzu ga shi Hajiyar tana son horashi da laifin da har ya mance da ya aikata, saboda yanzu giyar sonta da ke walagigi da rayuwarshi yasa ya manta baya, haka ya yi ta kukan zucinshi cikin ɗaki cike baƙin cikin da ya mamaye masa zuciya, saboda Zee sai damunshi da kira take yi wani bayan wani ko gajiya bata yi amman yaƙi ɗaukar ko ɗaya, saboda damuwar da yake ciki a ganinshi ta shi ta shalle tunanin ta ta damuwar.
Haka ya yi ta yiwa Hajiya magiya akan ta dawo masa da Khadijarshi, da ya ga ma ta ƙi saurararsa ne ya kira Fiddo cikin sirri yana tambayarta inda aka kai khadijar, amman itama cike da jin haushinshi ta ce ita bata ma san Dijen bata gidan ba, dole ya koma tambayar ma'aikatan gidan sai dai su ma duka bakinsu ɗaya ne babu wanda yasan inda aka kaita, sai ga Safwan da biyar gidajen ƴan'uwa lungu da saƙo yana binciken ina aka kawo sabuwar ƴar'aiki, amman dai iya bincikenshi babu Dije babu mafarinta, dole ya dawo gida a jigace yana yi wa Hajiya kuka da hawayen da suke ta sauka a kan fuskarshi ba tare da sautin kukan ya fito ba, amman a hakan Hajiyar ta bushe fitilarta ta ce ba zata dawo da ita ba kuma sai ya bata takardar sakin Dijen dolenshi.
Damuwa goma da ashirin suka yi masa yawa a kai saboda izuwa lokacin Mahaifin Zee ma ya shiga cikin jerin sahun masu kiran nashi akan ya turo Iyayenshi, saboda danginsu sun yo masa caa! Akan rashin kyautawar da zai yi wa Aminu, shi
kuma ya kafe akan cewa duk abunda ƴarshi take so shi ma cen yake so, don har meeting aka yi akan matsalar ƙarshe kuma aka watse baram baram, saboda wasu da yawa sun ga laifinshi ya yin da wasu kuma suka goyi bayan Daddyn Zee ɗin saboda illolin auren dolen da ake hangowa, a ƙarshe dai Aminu da kanshi yake baiwa masu goyon bayanshi haƙuri akan lamarin, tare da sare masu gwiwa wajen sanar da su cewa shi fa ya janye, dole kowa ya haƙura aka zubawa Daddyn Zee ido aga iya gudun ruwansu shi da ƴarshi.
Kan haka ne ya yi ta samun Safwan ɗin da kira sai dai zance ɗaya ne yake yi masa na cewa wanda zai zo nema masa auren ya yi tafiya, da ma ya fahimci kamar zillewa yake son yi yasa su ji kunya ga ƴan'uwansu ya ce ya ce da shi
"Ya bashi number'r wakilin nashi shi zai kirashi ya yi masa bayanin abunda ke faruwa"
Dole Safwan ya saka masu ranar da zasu zo shi da Iyayenshi akai ƙarshe akan lamarin, sannan hankalin Daddyn Zee ya kwanta tare da kwantar na ƴarshi da ta ƙi ci ta ƙi sha akan damuwar rashin ɗaukar wayarta da Safwan ɗin baya yi.
Safwan ya je wa da Hajiya Mama da maganar tare da fayyace mata komi akan halin da ake ciki, sai dai duk da ta ji zafin abun aranta amman hakan bai sa ta hanashi auren ba, asali ma ta amince masa kamar farko yanda yasa mutane suka tursasata kan zancen auren, saboda tausayin yanda ya firgice cikin lokaci ɗaya saboda rashin Dijen, ya bi ya rame saboda damuwar da ya sakawa zuciyarshi akan rashin Matarshi, sannan ta san muddin ta hanashi auren bayan ta ɗauke masa Dijen ta cutar da rayuwar ɗanta, sai dai bata amince da auren ba ne sai da ta yi nazarinshi sosai akan damuwar rashin Dijen bazai barshi ya ji daɗin auren da zai yi ba, kuma ta hakan ne zata ƙara samun wata damar da babu wata ƴa mace da zata samu a wurinshi.
Safwan kam cike da tausayin kanshi da ita kan Zee ɗin ya tura Iyayenshi suka neme masa aurenta inda aka saka rana da lokaci sati biyu kacal masu zuwa, saboda su koma school su ci gaba da harƙallar karatunsu.
****
Biki sai ƙaratowa yake yi duk da ango kam ba wani jin daɗin auren ko zumuɗi irin na ango da yake yi, don a kullum dare ya kwanta baya baccin kirki saboda mafalkin Dijen da yake yi cikin yanayi kala kala, ta ɓangaren Zee Kam sai shirye shiryensu suke yi cike da alfahari, saboda su cusawa waɗanda basu son auren haushi, inda su kuma suka koma gefe suna kallon ta yanda za'a yi auren cin amana ya yi daɗi.
*****
Dijen Baffah kam duk da ta ji daɗin garin amman zuciyarta cike take da kewar Mijinta, bata da wani aiki sai na tunaninshi da kalamanshi waɗanda ada take hangosu a matsayin na yaudara, sai ga su a lokacin tana jinsu har cikin ruhinta, saboda ba ƙaramin daɗi suke yi mata a kunnuwa da gangar jikinta ba, waɗanda wani zubin bata san lokacin da wasu hawwyen kuka yake zuwar mata ba, don ita a son samunta a barta ta koma wurin Mijinta ta yi masa biyayyar da Inna take ta yi mata jan kunne akan ta yi masa, yanzu ta amince wa zuciyarta cewa itama fa tana son MALAM Safwan, ga shi ko waya babu a hannunta ba le ta kirashi ta ji daɗi, kuma kunyar idon Auntyn da kashedin Hajiyar yake sa ta ƙi tambayar a wane hali yake.
Ganin halin da take ciki ne yasa Aunty Ummi ta fara shiga damuwa duk da tana iya ƙoƙarinta wajen sakata nishaɗi saboda gurinta na son cire mata damuwa, shiyasa ko auren da ta ji ƙin nuna mata wani abu da zata gano ta yi, saboda jan kunnen da Hajiyar ta yi mata akan kada ta bari ta san da zancen, da ma lokacin auren ya matso ne ta yi mata ƙaryar wani biki ne daban zata je, da ma Dijen ta nuna tana son zuwan itama sai ta ce da ita ta yi haƙuri ba zata daɗe ba, don ma ta kwantar mata da hankali ta bar yaranta mata manya ta tafi da ƙananun saboda Maigidanta daman cen ba mazauni bane ba.
****
Biki bidiri bireɗe amfanin soyayya aure Zee ta angwance da masoyinta Safwan, zuciyarta cike da tsantsar farin ciki saɓaninshi da yake cikin ƙunci don duk wasu events ma ba da shi aka yi ba, an ɗauki Amarya daga Gombe zuwa Yola mahaifar Mijinta, inda aka wuce da ita gidan Hajiya Mama kai tsaye saboda ta kwashi tubarrakin uwar mijinta ta sawa aurensu albarka kafin akaita gidan angonta.
Sorry team Dije 🙇🏻♀️ku sani babu ruwana nidai 🙌🏻🏃🏻♀️
Akafta🙌🏻
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Mutanen Dije ina baku haƙuri🙏🏻dangane da auren Zee da Safwan ya yi, amman ina son ku sani ana yin book ne don faɗakarwa tare da wa'azantarwa sannan da kwatanta abunda ke faruwa a cikin al'ummarmu, saboda haka ku natsu tsaf ku bini sannu a hankali zan warware maku komi cikin tsarinshi😉*
*Lamba ta 58*
Har ƙuryar ɗakin Hajiya Mama aka kai Zee da ke ta rufe fuska tana ta wasar baki saboda daɗin da ya kasa ɓoyuwa a kan fuskarta, gaban kowa da mutanen da suka yi mata rakiya Hajiya Mama ta ce da Zee
"ALLAH ya baku haƙurin zama,
kuma albarkaci aurenku tare da zuri'a ɗayyaba gaba ɗaya, sannan da fatar zaman lafiya ke da abokiyar zamanki"
Dirim! dum! Shine bugun da zuciyar da Zee ta yi amman ta wayance tare da noƙe fuskarta tace "Ameen" Hajiya Mama ta ƙara da cewa