Sashe 41
Dije Ƙarangiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ai Ni ce da godiya WALLAHi na gode sosai ALLAH ya biyaka ya saka maka dai dai da taimakon da ka yi"
Duka suka rakota har bakin gida sai godiya suke zubawa, har ta yi nisa Bala ya biyota cike da ladabi ya rusuna yace
"Afuwa nake nema nasan nayi maki laifi ki yi haƙuri ki yafe man don ALLAH"
Dije ta waigo tace da shi
"Zan yafe maka kuma zan ci gaba da kyautata maka matuƙar ka riƙe Ladiyo amana, ka kyautata zamanka tare da ita kuma ka gyara halayyarka ta son kuɗi ka daina kiranta ɓarauniya, sannan ka gyara duk wata mu'amalarka da ita, to da ka yi hakan ka ɗauka cewa tamkar ka sami alkhairina da na Maigidana ne, amman muddin na ji cewa baka zama da ita yanda ya da ce to ka ɗauka tamkar ka datse igiyar alkhairanka garemu ne, saboda haka idan ka gyara ka ga da kyau a aljihunka, idan kuma ka ɓata to shikenan ka lalace komi, ni ka ga tafiyata kuma ka sani zan saka masu kula da komi, don kada ka ga bana nan to ina da idanuwa ta ko'ina a garin nan"
Bala baki washe ya ce
"Ai Insha ALLAHu alkhairi ma zaki ji amman itama zan turo ta wajenki ki ja kunnenta akan abubuwan da take yi mani, da ta gyara shikenan matsala ta kau gareni da yardar Allah"
Dije tace, "tace wannan ba damuwa bace sai ta zo kawai ALLAH ya sa mu dace dai gaba ɗayanmu ya bamu zaman lafiya"
Yace "Ameen Ameen ranki ya daɗe ai ke kin haye saura mu kawai"
Dije ta so ta yi dariya ta mazge tace, "kai m ka kusa hayewar matuƙar na dawo garin nan na ji labari mai daɗi"
Bala sai duƙe ɗuke yake yi yan faɗin, "kar ki ji komi insha ALLAHu komi zai daidaita"
Haka suka rabu Dije sai ƙumshe dariyar da take cinta take yi, su Lantin ma sai da ta basu ɗari biyu tace su raba, suka tafi gida suna ta jin daɗi.
Hannuna ya yi sanyi yasin😩
Akafta😆
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*INA YINKU ALL MY FAN'S INA GODIYA🙏🏻 DA ADDU'ARKU GARENI KU DAƊE KU YI LASTING MUTANENA👍🏻*
*Lamba ta 42*
Dije kam tana cin kayan ƙwalam ɗin tana kyalkyatar dariya, tana baiwa Inna labarin abunda ya faru don ko da su Baffah suka dawo gidan ranar labarin ne kawai take ta basu ana dariya.
Haka Dijen ta ci gaba da ziyarar yan uwa da abokan arziƙi don har wani ƙauye suka je da Inna inda ainahin tushen iyayenta suke, kowa ya yi sambarka da auren Dijen don kuwa su ma sun sheda ta sanadiyyar tsarabar Dijen da Inna ta kai masu.
Satinta biyu dam a ƙiriu Direban da ya kawota ya zo ɗaukarta da uwar tsarabar ƙauyensu niƙi niƙi suka lula yola, bayan tasha kukan rabuwa da Inna da sauran ƙawayenta da yan uwa da abokan arziƙi, kowa da kalar tsarabar da ya bata ta kaiwa surukarta Hajiya Mama, don Maigarin kanshi galan ɗin manshanu lafiyayyen suya ya bada akai masu, Baffah da Inna kam babu ce kawai basu bayar ba don tsakanin tsintsiyar laushi, kuka, daddawa, guro, kayan yaji maburki, busasshiyar rama, gero, dawa, wake, niƙaƙƙen garin waken na ɗanwake lafiyayye, manja, manƙuli, soyayyar gyaɗa, kai kayan ƙwalam na Ladiyo ma ba'a barsu a baya ba, don kuwa kaf maƙulashenta sai da ta yo wa Dije tsarabarsu saboda takanas Bala ya bada kuɗi aka haɗa mata kayan.
Tafiyar wuni biyu ce ta kai Dije Yola cikin tsananin galabaita saboda rashin sabo da tafiyar, Ba Surry da Hajiya Mama ba har Fiddo kanta sai da ta nuna jin daɗin dawowar Dijen, saboda himilin kayan tsarabar da ta zo masu da su, Hajiya Mama baki har kunne sai godiya take zubawa saboda tsananin jin daɗin karamcin da su Baffah'n suka yi masu.
Kasancewar hutunsu Dijen ya ƙare kwananta biyu a gidan aka yi mata provision ta koma makaranta, ita kanta cike take da ɗokin ganin mutanenta sis Aysha da kuma ƙawarta Hannatu, saboda sunyi kewar juna ba kaɗan ba.
Kwanci tashi asarar mai rai sai ga Dijen Baffah ta shiga jerin sahun kowace mace a duniya, don kuwa ranar farko da ta fara ganin baƙon watanta duk house ɗinsu sai da kowa ya sani, saboda uban kuka da ta ci akan ita bata taɓa iskanci ba amman jini sai fitowa yake yi a jikinta, Wayyo ita ALLAH a taimaketa wani yaci amanarta ya iskanceta bata sani ba, Sis Aysha itace ta janyota zuwa toilet saboda uwar dariyar da taga anael yi mata, cikin natsuwa ta fahimtar da ita komi ta nuna mata ga yanda zata yi ta kimtsa kanta, sannan hankalin Dije ya kwanta amman fa tasha tsokana a wajen mutane ba kaɗan ba, lokacin da ta gama kwanakinta ma Sis Aysha itace ta yi mata gwari gwari akan yanda zata tsallake jikinta.
*Shin wai ina baƙin Turai ne?*
Malam Safwan kam tunda ya tafi Ƙasar ya yi ƙoƙarin danne damuwar da ya tafi da ita domin ya fuskanci karatunshi, sai dai wani gefe na zuciyarshi yana tunano masa Dijen Baffah da shirmenta, wani zubin ya yi dariya wani lokaci kuma ya ɓata fuska musamman idan ya tuno abunda Hajiya Mama take yi masa akanta.
Masha ALLAH kasancewarshi mutum mai tsattsauran ra'ayi yasa baya da wasu abokan kirki sai tsirara ko su just for mutunci kawai don shi miskili ne na gasken sosai, baya shiga shirgin kowa sai wanda ya dace ace ya shiga.
Wannan halin na shi ne ya janyo mata da yawa suka mato a kanshi, inda ko wace ƙoƙarin take yi ace itace ta yi sa'ar ƙulla alaƙa da shi, musamman ma da ya kasance gifted akan karatunshi ko kaɗan baya wasa, don daman cen shi tun asali yana baiwa karatu muhimmanci ko lokacin da ya yi karatun a gida Nigeria bale yanzu da ya shigo cikin fararen fata.
Matan turawan ma da yawa wasu sun ƙyasa ballantana na mu matan na baƙar fata masu zuwa cen karatu, sai dai rashin fuskarshi yasa kowace take ɗar ɗar da shiga sabgarshi don tsoron kada ya yanƙwanasu su ji kunya, amman a hakan sai da wasu turawa suka sami kanshi suka fara mutunci da shi, a cikin baƙaƙen fatarmu namu ma akwai mace ɗaya Zainab wacce ake kira da Zee bab da Namiji ɗaya Auwal da suka sami sa'ar shiga rayuwarshi, waɗanda su kansu yan asalin Nigeria ne sai dai kowane daga cikinsu suna garuruwa mabanbanta, zee Bab yar Gombe ce yayin da Auwal yake ɗan asalin Kano, wasa wasa sai gasu sun zamo aminanshi waɗanda komi zasu yi dole ne sai sun nemi junansu.
Zee Bab kam gurinta na shiga rayuwar Safwan ya cika don kuwa sannu a hankali ta fara nuna masa irin yanda ta damu da shi, kasancewar ba directly ta fito masa ba shiyasa bai hantareta kamar yanda ya saba yiwa sauran mata ba, cikin dabara ta ƙulla alaƙar soyayya da shi mai ƙarfi, wadda ta kai basa shayin nunawa duniya irin yanda suke son junansu ko a gaban ma waye, har suna iƙirarin zasu auri junansu duk runtsi duk da cewa itama Zee ɗin tana da mijinta da zata aura acen gida Nigeria.
Sai dai akasin da aka samu shine ranar da Safwan ya sanarwa da Hajiya Mama labarinta rufe ido ta yi fata fata da shi, akan cewa bata lamunta da ya auri kowace mace ba har sai ya mutunta auren Dije tukunna, shi ko ya nuna mata shi fa ba sonta yake yi ba yanzu ya sami matar aure kuma ita yake so ya aura, don hasali ma ita kanta Zee ɗin bai sanar da ita cewa yana da wata mata ba, saboda rena auren Dijen da ya yi a tunaninshi da ya auri Zee zai korata ta koma ƙauyensu, idan kuma Hajiya ta bashi dama zai cikawa amininshi Lawi alƙawalin da ya yi wa kanshi na duk runtsi sai ya mayar masa da ita ya aureta tunda har ya fishi sonta.
Sai dai kuma gashi Hajiya Mama tana son dakushe masa karsashi, don shi kam sun riga da sun daidaita da Zee akan da ya kammala karatunshi zasu dawo gida Nigeria ayi aurensu kawai.
Akan haka ne ma rashin fahimta ya shiga tsakaninshi da Hajiyar, idan ya kira wayarta ta ƙi ɗauka ya galabaita sosai da mugun fushin ta yi da shi sosai, saboda duk Iyayenshi maza ya yayunshi biyu mata da suke aure duk sunyi ta bata haƙuri akan ta barshi ya yi auren amman ta yi biris da kowa, tace in dai har akan ta goya masa baya ne ya yi wani auren ya ci amanar yarinyar mutane to bazata taɓa lamuncewa da auren ba, jin wannan kalaman nata masu tsauri yasa ya ajiye komi ya nufo Nigeria ba shiri, sai dai yanayin da ya taradda ita ya sa ya ƙara gasgata zancenta dole marairecewa akan neman biyan buƙatarshi, tare yi mata bayanin cewa shi ba zai ci amanar Dijen ba, asali ma so yake yi ya haɗata da masoyinta na asali tunda har ya sami matar da yake so.
ganin ta ƙi amince cewa ne yasa ya kwaso mata mutane suka zo suna bata baki kowa da abunda yake cewa dangane da ALLAH ya ce Annabi yace, ana roƙonta akan ta barshi ya yi aurenshi kafin ita Dijen ta mallaki hankalinta tasan minene auren, da ƙyar aka shawo kanta amman da sharaɗin duk ranar da Amaryar ta tare itama Dijen a ranar za'a kaita gidanshi a matsayinta na uwargida, hankalinshi ya ƙara tashi ya ruɗe gaba ɗaya saboda tsoron Zee taga kamar ya munafunceta tunda bai ce da ita yana da wata matar ba, aikam ba kalar magiyar da bai yi mata ba akan ta janye zancen tariyar Dijen sai daga baya idan Zee ta zo, amman Hajiya Mama tace sam! Bata san da wannan zance ba, dole ba kuzari ya harhaɗa kayanshi da nufin komawa, saboda yanda ita Zee ɗin ta dameshi akan ya dawo ya dawo.
Duka suka rakota har bakin gida sai godiya suke zubawa, har ta yi nisa Bala ya biyota cike da ladabi ya rusuna yace
"Afuwa nake nema nasan nayi maki laifi ki yi haƙuri ki yafe man don ALLAH"
Dije ta waigo tace da shi
"Zan yafe maka kuma zan ci gaba da kyautata maka matuƙar ka riƙe Ladiyo amana, ka kyautata zamanka tare da ita kuma ka gyara halayyarka ta son kuɗi ka daina kiranta ɓarauniya, sannan ka gyara duk wata mu'amalarka da ita, to da ka yi hakan ka ɗauka cewa tamkar ka sami alkhairina da na Maigidana ne, amman muddin na ji cewa baka zama da ita yanda ya da ce to ka ɗauka tamkar ka datse igiyar alkhairanka garemu ne, saboda haka idan ka gyara ka ga da kyau a aljihunka, idan kuma ka ɓata to shikenan ka lalace komi, ni ka ga tafiyata kuma ka sani zan saka masu kula da komi, don kada ka ga bana nan to ina da idanuwa ta ko'ina a garin nan"
Bala baki washe ya ce
"Ai Insha ALLAHu alkhairi ma zaki ji amman itama zan turo ta wajenki ki ja kunnenta akan abubuwan da take yi mani, da ta gyara shikenan matsala ta kau gareni da yardar Allah"
Dije tace, "tace wannan ba damuwa bace sai ta zo kawai ALLAH ya sa mu dace dai gaba ɗayanmu ya bamu zaman lafiya"
Yace "Ameen Ameen ranki ya daɗe ai ke kin haye saura mu kawai"
Dije ta so ta yi dariya ta mazge tace, "kai m ka kusa hayewar matuƙar na dawo garin nan na ji labari mai daɗi"
Bala sai duƙe ɗuke yake yi yan faɗin, "kar ki ji komi insha ALLAHu komi zai daidaita"
Haka suka rabu Dije sai ƙumshe dariyar da take cinta take yi, su Lantin ma sai da ta basu ɗari biyu tace su raba, suka tafi gida suna ta jin daɗi.
Hannuna ya yi sanyi yasin😩
Akafta😆
D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*INA YINKU ALL MY FAN'S INA GODIYA🙏🏻 DA ADDU'ARKU GARENI KU DAƊE KU YI LASTING MUTANENA👍🏻*
*Lamba ta 42*
Dije kam tana cin kayan ƙwalam ɗin tana kyalkyatar dariya, tana baiwa Inna labarin abunda ya faru don ko da su Baffah suka dawo gidan ranar labarin ne kawai take ta basu ana dariya.
Haka Dijen ta ci gaba da ziyarar yan uwa da abokan arziƙi don har wani ƙauye suka je da Inna inda ainahin tushen iyayenta suke, kowa ya yi sambarka da auren Dijen don kuwa su ma sun sheda ta sanadiyyar tsarabar Dijen da Inna ta kai masu.
Satinta biyu dam a ƙiriu Direban da ya kawota ya zo ɗaukarta da uwar tsarabar ƙauyensu niƙi niƙi suka lula yola, bayan tasha kukan rabuwa da Inna da sauran ƙawayenta da yan uwa da abokan arziƙi, kowa da kalar tsarabar da ya bata ta kaiwa surukarta Hajiya Mama, don Maigarin kanshi galan ɗin manshanu lafiyayyen suya ya bada akai masu, Baffah da Inna kam babu ce kawai basu bayar ba don tsakanin tsintsiyar laushi, kuka, daddawa, guro, kayan yaji maburki, busasshiyar rama, gero, dawa, wake, niƙaƙƙen garin waken na ɗanwake lafiyayye, manja, manƙuli, soyayyar gyaɗa, kai kayan ƙwalam na Ladiyo ma ba'a barsu a baya ba, don kuwa kaf maƙulashenta sai da ta yo wa Dije tsarabarsu saboda takanas Bala ya bada kuɗi aka haɗa mata kayan.
Tafiyar wuni biyu ce ta kai Dije Yola cikin tsananin galabaita saboda rashin sabo da tafiyar, Ba Surry da Hajiya Mama ba har Fiddo kanta sai da ta nuna jin daɗin dawowar Dijen, saboda himilin kayan tsarabar da ta zo masu da su, Hajiya Mama baki har kunne sai godiya take zubawa saboda tsananin jin daɗin karamcin da su Baffah'n suka yi masu.
Kasancewar hutunsu Dijen ya ƙare kwananta biyu a gidan aka yi mata provision ta koma makaranta, ita kanta cike take da ɗokin ganin mutanenta sis Aysha da kuma ƙawarta Hannatu, saboda sunyi kewar juna ba kaɗan ba.
Kwanci tashi asarar mai rai sai ga Dijen Baffah ta shiga jerin sahun kowace mace a duniya, don kuwa ranar farko da ta fara ganin baƙon watanta duk house ɗinsu sai da kowa ya sani, saboda uban kuka da ta ci akan ita bata taɓa iskanci ba amman jini sai fitowa yake yi a jikinta, Wayyo ita ALLAH a taimaketa wani yaci amanarta ya iskanceta bata sani ba, Sis Aysha itace ta janyota zuwa toilet saboda uwar dariyar da taga anael yi mata, cikin natsuwa ta fahimtar da ita komi ta nuna mata ga yanda zata yi ta kimtsa kanta, sannan hankalin Dije ya kwanta amman fa tasha tsokana a wajen mutane ba kaɗan ba, lokacin da ta gama kwanakinta ma Sis Aysha itace ta yi mata gwari gwari akan yanda zata tsallake jikinta.
*Shin wai ina baƙin Turai ne?*
Malam Safwan kam tunda ya tafi Ƙasar ya yi ƙoƙarin danne damuwar da ya tafi da ita domin ya fuskanci karatunshi, sai dai wani gefe na zuciyarshi yana tunano masa Dijen Baffah da shirmenta, wani zubin ya yi dariya wani lokaci kuma ya ɓata fuska musamman idan ya tuno abunda Hajiya Mama take yi masa akanta.
Masha ALLAH kasancewarshi mutum mai tsattsauran ra'ayi yasa baya da wasu abokan kirki sai tsirara ko su just for mutunci kawai don shi miskili ne na gasken sosai, baya shiga shirgin kowa sai wanda ya dace ace ya shiga.
Wannan halin na shi ne ya janyo mata da yawa suka mato a kanshi, inda ko wace ƙoƙarin take yi ace itace ta yi sa'ar ƙulla alaƙa da shi, musamman ma da ya kasance gifted akan karatunshi ko kaɗan baya wasa, don daman cen shi tun asali yana baiwa karatu muhimmanci ko lokacin da ya yi karatun a gida Nigeria bale yanzu da ya shigo cikin fararen fata.
Matan turawan ma da yawa wasu sun ƙyasa ballantana na mu matan na baƙar fata masu zuwa cen karatu, sai dai rashin fuskarshi yasa kowace take ɗar ɗar da shiga sabgarshi don tsoron kada ya yanƙwanasu su ji kunya, amman a hakan sai da wasu turawa suka sami kanshi suka fara mutunci da shi, a cikin baƙaƙen fatarmu namu ma akwai mace ɗaya Zainab wacce ake kira da Zee bab da Namiji ɗaya Auwal da suka sami sa'ar shiga rayuwarshi, waɗanda su kansu yan asalin Nigeria ne sai dai kowane daga cikinsu suna garuruwa mabanbanta, zee Bab yar Gombe ce yayin da Auwal yake ɗan asalin Kano, wasa wasa sai gasu sun zamo aminanshi waɗanda komi zasu yi dole ne sai sun nemi junansu.
Zee Bab kam gurinta na shiga rayuwar Safwan ya cika don kuwa sannu a hankali ta fara nuna masa irin yanda ta damu da shi, kasancewar ba directly ta fito masa ba shiyasa bai hantareta kamar yanda ya saba yiwa sauran mata ba, cikin dabara ta ƙulla alaƙar soyayya da shi mai ƙarfi, wadda ta kai basa shayin nunawa duniya irin yanda suke son junansu ko a gaban ma waye, har suna iƙirarin zasu auri junansu duk runtsi duk da cewa itama Zee ɗin tana da mijinta da zata aura acen gida Nigeria.
Sai dai akasin da aka samu shine ranar da Safwan ya sanarwa da Hajiya Mama labarinta rufe ido ta yi fata fata da shi, akan cewa bata lamunta da ya auri kowace mace ba har sai ya mutunta auren Dije tukunna, shi ko ya nuna mata shi fa ba sonta yake yi ba yanzu ya sami matar aure kuma ita yake so ya aura, don hasali ma ita kanta Zee ɗin bai sanar da ita cewa yana da wata mata ba, saboda rena auren Dijen da ya yi a tunaninshi da ya auri Zee zai korata ta koma ƙauyensu, idan kuma Hajiya ta bashi dama zai cikawa amininshi Lawi alƙawalin da ya yi wa kanshi na duk runtsi sai ya mayar masa da ita ya aureta tunda har ya fishi sonta.
Sai dai kuma gashi Hajiya Mama tana son dakushe masa karsashi, don shi kam sun riga da sun daidaita da Zee akan da ya kammala karatunshi zasu dawo gida Nigeria ayi aurensu kawai.
Akan haka ne ma rashin fahimta ya shiga tsakaninshi da Hajiyar, idan ya kira wayarta ta ƙi ɗauka ya galabaita sosai da mugun fushin ta yi da shi sosai, saboda duk Iyayenshi maza ya yayunshi biyu mata da suke aure duk sunyi ta bata haƙuri akan ta barshi ya yi auren amman ta yi biris da kowa, tace in dai har akan ta goya masa baya ne ya yi wani auren ya ci amanar yarinyar mutane to bazata taɓa lamuncewa da auren ba, jin wannan kalaman nata masu tsauri yasa ya ajiye komi ya nufo Nigeria ba shiri, sai dai yanayin da ya taradda ita ya sa ya ƙara gasgata zancenta dole marairecewa akan neman biyan buƙatarshi, tare yi mata bayanin cewa shi ba zai ci amanar Dijen ba, asali ma so yake yi ya haɗata da masoyinta na asali tunda har ya sami matar da yake so.
ganin ta ƙi amince cewa ne yasa ya kwaso mata mutane suka zo suna bata baki kowa da abunda yake cewa dangane da ALLAH ya ce Annabi yace, ana roƙonta akan ta barshi ya yi aurenshi kafin ita Dijen ta mallaki hankalinta tasan minene auren, da ƙyar aka shawo kanta amman da sharaɗin duk ranar da Amaryar ta tare itama Dijen a ranar za'a kaita gidanshi a matsayinta na uwargida, hankalinshi ya ƙara tashi ya ruɗe gaba ɗaya saboda tsoron Zee taga kamar ya munafunceta tunda bai ce da ita yana da wata matar ba, aikam ba kalar magiyar da bai yi mata ba akan ta janye zancen tariyar Dijen sai daga baya idan Zee ta zo, amman Hajiya Mama tace sam! Bata san da wannan zance ba, dole ba kuzari ya harhaɗa kayanshi da nufin komawa, saboda yanda ita Zee ɗin ta dameshi akan ya dawo ya dawo.